Aminiya:
2025-05-15@20:09:23 GMT

Hauhawar farashi ya ragu zuwa kashi 23.71 — NBS

Published: 15th, May 2025 GMT

Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS), ta bayyana cewa hauhawar farashi a Najeriya ya sauka kaɗan a watan Afrilu 2025 zuwa kashi 23.71, daga kashi 24.23 da aka samu a watan Maris.

Wannan na nuna cewa hauhawar farashi ya ragu idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata, inda a watan Afrilun 2024 aka samu kashi 33.

69.

Sabon Hari: An kashe makiyayi da shanu sama da 100 a Filato Wuta ta kashe ɓarawon wayar lantarki a Jigawa

Wannan ragi da aka samu a watan Afrilu ya kai kusan kashi 10.

Har ila yau, hukumar ta ce hauhawar farashi daga wata zuwa wata ya ragu a watan Afrilu, inda aka samu kashi 1.86, ƙasa da kashi 3.90 da aka samu a watan Maris.

Wannan na nuna cewar hauhawar farashin kaya bai yi tsada da yawa ba a watan Afrilu idan aka kwatanta da watan Maris.

Farashin kayan abinci, wanda yafi shafar rayuwar yau da kullum, ya tsaya a kashi 21.26 a watan Afrilu, idan aka kwatanta da kashi 40.53 a bara.

Wannan ragin ya faru ne sakamakon sauyin yadda ake ƙididdigar bayanai.

A matakin wata-wata, hauhawar farashin kayan abinci ya kasance kashi 2.06 a watan Afrilu, wanda ya ragu daga kashi 2.18 da aka samu a watan Maris.

Ragi farashin wasu kayayyaki kamar garin masara, hatsi, kuɓewa busasshiya, garin doya, wake, da shinkafa ya taimaka wajen samun wannan sauƙi.

A tsaka-tsaki kuwa, hauhawar farashin abinci a cikin shekara guda zuwa watan Afrilu 2025 ya tsaya a kashi 31.43, wanda ya ragu da kashi 1.31 idan aka kwatanta da shekara da ta gabata wanda yake a kashi 32.74.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hauhawar Farashi Kayan abinci Kayan Masarufi Kayayyaki idan aka kwatanta da da aka samu a watan hauhawar farashi a watan Afrilu a watan Maris

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025

Majalisar wakilai za ta binciki yadda aka samu mummunar faduwa a jarabawar shiga makarantun gaba da sakandire (UTME) ta 2025 da hukumar shirya jarabawar (JAMB) ta gudanar kwanan nan. Hakan ya biyo bayan amincewa da kudirin da dan majalisa, Adewale Adebayo ya gabatar a zauren majalisar a ranar Alhamis. Da yake gabatar da kudirin, ya koka da cewa, da yawa daga cikin daliban, sun yi tafiya mai nisa domin zana jarabawar UTME a cibiyoyin jarabawar. Amma abin takaici, sai ga sakamakon ya fito da koma baya da yawa. Duk da cewa, hukumar JAMB ta amince cewa, tangardar na’ura ce ta janyo faduwar amma akwai bukatar a binciki hukumar. Idan za a iya tunawa, sakamakon jarabawar UTME na 2025 da JAMB ta fitar a ranar 9 ga watan Mayu ya nuna cewa sama da kashi 70 cikin 100 na masu zana jarabawar sun samu kasa da maki 200 daga cikin mafi girman maki 400 da ake iya samu. Sai dai, shugaban hukumar JAMB, ya bayyana tangardar na’ura a matsayin silar faduwar a yayin wani taron manema labarai a Abuja ranar Laraba, inda ya ce hukumar ta gudanar da bincike, inda ta gano matsalar ta shafi sakamakon masu zana jarabawar  su 379,997.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025
  • An kama wata mata kan zargin safarar makamai zuwa Katsina
  • Rasha Ta Ce Putin Ba Zai Halarci Tattaunawar Zaman Lafiya A Istanbul Ba
  • Kashi Na Biyu Na Maniyyata 415 Daga Jihar Kwara Sun Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
  • Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
  • Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Buƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
  • Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe
  • ‘Duk da hauhawar farashi tattalin arzikin Nijeriya ya haɓaka’
  •  An Bude  Taron Karawa Juna Sani Akan Makamashin Nukiliyar Iran Karo Na 31 A birnin Mashhad