Fiye Da Falasdinawa 300 Ne Su Ka Yi Shahada Da Jikkata Daga Safiyar Yau Juma’a
Published: 16th, May 2025 GMT
HKI tana ci gaba da yi wa Falasdinawa kisan kiyashi a Gaza wanda ya ci rayukan Falasdiniwa kusan 300 da su ka hada kananan yara da mata.
Tashar talabijin din ‘almayadin’ ta ambaci cewa;Tun da asubahin yau ne dai sojojin mamayar su ka fara kai wadannan munanan hare-haren wanda ba komai ba ne, sai kisan kiyashi akan Falasdinawada suke fama da matsananciyar yunwa saboda rashin abinci.
Bugu da kari, mafi yawancin Falasdinawan da HKI take kai wa hare-haren suna rayuwa ne a cikin hemomi bayan da ta rushe musu gidajensu.
Ma’aikatar kiwon lafiya ta Falasdinu ta sanar a cewa; A cikin sa’oi 24 da su ka gabata, adadin wadanda su ka yi shahada sun kai 109, kuma tuni an fito da gawawwakinsu daga gine-gine da hemomin da su ka fada a kansu, yayin da wasu 216 su ka jikkata.
A jiya kadai, adadin Falasdinawan da su ka yi shahada sun haura 100. Baya ga wadanda su ka yi shahadar, da akwai kuma wani adadi na falasdinawa da ya kai 100 da sun bace.
Daga 7 ga watan Oktoba na 2023 zuwa yanzu, adadin Falasdinawan da su ka yi shahada sun kai dubu 53, da 119, sai kuma wadanda su ka jikkata da sun kai 120,114.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Za A Yi Wa Masu Lalurar Ido Aiki Kyauta A Jihar Jigawa
Wata kungiya mai zaman kanta ta tantance mutane 60 wadanda za’a yiwa aikin ido kyauta a wasu kananan hukumomi 2 dake jihar Jigawa.
Shugaban kungiyar mai zaman kanta, Alhaji Umar Saidu Yelleman Jambola ya bayyana cewar za’a gudanar da aikin ne kyauta ga mutane 60 a kananan hukumomin Malam madori da kaugama.
A cewar sa wadanda za su ci moriyar aikin an zabi su ne daga dukkanin mazabu da ke kananan hukumomin.
Sa’idu Yalleman ya kara da cewa yara da manya ne za su amfana da aikin idon kyauta wanda kungiyar ta dau nauyi.
Da yake jawabi ga manema labarai, Dr Abubakar Adamu yace wadanda aka tantance kuma suke da yanar ido za’a kai su asibitin koyarwa na Malam Aminu Kano dake birnin Kano don yi masu aikin.
Wakilan shirin na kananan hukumomin Malam Madori and Kaugama, Malam Bashari Suleiman da Dan-Alhaji sun ce a mako mai zuwa ne za’a gudanar da aikin ga wadanda aka tantance.
Da yake jawabi a madadin wadanda zasu ci moriyar aikin, wakilan mazabun Garun-Gabas da Mairakumi, Mustapha Bala da Suraja Garba sun yabawa kokarin Alhaji Umar Jambola.
A nasu jawaban, Shugabannin kananan hukumomin Kaugama da Malam madori, Alhaji Salisu Sani Garun-Gabas da Alhaji Masaki Usman Dansule sun yaba da hobbasan Umar Jambola na taimakawa masu karamin karfi a kananan hukumominsu.
Usman Mohammed Zaria