Sojojin Libiya Sun ‘Yantar Da Fursunoni Daga Gidajen Yarin Sirri Da Ake Tsare Da Su Ba Bisa Ka’ida Ba
Published: 18th, May 2025 GMT
Sojojin Libiya sun ‘yantar da fursunoni da dama daga gidajen yari na sirri da ke karkashin dakarun Tallafawa da Wanzar da Kwanciyar hankali na Kasar
Sojojin kasar Libya a birnin Tripoli fadar mulkin kasar sun ‘yantar da fursunoni da dama da ake tsare da su a gidajen yari na sirri karkashin hukumar “Tallafawa da wanzar da zaman lafiya” bayan sun kwace iko da wasu helkwatar tsaro a babban birnin kasar.
‘Yanto fursunonin ya biyo bayan fitar da faifan bidiyo da sojojin Libiya da ma’aikatar harkokin cikin gidan kasar suka yi ne da ke nuna lokacin da aka ‘yantar da fursunonin. Hotunan sun nuna akwai dakunan tsare mutane ba bisa ka’ida ba da kuma gidajen yari da ake amfani da su a cikin hedkwatar hukumar, wanda ya wuce ikon hukumomin shari’a na kasa.
A wani labarin kuma, Fira Ministan gwamnatin hadin kan kasa, Abdul Hamid Dabaiba, ya fitar da kuduri mai lamba (226) na shekara ta 2025, dangane da kafa kwamitin gaggawa da zai binciki yanayin gidajen yari da na tsare tsare a kasar, biyo bayan wadannan bayanai masu ban mamaki.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: a gidajen yari
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda noma ya kankama bayan sulhu da ’yan bindigar Katsina
A wasu yankunan Jihar Katsina da suka daɗe cikin fargaba da hare-haren ’yan bindiga, zaman lafiya ya fara dawowa sakamakon sulhu da al’umma suka yi da masu tayar da ƙayar baya.
Wannan sulhu, wanda ba a haɗa gwamnati ba, ya bai wa manoma damar komawa gonakinsu cikin daminar bana.
Manoma sun fara noma cikin kwanciyar hankaliƘananan hukumomin Batsari, Jibiya da Ɗanmusa na daga cikin wuraren da aka samu wannan ci gaba. Wasu manoma da wakilinmu ya zanta da su sun bayyana farin cikinsu da yadda rayuwa ke dawowa dai-dai.
Malam Rabe, manomi daga Nasarawa a Ƙaramar Hukumar Jibiya, ya ce: “Mu kam yanzu sai mu ce Alhamdulillahi. Lallai sulhu alheri ne a tsakanin al’umma. Ni rabon da na duƙa gonata da sunan noma na fi shekara 8. Amma yanzu gashi ni ne har da yin ɓaɓar shanu.”
Ya ƙara da cewa: “Jiya sai kusan magariba na baro gona, wanda can baya ƙarfe sha biyu ba ta yi mani. Rabinmu duk hijira muka yi, tun daga nan har Bugaje, Gangara, Zandam da sauran yankuna.”
Sulhu da ’yan bindiga ya sauya fasalin rayuwaAlhaji Surajo Jibiya, ɗaya daga cikin masu shirya sulhun, ya ce: “Mun ga canji sosai. Manomanmu duk sun koma gona. Hatta cikin lunguna mun samu labarin sun ci gaba da noma ba tare da wata fargaba ba. Duk inda ba a yi noma ba shekaru biyar da suka wuce, wannan shekarar an yi fiye da tunani.”
A cewar Surajo, hatta tsohon jagoran ’yan bindiga, Abdu Lanƙai, ya koma noma.
“Duk wata yarjejeniyar da aka yi da shi Lanƙai yana bin ta sau da ƙafa. In ya gano mai laifi, zai yanke hukunci nan take.”
Noman kankana ya kankama a Jibiya
Malam Salisu, mazaunin kan iyakar Jibiya da Batsari, ya ce: “Har waɗanda ba su yi noman kankana ba a baya, yanzu sun yi kuma an fitar da ita zuwa Abuja da sauran kasuwanni. Duk wata matsala da muke tunanin za ta kunno kai, Allah cikin ikon shi har yanzu babu wata matsala da aka samu.”
Koyi da Batsari aka yiA Batsari, inda aka fara sulhun, ana tafiya da yarjejeniyar yadda ya kamata. Hassan Dogon Faci ya ce: “Garuruwan da suka kusan zama kufai kamar Batsarin Alhaji, Watangakiyya, Ɗangeza, Zamfarawa, Madogara, Nahuta, Kofa da Dumburawa — a yanzu duk noma ake yi a cikinsu kuma babu wata matsala.”
Ya ƙara da cewa: “Ranar Juma’ar da ta wuce har wa’azi muka je muka yi a garin Labo. Ashe sai mu ce, an samu nasara. Yanzu sai dai mu ji labari ana fama da matsala, amma mu kam Alhamdulillahi.”
Da sauran rina a kabaDuk da wannan ci gaba, wasu yankuna kamar Ƙanƙara, Bakori, Faskari, Malumfashi da Ƙafur na ci gaba da fuskantar hare-hare. A kwanan nan, an yi garkuwa da mutane akalla goma sha takwas daga Ƙanƙara zuwa Sheme da Kakumi da sauran yankuna.
Manoman yankunan sun ce duk da akwai gonakin da aka noma, yawancin su na bakin gari ne, amma waɗanda ke nesa sun ɓar gonakin saboda tsoron hare-hare.
A cikin ƙananan hukumomin Batsari, Jibiya da ƊanMusa da ke Jihar Katsina, al’umma sun ɗauki matakin da ba a saba gani ba — sun yi sulhu da ’yan bindigar daji, waɗanda suka daɗe suna addabar yankin da garkuwa da mutane, kisan gilla da satar shanu.
Wannan sulhu, wanda ba a haɗa gwamnati ba, ya fara haifar da zaman lafiya da ci gaba.
Manoma sun koma gonaManoman yankin sun fara komawa gonakinsu cikin daminar bana, suna noma ba tare da fargaba ba. Wasu daga cikinsu sun bayyana cewa sulhun ya kawo sauyi mai ma’ana.
Malam Rabe, wani manomi daga garin Nasarawa a Ƙaramar Hukumar Jibiya, ya ce: “Mu kam yanzu sai mu ce Alhamdulillahi. Lallai sulhu alheri ne a tsakanin al’umma. Ni rabon da na duƙa gonata da sunan noma gaskiya na fi shekara 8, ko in ce 10. Amma yanzu gashi ni ne har da yin huɗar shanu.”
Ya ƙara da cewa: “Jiya sai kusan magariba na baro gona, wanda can baya ƙarfe sha biyu ba ta yi mani a cikin gonar. Ka san daga bisani rabinmu duk hijira muka yi, tun daga nan har Bugaje, ka tafi har can wajen su Gangara da su Zandam da sauran waɗannan yankuna.”
Sulhu ya canza rayuwaAlhaji Surajo Jibiya, ɗaya daga cikin masu shirya sulhun, ya ce: “Lallai mun ga canji sosai. Manomanmu duk sun koma gona. Hatta da cikin lunguna mun samu labarin sun ci gaba da noma ba tare da wata fargaba ba. Duk inda ba a yi noma ba shekaru biyar da suka wuce, wannan shekarar an yi fiye da tunani.”
Abin ban mamaki shi ne, tsohon jagoran ’yan bindiga, Abdu Lanƙai, shi ma ya koma noma.
“Duk wata yarjejeniyar da aka yi da shi Lanƙai yana bin ta sau da ƙafa. In ya gano mai laifi, zai yanke hukunci nan take.”
Noman kankana ya kankama a JibiyaMalam Salisu, mazaunin kan iyakar Jibiya da Batsari, ya ce: “Har waɗanda ba su yi noman kankana ba a baya, yanzu sun yi kuma an fitar da ita zuwa Abuja da sauran kasuwanni. Duk wata matsala da muke tunanin za ta kunno kai, Allah cikin ikon shi har yanzu babu wata matsala da aka samu.”
Batsari ta fara, sauran na biA Batsari, inda aka fara sulhun, ana tafiya da yarjejeniyar yadda ya kamata. Hassan Dogon Faci ya ce:
“Garuruwan da suka kusan zama kufai kamar Batsarin Alhaji, Watangakiyya, Ɗangeza, Zamfarawa, Madogara, Nahuta, Kofa da Dumburawa — a yanzu duk noma ake yi a cikinsu kuma babu wata matsala.”
Ya ƙara da cewa: “Ranar Juma’ar da ta wuce har wa’azi muka je muka yi a garin Labo. Ashe sai mu ce, an samu nasara. Yanzu sai dai mu ji labari ana fama da matsala, amma mu kam Alhamdulillahi.”
Da sauran rina a kabaƘaramar Hukumar ƊanMusa ta baya-bayan nan ce da ta yi sulhu, kuma ana ganin tasirinsa. Sai dai a wasu yankuna kamar Ƙanƙara, Bakori, Faskari, Malumfashi da Ƙafur, harin ’yan bindiga bai tsaya ba.
A kwanan nan, an yi garkuwa da mutane akalla goma sha takwas daga Ƙanƙara zuwa Sheme da Kakumi da sauran yankuna.
Manoman yankunan sun ce duk da akwai gonakin da aka noma, yawancin su na bakin gari ne, amma waɗanda ke nesa sun bar gonakin.