Kwankwaso ya fice daga NNPP tun a 2023 — Shugaban jam’iyya
Published: 16th, May 2025 GMT
Shugaban jam’iyyar NNPP na ƙasa, Dokta Agbo Gilbert Major, ya tabbatar da cewa tsohon gwamnan Jihar Kano kuma jagoran Kwankwasiyya, Rabi’u Musa Kwankwaso, ba ya tare da jam’iyyar tun watan Yunin 2023.
Ya ce Kwankwaso ya fice daga NNPP tare da mabiyansa na Kwankwasiyya.
Tinubu zai halarci rantsar da sabon Fafaroma Leo Cikin makonni kaɗan Obasanjo ya murƙushe Boko Haram — AtikuA yayin wata tattaunawa da aka yi da shi a shirin ‘Daily Politics’ na Trust TV, Dokta Major ya ce:
“Kwankwaso ya zama tarihi a jam’iyyar NNPP.
“Bisa tsarinmu da kuma hukuncin kotu daga Abiya da Abuja, ba ya cikin jam’iyyar tun 2023.”
Shugaban jam’iyyar ya kuma yi bayani game da sauya sheƙa da wasu ‘yan siyasa ke yi daga jam’iyyar, inda ya bayyana cewa yawancin waɗanda suka fice ba su da matsala da NNPP, sai dai da tsagin Kwankwasiyya.
Ya ce waɗanda suka fice har yanzu suna da alaƙa da jam’iyyar.
“Suna ci gaba da faɗa mana cewa ba su da matsala da NNPP, matsalarsu dai ita ce tsarin tafiyar Kwankwasiyya. Wasu na cewa ta koma tafiyar mutum ɗaya, kuma sun gaji da haka,” in ji Major.
Ya ƙara da cewa waɗanda suka fice sun taka muhimmiyar rawa wajen nasarar NNPP, musamman a Jihar Kano, kuma ficewarsu babbar asara ce.
Amma ya ce jam’iyyar na nan da ƙarfinta – duk da ba ta tare da Kwankwasiyya.
Dokta Major ya kuma ƙi bayyana yadda dangantakar Kwankwaso ta ke da fadar shugaban ƙasa.
“Yana da ’yancin zuwa inda ya ga dama. Mu fa mun wuce wannan batun, mu yanzu muna duba gaba ne.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: jam iyya Kwankwaso Siyasa a jam iyyar
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Dokokin Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukumar Rano Na Tsawon Watanni Uku
Majalisar Dokokin Jihar Kano ta dakatar da Shugaban Karamar Hukumar Rano, Alhaji Muhammad Naziru Ya’u, na tsawon watanni uku sakamakon zarge-zargen aikata ba daidai ba.
An yanke wannan hukunci ne a zauren majalisa ƙarƙashin jagorancin Shugaban Majalisar, Alhaji Jibril Isma’il Falgore, bayan kwamitin majalisar kan ƙorafe-ƙorafe ya gabatar da rahoton bincikensa.
Yayin gabatar da rahoton, Shugaban Kwamitin wanda shi ne shugaban masu rinjaye, Alhaji Lawan Hussaini Dala, ya ce binciken ya samo asali ne daga ƙorafin da kansiloli tara daga cikin goma na Rano suka sanya wa hannu.
A cewarsa, ƙorafin ya zargi shugaban da yin sakacin kuɗi, sayar da shaguna, da karkatar da takin zamani da aka ware wa ƙaramar hukumar, tare da wasu zarge-zarge daban.
Lawan ya bayyana cewa ko da yake shugaban ya ƙi amincewa da waɗannan zarge-zargen, ‘yan majalisar bisa ga Sashe na 128 na Kundin Tsarin Mulki da kuma Sashe na 55 (1–6) na Dokar Kananan Hukumomi ta Kano ta 2006, sun ba da shawarar a dakatar da shi na tsawon watanni uku domin gudanar da cikakken bincike.
Sauran shawarwarin sun haɗa da miƙa cikakken bayanin kuɗin shekarar 2025 na Karamar Hukumar Rano cikin gaggawa, da kuma naɗa mataimakin shugaban ya rike mukamin na wucin gadi yayin dakatarwar.
Bayan tattaunawa mai zurfi, majalisar ta amince da shawarwarin kwamitin, wanda hakan ya jawo dakatar da shugaban tare da sanya ƙaramar hukumar ƙarƙashin kulawa ta wucin gadi.
Daga Khadijah Aliyu