Wata ƙungiyar ’yan ta’adda mai alaƙa da ƙungiyar Alƙa’ida ta ɗauki alhakin kashe sojoji 200 a ƙasar Burkina Faso.

Ƙungiyar mai suna Jama’at Nusrat al-Islam wal-Muslimin (JNIM), ta ɗauki alhakin kai hari a Djibo, arewacin Burkina Faso, tana mai cewa ta kashe sojoji 200.

Wannan ikirarin, wanda cibiyar SITE Intelligence Group mai hedkwata a Amurka ta ruwaito a ranar Alhamis, ya biyo bayan iƙirarin JNIM na baya da ta yi na kashe sojoji 60 a harin.

SITE Intelligence Group, wacce ke sanya idanu kan ayyukan ƙungiyoyin masu tsattsauran ra’ayi ta intanet, ta nuna cewa harin wani bangare ne na ƙaruwar ayyukan JNIM a Burkina Faso a cikin watan da ya gabata, wanda ya haifar da asarar rayuka da dama.

Ɗaukar fansa: Sojoji sun ragargaji Boko Haram a Dajin Sambisa An kama wata mata kan safarar makamai zuwa Katsina

Duk da cewa babu wani adadi na asarar rayuka a hukumance daga gwamnatin Burkina Faso, rahotanni sun ruwaito mazauna yankin Djibo sun nuna cewa an kashe sojoji da fararen hula da dama.

Sai dai, wata majiyar sojojin Burkina Faso, da take magana da Al Jazeera, ta nuna cewa ƙungiyar ’uan tayar da ƙayar bayan na iya aringizon da adadin waɗanda suka mutu.

Gwamnatin Burkina Faso har yanzu ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance kan harin ba.

Burkina Faso tana fama da ƙaruwar rikicin ƙungiyoyin masu ɗauke da makamai a yankin Sahel.

Tun daga shekarar 2019, ƙaruwar tashe-tashen hankula ya raba sama da mutane miliyan da gidajensu, kuma ya nakasa muhimman ababen more rayuwa na farar hula, kamar asibitoci da makarantu.

Duk da alkawuran da gwamnatin mulkin soja, ƙarƙashin jagorancin Ibrahim Traore, ta yi na inganta yanayin tsaro da ƙulla sabbin ƙawance na tsaro da Rasha, ƙalubalen tsaro na ƙasar sun ƙara tabarbarewa a tsawon lokaci.

Burkina Faso ce ta kan gaba a jerin ƙasashe masu fama da ta’addanci na duniya (Global Terrorism Index) na shekarar 2024, inda ta zama kasa ta farko cikin sama da shekaru goma, baya ga Afghanistan ko Iraƙi, da ta mamaye matsayi na farko.

A shekarar 2023, kusan mutane 2,000 aka kashe a hare-haren ta’addanci 258 a ƙasar, wanda ya kai kusan kashi ɗaya cikin huɗu na mutuwar da ta shafi ta’addanci a duniya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan ta adda hare hare Ibrahim Traore

এছাড়াও পড়ুন:

Iran : harin da Isra’ila ta kai ‘ ayyana yaki’ ne_ Araghchi

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce matakin da gwamnatin Isra’ila ta dauka a kan kasar tamkar shelanta yaki ne.

Araghchi ya bayyana hakan ne a cikin wata wasika da ya aikewa babban sakatare na MDD da kuma shugaban kwamitin sulhu bayan da Isra’ila ta kai munanan hare-hare kan wuraren soji da cibiyoyin nukiliya da kuma wuraren zama wanda ya yi sanadiyar mutuwar wasu manyan kwamandojin dakarun kare juyin juya halin Musulunci (IRGC), masana kimiyyar nukiliya da fararen hula na iran.

“Wadannan ayyuka na zalunci ba wai kawai sun zama babban cin zarafi ne ga ‘yancin kan kasar Iran a matsayinta na mamba mai cin gashin kanta a Majalisar Dinkin Duniya ba, amma kamar yadda dokokin kasa da kasa da dokokin jin kai na duniya, ciki har da yarjejeniyar Geneva, suka tanada wannan na daga cikin ayyukan wuce gona da iri da laifukan yaki.”

Ministan harkokin wajen na Iran ya yi kira ga kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da ya sauke nauyin da ke wuyansa, ya yi kakkausar suka ga wannan ta’addanci tare da daukar matakin gaggawa kan Isra’ila.

Ya kara da cewa “Jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta yi aiki da cikakkiyar azama wajen kare ‘yancinta, al’ummarta da kuma tsaron kasarta. Wannan wani hakki ne da ba za a iya tattaunawa da shi ba.”

Daga cikin hare-haren da ta kai, Isra’ila ta kai hari kan Cibiyar Nukiliya ta Natanz da ke tsakiyar kasar Iran, wadda ke aiki karkashin cikakken kulawar Hukumar Makamashin Nukiliya ta Duniya (IAEA), in ji shi.

Babban jami’in diflomasiyyar na Iran ya yi gargadin cewa hare-haren ta’addanci na gwamnatin Tel Aviv na jefa rayuwar fararen hular Iran cikin hadari tare da haifar da barazana ga zaman lafiya da tsaro a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Aike Da Sako Ga Al’ummar Iran Bayan Harin Da Iran Ta Fuskanta
  • Iran : harin da Isra’ila ta kai ‘ ayyana yaki’ ne_ Araghchi
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • Harin Isra’ila a kan Iran ya jefa yankin Gabas ta Tsakiya cikin zama dar-dar
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara
  • Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara
  • An kashe jaririn wata 9 da wasu 3 a Filato
  • ‘Yan Bindiga Sun Sake Kashe Mutane 8 A Jihar Filato
  • An kashe mutum 15 a sabbin hare-hare a Filato
  • Ana zargin uwa da kashe ’yarta kan Naira 100 a Zariya