HausaTv:
2025-08-15@07:10:32 GMT

Human Rights Watch : Katange Gaza mataki ne na share al’umma

Published: 15th, May 2025 GMT

Kungiyar kare hakkin bil’adama ta Human Rights Watch ta zargi Isra’ila da amfani da katangewar da ta yi wa Gaza a matsayin makamin kawar da wata al’umma.

A wani rahoto data fitar yau  Alhamis, kungiyar ta Human Rights Watch ta zargi Isra’ila da yin amfani da shingen da aka yi wa Zirin Gaza a matsayin “wani makami na share al’umma,” yayin da hukumomin Isra’ila suka hana shigar da duk wani agajin jin kai cikin yankin Falasdinu tun ranar 2 ga Maris.

Katange zirin da Isra’ila ta yi ya fi karfin dabarun soji, ya kai wani yunkuri na share al’umma inji Federico Borello, darakan zatarwa mai riko na kungiyar a cikin wata sanarwa da ya caccaki shirin Isra’ila na zaunar da mutanan Gaza miliyan biyu a wani shinge da aka takaice lamura tare da maida yankin wani kufai da ba za’a iya rayuwa a ciki ba.

Sojojin Isra’ila sun sake kai hare-hare a zirin Gaza a ranar 18 ga Maris, ta hanyar keta yarjejeniyar tsagaita wuta da kungiyar Hamas, inda suka kashe dubban Falasdinawa tare da raunata wasu da dama.

Akalla Falasdinawa 53,010 aka kashe, akasari mata da kananan yara, yayin da wasu 119,998 suka jikkata a munanan hare-haren da sojojin Isra’ila suka kai a Gaza tun ranar 7 ga Oktoba, 2023.

Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta fada bay abaya nan cewa a shirye ta ke ta shiga tattaunawa cikin gaggawa domin cimma yarjejeniyar tsagaita wuta mai dorewa a zirin Gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Nijeriya ta sake ƙulla alaƙar tsaro da Isra’ila

Nijeriya da ƙasar Isra’ila sun sake jaddada aniyarsu ta ƙarfafa haɗin gwiwar tsaro a fannoni masu muhimmanci kamar yaƙi da ta’addanci, musayar bayanan sirri, samar da kuɗin tsaro da kuma horaswa ta musamman.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwar haɗin gwiwa wadda Ƙaramar Ministar Harkokin Wajen Nijeriya, Ambasada Bianca Odumegwu-Ojukwu, da Mataimakiyar Ministan Harkokin Waje ta Isra’ila, Sharren Haskel-Harpaz suka fitar bayan wani taro na musamman da suka gudanar ranar Litinin a Abuja.

Tinubu na amfani da EFCC ya muzguna wa ’yan adawa — Atiku Amurka da China sun dakatar da harajin da suka ƙaƙaba wa juna

Sanarwar, wadda mai magana da yawun Ofishin Ƙaramar Ministar Harkokin Wajen, Dokta Magnus Eze ya fitar, ta ce taron ya nuna alaƙa mai ɗorewa da muhimmanci tsakanin ƙasashen biyu.

A  yayin taron, wakilan ƙasashen biyu sun tattauna batutuwan da suka shafi tsaro a duniya, musamman yaƙi da ta’addanci, da kuma inganta hulɗar siyasa da tattalin arziki.

Ministocin biyu sun yi ƙara jan hankali kan barazanar ta’addanci a duniya, inda suka ce dole ne ƙasashe su haɗa kai wajen yaƙi da shi, musamman wajen samun bayanai kan hanyoyin samar da kuɗaɗen da ke ɗaukar nauyin ta’addanci.

Mahalarta taron

Haka kuma, ƙasashen biyu sun amince su ƙara haɗin kai a fannonin da suka shafi ƙasa da ƙasa tare da mara wa juna baya a muhimman batutuwa masu kawo ci gaba.

Baya ga tsaro, taron ya mayar da hankali kan amfani da fasaha da ƙirkire-ƙirkire wajen kula da iyakoki, inganta ƙwarewar makamar aiki, musayar al’adu, yawon buɗe ido, noma, da ayyukan jakadanci da shige-da-fice.

Kazalika, ƙasashen sun amince da shirye-shiryen musayar ma’aikata da ziyarar ƙara ilimi, tare da kafa tsari na musamman domin ci gaba da tattaunawa da haɗin gwiwa a nan gaba.

A wani ɓangare na taron, an yi muhawara kan fasahar zamani wadda Ambasada Janet Olisa daga Ma’aikatar Harkokin Waje ta Nijeriya ta jagoranta tare da Ambasada Sharon Bar-Li daga Ma’aikatar Harkokin Waje ta Isra’ila.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kungiyoyin Kasa Da Kasa Sun Koka Kan Hana Shigar Da Kayayyakin Jin Kai Yankin Gaza
  • Bello Turji bai miƙa wuya ba har yanzu — DHQ
  • Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwaman Zamfara
  • Wani Bangaren Majalisar Dokokin Jihar Zamfara Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Da Ta Karbe Mulkin Jihar
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’Ila Har Sau Shida 
  • Wakilan Hamas sun isa a Alkahira don tattaunawa kan sabuwar shawarar tsagaita wuta a Gaza
  • Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana
  • Fursunoni 16 sun tsere daga gidan yarin Keffi
  • An kama ɗan shekara 18 kan zargin fashi da makami a Gombe
  • Nijeriya ta sake ƙulla alaƙar tsaro da Isra’ila