Aminiya:
2025-05-17@03:39:16 GMT

Kwankwaso ya fice daga NNPP tun a 2023 — Shugaban jam’iyya

Published: 16th, May 2025 GMT

Shugaban jam’iyyar NNPP na ƙasa, Dokta Agbo Gilbert Major, ya tabbatar da cewa tsohon gwamnan Jihar Kano kuma jagoran Kwankwasiyya, Rabi’u Musa Kwankwaso, ba ya tare da jam’iyyar tun watan Yunin 2023.

Ya ce Kwankwaso ya fice daga NNPP tare da mabiyansa na Kwankwasiyya.

Tinubu zai halarci rantsar da sabon Fafaroma Leo Cikin makonni kaɗan Obasanjo ya murƙushe Boko Haram — Atiku

A yayin wata tattaunawa da aka yi da shi a shirin ‘Daily Politics’ na Trust TV, Dokta Major ya ce:

“Kwankwaso ya zama tarihi a jam’iyyar NNPP.

Ya zo a wani lokaci, sannan ya tafi da nasa mutanen.

“Bisa tsarinmu da kuma hukuncin kotu daga Abiya da Abuja, ba ya cikin jam’iyyar tun 2023.”

Shugaban jam’iyyar ya kuma yi bayani game da sauya sheƙa da wasu ‘yan siyasa ke yi daga jam’iyyar, inda ya bayyana cewa yawancin waɗanda suka fice ba su da matsala da NNPP, sai dai da tsagin Kwankwasiyya.

Ya ce waɗanda suka fice har yanzu suna da alaƙa da jam’iyyar.

“Suna ci gaba da faɗa mana cewa ba su da matsala da NNPP, matsalarsu dai ita ce tsarin tafiyar Kwankwasiyya. Wasu na cewa ta koma tafiyar mutum ɗaya, kuma sun gaji da haka,” in ji Major.

Ya ƙara da cewa waɗanda suka fice sun taka muhimmiyar rawa wajen nasarar NNPP, musamman a Jihar Kano, kuma ficewarsu babbar asara ce.

Amma ya ce jam’iyyar na nan da ƙarfinta – duk da ba ta tare da Kwankwasiyya.

Dokta Major ya kuma ƙi bayyana yadda dangantakar Kwankwaso ta ke da fadar shugaban ƙasa.

“Yana da ’yancin zuwa inda ya ga dama. Mu fa mun wuce wannan batun, mu yanzu muna duba gaba ne.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: jam iyya Kwankwaso Siyasa a jam iyyar

এছাড়াও পড়ুন:

Cikin makonni kaɗan Obasanjo ya murƙushe Boko Haram — Atiku

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya ce tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo ne ya murƙushe ƙungiyar Boko Haram lokacin da ta fara bayyana a shekarar 2002.

Atiku, wanda ya yi mataimakin shugaban ƙasa daga 1999 zuwa 2007, ya bayyana hakan ne a wata ganawa da masu ruwa da tsaki daga Jihar Kogi a birnin Abuja.

Gwamnatin Katsina za ta gina birnin dawakai na farko a Afirka Ƙungiya mai alaƙa da Alƙa’ida ta yi iƙirarin kashe sojoji 200 a Buarkina Faso

Ya bayyana cewa lokacin da Boko Haram ta fara tayar da hankali a Jihar Yobe, Obasanjo ya kira shi domin neman shawararsa.

Atiku, ya bayar da shawarar a kira shugabannin tsaro a ba su wa’adin daƙile lamarin, ko su sauka daga muƙamansu.

Obasanjo ya amince, ya kira su, ya ba su umarnin ɗaukar matakin gaggawa.

Atiku, ya ce cikin makonni kaɗan, dakarun tsaro suka murƙushe ƙungiyar Boko Haram a Yobe, kuma ba ta sake bayyana ba har sai da suka bar mulki.

Atiku, ya soki shugabannin da suka biyo bayan gwamnatinsu, inda ya bayyana cewa sun gaza ɗaukar matakin da ya dace kan matsalar tsaro.

“Babu ƙwarin gwiwar siyasa daga shugabanni,” in ji shi.

“Mutane na mutuwa, amma shugabanni ba su damu ba. Wannan babbar gazawa ce a hakar shugabanci.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Chadi: An Kama Tsohon Fira Minista Kuma Jagoran ‘Yan Hamayyar Siyasa
  • Cikin makonni kaɗan Obasanjo ya murƙushe Boko Haram — Atiku
  • NAJERIYA A YAU: Shin Jam’iyyar NNPP Za Ta Kai Labari A 2027?
  • Ganduje ya halarci Majalisar Wakilai don sheda ’Yan Majalisa 2 zuwa APC
  • NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC
  • Kasar Katar Za Ta Sayi Jirage Samfurin Boeing 106 Daga Amurka Da Kudi Dala Biliyan 400
  • Wata Kotu A Amurka Ta Bukaci A Saki Wani Malami Mai Goyon Bayan Palasdinawa A Jami’ar Georgetown academic
  • ’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa
  • Donal Trump Ya Ce Zai Dagewa Kasar Siriya Dukkan Takunkuman Tattalinn Arzikin Da Ta Dora Mata