Kwankwaso ya fice daga NNPP tun a 2023 — Shugaban jam’iyya
Published: 16th, May 2025 GMT
Shugaban jam’iyyar NNPP na ƙasa, Dokta Agbo Gilbert Major, ya tabbatar da cewa tsohon gwamnan Jihar Kano kuma jagoran Kwankwasiyya, Rabi’u Musa Kwankwaso, ba ya tare da jam’iyyar tun watan Yunin 2023.
Ya ce Kwankwaso ya fice daga NNPP tare da mabiyansa na Kwankwasiyya.
Tinubu zai halarci rantsar da sabon Fafaroma Leo Cikin makonni kaɗan Obasanjo ya murƙushe Boko Haram — AtikuA yayin wata tattaunawa da aka yi da shi a shirin ‘Daily Politics’ na Trust TV, Dokta Major ya ce:
“Kwankwaso ya zama tarihi a jam’iyyar NNPP.
“Bisa tsarinmu da kuma hukuncin kotu daga Abiya da Abuja, ba ya cikin jam’iyyar tun 2023.”
Shugaban jam’iyyar ya kuma yi bayani game da sauya sheƙa da wasu ‘yan siyasa ke yi daga jam’iyyar, inda ya bayyana cewa yawancin waɗanda suka fice ba su da matsala da NNPP, sai dai da tsagin Kwankwasiyya.
Ya ce waɗanda suka fice har yanzu suna da alaƙa da jam’iyyar.
“Suna ci gaba da faɗa mana cewa ba su da matsala da NNPP, matsalarsu dai ita ce tsarin tafiyar Kwankwasiyya. Wasu na cewa ta koma tafiyar mutum ɗaya, kuma sun gaji da haka,” in ji Major.
Ya ƙara da cewa waɗanda suka fice sun taka muhimmiyar rawa wajen nasarar NNPP, musamman a Jihar Kano, kuma ficewarsu babbar asara ce.
Amma ya ce jam’iyyar na nan da ƙarfinta – duk da ba ta tare da Kwankwasiyya.
Dokta Major ya kuma ƙi bayyana yadda dangantakar Kwankwaso ta ke da fadar shugaban ƙasa.
“Yana da ’yancin zuwa inda ya ga dama. Mu fa mun wuce wannan batun, mu yanzu muna duba gaba ne.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: jam iyya Kwankwaso Siyasa a jam iyyar
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnan Bauchi zai ƙirƙiro sabbin masarautu
Gwamna Bala Mohammed na Jihar Bauchi ya amince da kafa kwamitin mambobi 41 da nufin kafa sabbin masarautu a faɗin jihar.
Wata sanarwa da kakakin gwamnan, Mukhtar Gidado, ya fitar ta bayyana cewa kwamitin ya ƙunshi fitattun mambobi 41 da aka zabo daga ɓangarori daban-daban, ciki har da sarakunan gargajiya, ƙwararru, malaman jami’a, wakilan ƙungiyoyin farar hula, lauyoyi, jami’an tsaro, da ƙungiyoyin addini.
Sanarwar ta ce, “Wannan shiri ya biyo bayan kiran da gwamnatin jihar ta yi tun da farko na gayyatar al’ummomi da su gabatar da buƙatunsu na sabbin masarautun gargajiya.
“Kwamitin yana da alhakin tantance waɗannan bukatun bisa ƙa’idar adalci, daidaito, shigar da kowa cikin harkokin siyasa da zamantakewa, da ɗorewar tattalin arziki.”
Alhaji Hamza Koshe ne zai jagoranci kwamitin, tare da Mai Shari’a Habibu Idris a matsayin Mataimakin Shugaba. Sauran mambobin sun haɗa da manyan jami’an gwamnati, masu ba da shawara na musamman, da wakilai daga Ƙungiyar Lauyoyi ta Najeriya (NBA), Ƙungiya Jama’atu Nasril Islam (JNI), Ƙungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN), Kungiyar ’Yan Jarida ta Ƙasa (NUJ), da kuma hukumomin tsaro daban-daban.
Farfesa Ibrahim Garba, wani masanin tarihi daga Jami’ar Maiduguri, yana cikin ƙwararrun da aka kawo don jagorantar kwamitin kan la’akari da al’adu da tarihi.
An shirya cewa Gwamna Bala Mohammed zai ƙaddamar da kwamitin ranar Alhamis, 3 ga Yuli, a Gidan Gwamnati, Bauchi, da karfe 10:00 na safe, in ji Gidado.
Ya ƙara da cewa duk wannan tsari na da nufin ƙarfafa masarautun gargajiya, inganta shigar jama’a cikin harkokin mulki, da kuma raya al’adun jihar. (NAN)