Wata ƙungiyar ’yan ta’adda mai alaƙa da ƙungiyar Alƙa’ida ta ɗauki alhakin kashe sojoji 200 a ƙasar Burkina Faso.

Ƙungiyar mai suna Jama’at Nusrat al-Islam wal-Muslimin (JNIM), ta ɗauki alhakin kai hari a Djibo, arewacin Burkina Faso, tana mai cewa ta kashe sojoji 200.

Wannan ikirarin, wanda cibiyar SITE Intelligence Group mai hedkwata a Amurka ta ruwaito a ranar Alhamis, ya biyo bayan iƙirarin JNIM na baya da ta yi na kashe sojoji 60 a harin.

SITE Intelligence Group, wacce ke sanya idanu kan ayyukan ƙungiyoyin masu tsattsauran ra’ayi ta intanet, ta nuna cewa harin wani bangare ne na ƙaruwar ayyukan JNIM a Burkina Faso a cikin watan da ya gabata, wanda ya haifar da asarar rayuka da dama.

Ɗaukar fansa: Sojoji sun ragargaji Boko Haram a Dajin Sambisa An kama wata mata kan safarar makamai zuwa Katsina

Duk da cewa babu wani adadi na asarar rayuka a hukumance daga gwamnatin Burkina Faso, rahotanni sun ruwaito mazauna yankin Djibo sun nuna cewa an kashe sojoji da fararen hula da dama.

Sai dai, wata majiyar sojojin Burkina Faso, da take magana da Al Jazeera, ta nuna cewa ƙungiyar ’uan tayar da ƙayar bayan na iya aringizon da adadin waɗanda suka mutu.

Gwamnatin Burkina Faso har yanzu ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance kan harin ba.

Burkina Faso tana fama da ƙaruwar rikicin ƙungiyoyin masu ɗauke da makamai a yankin Sahel.

Tun daga shekarar 2019, ƙaruwar tashe-tashen hankula ya raba sama da mutane miliyan da gidajensu, kuma ya nakasa muhimman ababen more rayuwa na farar hula, kamar asibitoci da makarantu.

Duk da alkawuran da gwamnatin mulkin soja, ƙarƙashin jagorancin Ibrahim Traore, ta yi na inganta yanayin tsaro da ƙulla sabbin ƙawance na tsaro da Rasha, ƙalubalen tsaro na ƙasar sun ƙara tabarbarewa a tsawon lokaci.

Burkina Faso ce ta kan gaba a jerin ƙasashe masu fama da ta’addanci na duniya (Global Terrorism Index) na shekarar 2024, inda ta zama kasa ta farko cikin sama da shekaru goma, baya ga Afghanistan ko Iraƙi, da ta mamaye matsayi na farko.

A shekarar 2023, kusan mutane 2,000 aka kashe a hare-haren ta’addanci 258 a ƙasar, wanda ya kai kusan kashi ɗaya cikin huɗu na mutuwar da ta shafi ta’addanci a duniya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan ta adda hare hare Ibrahim Traore

এছাড়াও পড়ুন:

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

Mai shari’a Dahiru ya amince da buƙatar, ya kuma ɗage shari’ar zuwa ranar 12 ga watan Disamba, 2025, domin ci gaba da sauraron shari’ar.

Ƙuli-ƙuli dai nau’in abin ci ne mai taushi da ake yi da gyaɗa, ana soyawa har sai ya zama ƙura-ƙura ta yadda za a ci cikin nishaɗi.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi October 31, 2025 Manyan Labarai Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar October 31, 2025 Manyan Labarai NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NARD Ta Yi Fatali Da Iƙirarin Gwamnatin Tarayya Na Ba Ta ₦43bn, Kuma Yajin Aiki Na Nan
  • Ministar Jin Dadin Jama’a ta Sudan: Mayakan RSF Sun Kashe Mata 300 Da Yi Wa 25 Fyade A El Fasher
  • Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka
  • IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya
  • Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump
  • PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu da ke da alaƙa da Wike
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede