Tsohon fira ministan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ya ce: Fira ministan Netanyahu ya yi sakaci da rayuwar yahudawa a cikin aikinsa don haka hambarar da gwamnatinsa ita ce mafita

Tsohon Fira ministan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila Ehud Barak ya yi kira da a hambarar da Benjamin Netanyahu da gwamnatinsa, yana mai zarginsa da yin sakaci wajen kubutar da fursunonin yahudawa da suke hannu ‘yan gwagwarmaya a Zirin Gaza.

Barak ya ce: Netanyahu yana sakaci da rayuwar fursunonin yahudawa da ake tsare da su a Gaza domin faranta wa masu tsattsauran ra’ayi a gwamnatinsa rai.” Ya bayyana shi a matsayin mai sakaci wajen gudanar da ayyukansa, da kuma ci gaba da kisan kiyashi a Zirin Gaza domin karecmanufofin siyasa saboda neman ci gaba da mulki.

A wata hira da yayi da tashar talabijin mai zaman kanta ta Isra’ila ta 12, Barak ya bayyana cewa: Netanyahu “yana sakaci da rayukan mutanen da ake tsare da su a Gaza domin farantawa masu tsatsauran ra’ayi a gwamnatinsa rai. Don haka ya jaddada yin kira ga ‘yan adawa da su dauki matakin ruguza gwamnatin Netanyahu maimakon ceto shi.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: a gwamnatinsa

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda muka daƙile yunƙurin tsige Akpabio daga shugabancin Majalisa – Orji Kalu

Sanata mai wakiltar Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana yadda wasu yan majalisa suka haɗa kai suka daƙile yunkurin tsige Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio.

Yayin da yake zantawa da manema labarai a ranar Talata a Majalisar Tarayya da ke Abuja, Sanata Kalu ya tabbatar da cewa akwai yunkuri daga wasu ’yan majalisa na tsige Akpabio daga mukaminsa, wanda bai yi nasara ba.

Babu wani gwamna da zai yi ƙorafin ƙarancin kuɗi a mulkin Tinubu — Sanwo Olu Mai cutar HIV ya yi wa ’yar shekara 4 fyaɗe a Yobe

Kalu wanda kuma tsohon Gwamnan Jihar Abia ne ya ce, “Kodayake an yi yunkuri, amma ba mu bari hakan ta faru ba. Shi ya sa kullum nake cewa mu ’yan gida daya ne, kuma hakan ba zai faru ba,” in ji shi.

Ya jaddada cewa Majalisar Dattawa na da hadin kai kuma tana mayar da hankali kan aikinta na doka, musamman wajen tallafa wa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu domin fuskantar kalubalen tattalin arziki da ’yan Najeriya ke fuskanta.

‘Soludo zai iya komawa APC’

Dangane da ci gaban siyasa a Kudu Maso Gabas, Kalu ya nuna yiwuwar Gwamnan Jihar Anambra, Farfesa Charles Soludo, zai sauya sheka zuwa jam’iyyar APC mai mulki.

A yayin da yake amsa tambaya kan makomar siyasar Soludo, Kalu ya ce: “Ina ganin bayan shari’o’in da ke gabansa, Soludo mutum ne mai ra’ayin cigaba kamar ni, Shugaba Tinubu, da Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, da kuma gwamnonin APC na Imo, Ebonyi, Enugu da sauransu. Don haka Soludo mutum ne mai ra’ayin ci gaba.”

“Ba na ganin wani abu ne da ba daidai ba idan ya shigo APC. A gaskiya, an tabbatar da cewa zai shiga jam’iyyar. Babu wani zabi da ya fi dacewa da shi face ya zo mu hada kai.”

Kalu ya kuma bayar da tabbacin cewa Shugaba Tinubu zai samu wa’adi na biyu, yana mai cewa a halin yanzu babu wata gagarumar adawa da ke kalubalantar shi.

“Shin akwai wani da ke fafatawa da shi? Zaben nan Tinubu ne da Tinubu, kamar yadda Soludo ya fafata da kansa a zaben Abia.”

“Shugaban kasa ba shi da adawa. Jam’iyyarmu tana da karfi a kasa kuma muna tare da jama’a. Babu wanda zai ce ba mu da jama’a. Za mu ci gaba da yin iya kokarinmu domin ganin talakawan Najeriya sun samu ci gaba,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle
  • Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna
  • Amurka Na Shirye-Shiryen Aikewa Da Sojoji Guda 1000 A Iyakar Isra’ila Da Yankin Gaza
  • Wike: Za mu kare duk wani soja da ke aiki bisa doka — Ministan Tsaro
  • Za Mu Kare Sojojin Da Ke Bakin Aiki — Ministan Tsaro
  • Sheikh Qassem: Kawar Da Hizbullah Ne Babban Burin Isra’ila A Lebanon
  • UNICEF ta ce Isra’ila ta hana allurar rigakafin yara masu mahimmanci shiga Gaza
  • Yadda muka daƙile yunƙurin tsige Akpabio daga shugabancin Majalisa – Orji Kalu
  • Gaza : Isra’ila ta karya yarjejeniyar tsagaita wuta sau 282 tun bayan aiwatar da ita
  • Gwamnatin Tarayya Ta Jinjinawa Gwamnan Jigawa Bisa Ayyukan Ci Gaban Jihar