Human Rights Watch : Katange Gaza mataki ne na share al’umma
Published: 15th, May 2025 GMT
Kungiyar kare hakkin bil’adama ta Human Rights Watch ta zargi Isra’ila da amfani da katangewar da ta yi wa Gaza a matsayin makamin kawar da wata al’umma.
A wani rahoto data fitar yau Alhamis, kungiyar ta Human Rights Watch ta zargi Isra’ila da yin amfani da shingen da aka yi wa Zirin Gaza a matsayin “wani makami na share al’umma,” yayin da hukumomin Isra’ila suka hana shigar da duk wani agajin jin kai cikin yankin Falasdinu tun ranar 2 ga Maris.
Katange zirin da Isra’ila ta yi ya fi karfin dabarun soji, ya kai wani yunkuri na share al’umma inji Federico Borello, darakan zatarwa mai riko na kungiyar a cikin wata sanarwa da ya caccaki shirin Isra’ila na zaunar da mutanan Gaza miliyan biyu a wani shinge da aka takaice lamura tare da maida yankin wani kufai da ba za’a iya rayuwa a ciki ba.
Sojojin Isra’ila sun sake kai hare-hare a zirin Gaza a ranar 18 ga Maris, ta hanyar keta yarjejeniyar tsagaita wuta da kungiyar Hamas, inda suka kashe dubban Falasdinawa tare da raunata wasu da dama.
Akalla Falasdinawa 53,010 aka kashe, akasari mata da kananan yara, yayin da wasu 119,998 suka jikkata a munanan hare-haren da sojojin Isra’ila suka kai a Gaza tun ranar 7 ga Oktoba, 2023.
Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta fada bay abaya nan cewa a shirye ta ke ta shiga tattaunawa cikin gaggawa domin cimma yarjejeniyar tsagaita wuta mai dorewa a zirin Gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kafar Labaran Amurka Ta Ce: Isra’ila Ta Yi Mummunar Hasara A Yakinta Da Kasar Iran
Hasarar da gwamnatin mamayar Isra’ila ta yi a hare-haren da ta kai wa kasar Iran ya kai dala biliyan uku
Kafar watsa labaran Bloomberg ta Amurka ta yi kiyasin cewa: Hasarar da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta yi a yakin da ta yi da Iran ya kai kusan dala biliyan 3, saboda gyaran gine-gine da suka lalace da kuma biyan diyya ga kamfanoni.
Kafar ta Bloomberg ta bayyana a cikin wani rahoto cewa: Hasarar da gwamnatin mamayar Isra’ila ta yi na nuni da irin yadda Iran ta kutsa kai cikin tsaron Isra’ila a cikin kimanin makonni biyu da harba makaman masu linzami kan yankunan kasar.
Jaridar Amurka ta rawaito wani jami’in gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila yana cewa: “Wannan shi ne kalubale mafi girma da suka fuskanta, wanda ba a taba samun irin wannan barna a tarihin haramtacciyar kasar Isra’ila ba.”
Bayanai na hukuma da ma’aikatar kudi ta haramtacciyar kasar Isra’ila ta fitar a cikin wannan yanayi na nuni da cewa: Irin barnar da aka yi na nuna irin yadda makamai masu linzami na Iran suka kutsa cikin tsarin tsaron haramtacciyar kasar Isra’ila a cikin kimanin makonni biyu da harba makaman.