Tsohon Fira Ministan Gwamnatin Isra’ila Ya Bukaci A Tsige Netanyahu Daga Kan Fira Ministan Isra’ila
Published: 17th, May 2025 GMT
Tsohon fira ministan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ya ce: Fira ministan Netanyahu ya yi sakaci da rayuwar yahudawa a cikin aikinsa don haka hambarar da gwamnatinsa ita ce mafita
Tsohon Fira ministan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila Ehud Barak ya yi kira da a hambarar da Benjamin Netanyahu da gwamnatinsa, yana mai zarginsa da yin sakaci wajen kubutar da fursunonin yahudawa da suke hannu ‘yan gwagwarmaya a Zirin Gaza.
Barak ya ce: Netanyahu yana sakaci da rayuwar fursunonin yahudawa da ake tsare da su a Gaza domin faranta wa masu tsattsauran ra’ayi a gwamnatinsa rai.” Ya bayyana shi a matsayin mai sakaci wajen gudanar da ayyukansa, da kuma ci gaba da kisan kiyashi a Zirin Gaza domin karecmanufofin siyasa saboda neman ci gaba da mulki.
A wata hira da yayi da tashar talabijin mai zaman kanta ta Isra’ila ta 12, Barak ya bayyana cewa: Netanyahu “yana sakaci da rayukan mutanen da ake tsare da su a Gaza domin farantawa masu tsatsauran ra’ayi a gwamnatinsa rai. Don haka ya jaddada yin kira ga ‘yan adawa da su dauki matakin ruguza gwamnatin Netanyahu maimakon ceto shi.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: a gwamnatinsa
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Mayar Da Martani Ga Shugaban Kasar Amurka
Ministan harkokin wajen Iran ya mayar da martani ga kalaman shugaban Amurka Donald Trump na baya-bayan nan game da Iran
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya bayyana cewa: Amurka ita ce ta kawo cikas ga ci gaban al’ummar Iran ta hanyar kakaba takunkumai, matsin lamba da kuma barazanar soji da ba na soji ba, don haka ne Amurka ke haddasa matsalolin tattalin arzikin Iran.
A gefen taron majalisar ministocin a yau Laraba, Araqchi ya bayyana cewa, abin da Trump ya fada game da kasashen yankin da suke son bin hanyar samun ci gaba da wadata shi ne, a hakikanin gaskiya irin tafarkin da al’ummar Iran suka bi a lokacin juyin juya halinsu, da kuma tafarkin da suka zaba na gina kasa mai cin gashin kanta, ta dimokiradiyya, mai ‘yanci da ci gaba. Amma Amurka ta hana al’ummar Iran samun ci gaba ta hanyar takunkumai da ta kakaba mata wanda ya shafe sama da shekaru arba’in, baya ga matsin lamba da barazanar da take fuskanta na soji da wanda ba na soji ba.
Ya ci gaba da cewa: Amurka ita ce musabbabin tabarbarewar tattalin arziki, kuma ita ce ta dora ma al’ummar Iran manufofinta na girman kai da kama-karya, saboda tana son mulkin da ba shi da ‘yancin kai, ba kuma mai biyayya gare ta a kan wannan tubali, wanda a dabi’ance bai dace da martabar al’ummar Iran ba.