Hauhawar farashi ya ragu zuwa kashi 23.71 — NBS
Published: 15th, May 2025 GMT
Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS), ta bayyana cewa hauhawar farashi a Najeriya ya sauka kaɗan a watan Afrilu 2025 zuwa kashi 23.71, daga kashi 24.23 da aka samu a watan Maris.
Wannan na nuna cewa hauhawar farashi ya ragu idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata, inda a watan Afrilun 2024 aka samu kashi 33.
Wannan ragi da aka samu a watan Afrilu ya kai kusan kashi 10.
Har ila yau, hukumar ta ce hauhawar farashi daga wata zuwa wata ya ragu a watan Afrilu, inda aka samu kashi 1.86, ƙasa da kashi 3.90 da aka samu a watan Maris.
Wannan na nuna cewar hauhawar farashin kaya bai yi tsada da yawa ba a watan Afrilu idan aka kwatanta da watan Maris.
Farashin kayan abinci, wanda yafi shafar rayuwar yau da kullum, ya tsaya a kashi 21.26 a watan Afrilu, idan aka kwatanta da kashi 40.53 a bara.
Wannan ragin ya faru ne sakamakon sauyin yadda ake ƙididdigar bayanai.
A matakin wata-wata, hauhawar farashin kayan abinci ya kasance kashi 2.06 a watan Afrilu, wanda ya ragu daga kashi 2.18 da aka samu a watan Maris.
Ragi farashin wasu kayayyaki kamar garin masara, hatsi, kuɓewa busasshiya, garin doya, wake, da shinkafa ya taimaka wajen samun wannan sauƙi.
A tsaka-tsaki kuwa, hauhawar farashin abinci a cikin shekara guda zuwa watan Afrilu 2025 ya tsaya a kashi 31.43, wanda ya ragu da kashi 1.31 idan aka kwatanta da shekara da ta gabata wanda yake a kashi 32.74.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Hauhawar Farashi Kayan abinci Kayan Masarufi Kayayyaki idan aka kwatanta da da aka samu a watan hauhawar farashi a watan Afrilu a watan Maris
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Kefas Ya Bayyana Alhininsa Bisa Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi
Daga Sani Sulaiman
Gwamnan Jihar Taraba, Dr. Agbu Kefas, ya yi jimami kan rasuwar fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, wanda ya rasu a ranar Alhamis 27 ga watan Nuwamban 2025, yana da shekaru 102.
Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai bai wa gwamnan shawara na musamman kan Yada Labarai da Hulda da Jama’a, Mista Emmanuel Bello, ya sanyawa hannu.
Gwamnan ya ce rasuwar wannan babban malami babban rashi ne ga kasa, yana mai nuna cewa a wannan lokaci ne ake matuƙar bukatar irin gudummawar da yake bayarwa, duba da kalubalen da kasar ke fusfuskanta.
Ya kara da cewa marigayi Sheikh ya koyar da ilimi da zai ci gaba da jagorantar kasa kan batun zaman lafiya tsakanin addinai.
Haka kuma, Dr. Kefas ya yabawa halayen Sheikh Bauchi, wanda ya bayyana shi a matsayin mutum mai tawali’u, jin kai, da haƙuri.
Saboda haka, Gwamna Agbu Kefas ya yi kira ga jama’a da su yi koyi da jagorancin wannan fitaccen malami.
Ya ce al’ummar kasa za su ci gaba da bin tsarin ladabi da tarbiyyar da marigayi Sheikh Dahiru Usman Bauchi ya koyar.
A wani bangaren, Dr. Kefas ya ja hankalin ‘yan Najeriya da su ci gaba da kasancewa cikin zaman lafiya da juna ba tare da la’akari da addininsu ba.
Ya jaddada muhimmancin jurewa da girmama ra’ayin juna maimakon nacewa a kan namu ra’ayin, tare da tabbatar da aniyarsa ta ci gaba da hidima ga dukkan ‘yan Jihar Taraba bisa adalci ba tare da la’akari da addini ko kabilarsu ba.