Aminiya:
2025-10-13@20:09:41 GMT

Kwankwaso ya fice daga NNPP tun a 2023 — Shugaban jam’iyya

Published: 16th, May 2025 GMT

Shugaban jam’iyyar NNPP na ƙasa, Dokta Agbo Gilbert Major, ya tabbatar da cewa tsohon gwamnan Jihar Kano kuma jagoran Kwankwasiyya, Rabi’u Musa Kwankwaso, ba ya tare da jam’iyyar tun watan Yunin 2023.

Ya ce Kwankwaso ya fice daga NNPP tare da mabiyansa na Kwankwasiyya.

Tinubu zai halarci rantsar da sabon Fafaroma Leo Cikin makonni kaɗan Obasanjo ya murƙushe Boko Haram — Atiku

A yayin wata tattaunawa da aka yi da shi a shirin ‘Daily Politics’ na Trust TV, Dokta Major ya ce:

“Kwankwaso ya zama tarihi a jam’iyyar NNPP.

Ya zo a wani lokaci, sannan ya tafi da nasa mutanen.

“Bisa tsarinmu da kuma hukuncin kotu daga Abiya da Abuja, ba ya cikin jam’iyyar tun 2023.”

Shugaban jam’iyyar ya kuma yi bayani game da sauya sheƙa da wasu ‘yan siyasa ke yi daga jam’iyyar, inda ya bayyana cewa yawancin waɗanda suka fice ba su da matsala da NNPP, sai dai da tsagin Kwankwasiyya.

Ya ce waɗanda suka fice har yanzu suna da alaƙa da jam’iyyar.

“Suna ci gaba da faɗa mana cewa ba su da matsala da NNPP, matsalarsu dai ita ce tsarin tafiyar Kwankwasiyya. Wasu na cewa ta koma tafiyar mutum ɗaya, kuma sun gaji da haka,” in ji Major.

Ya ƙara da cewa waɗanda suka fice sun taka muhimmiyar rawa wajen nasarar NNPP, musamman a Jihar Kano, kuma ficewarsu babbar asara ce.

Amma ya ce jam’iyyar na nan da ƙarfinta – duk da ba ta tare da Kwankwasiyya.

Dokta Major ya kuma ƙi bayyana yadda dangantakar Kwankwaso ta ke da fadar shugaban ƙasa.

“Yana da ’yancin zuwa inda ya ga dama. Mu fa mun wuce wannan batun, mu yanzu muna duba gaba ne.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: jam iyya Kwankwaso Siyasa a jam iyyar

এছাড়াও পড়ুন:

Wakiliyar CMG Ta Zanta Da Farfesa Jeffrey Sachs Na Jami’ar Columbia

Farfesa Jeffrey Sachs na jami’ar Columbia, ya yaba wa nasarorin da Sin ta samu, inda ya ce, “shawarar ‘ziri daya da hanya daya’, wani shiri ne mai ban mamaki kuma na musamman.”

 

Farfesa Sachs ya fadi hakan ne a kwanan nan, yayin da wakiliyar rukunin gidan rediyo da talibijin kasar Sin wato CMG ta zanta da shi. Ya kuma bayyana cewa, kamar yadda shugaban kasar Xi Jinping ya fada a karon farko, yayin gabatar da wannan shawara, tushen ta ya samo asali ne daga hanyar kasuwanci ta hanyar siliki, hanyar dake da tarihin fiye da shekaru dubu biyu tsakanin yankin gabas da yamma. Ya ce, “Idan kina nazarin tattalin arziki kamar yadda nake yi, za ki yi imanin cewa, ainihin ciniki shi ne samun moriyar juna, da habaka al’adu, da samar da ingantattun kayayyaki, wanda ke amfanar mutane daga sassa daban-daban na duniya, to za ki amince cewa ciniki shi ne tsarin gaskiya na samun riba ga kowa. Ina goyon bayan wannan ra’ayi na hadin kai, kuma na yi imanin cewa yana da fa’ida mai yawa. Shirin Sin na tabbatar da shawarar ‘ziri daya da hanya daya’ cikin hadin gwiwa, ya yi kokari sosai a fannin inganta hadin kai da kara zurfafa mu’ammala.” (Amina Xu)

 

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Li Qiang Ya Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Koriya Ta Arewa October 11, 2025 Daga Birnin Sin Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza October 10, 2025 Daga Birnin Sin Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya October 10, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dan Majalisar Tarayyar Kaduna ya bar Jam’iyyar PDP
  • Zaben Kamaru: Issa Tchiroma Bakary ya lashe yankunan da Biya ke da rinjaye
  • Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa
  • Ayyukan Da Suka Sauya Fuskar Zamfara A Ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal
  • Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
  • Wakiliyar CMG Ta Zanta Da Farfesa Jeffrey Sachs Na Jami’ar Columbia
  • Li Qiang Ya Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Koriya Ta Arewa
  • Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
  • Pakistan Ta Kai Hari Kan Kasar Afganistan, Inda Ake Rade-Radin Kashe Shugaban Taliban Na Kasarta
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida