Aminiya:
2025-06-30@06:18:53 GMT

Hauhawar farashi ya ragu zuwa kashi 23.71 — NBS

Published: 15th, May 2025 GMT

Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS), ta bayyana cewa hauhawar farashi a Najeriya ya sauka kaɗan a watan Afrilu 2025 zuwa kashi 23.71, daga kashi 24.23 da aka samu a watan Maris.

Wannan na nuna cewa hauhawar farashi ya ragu idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata, inda a watan Afrilun 2024 aka samu kashi 33.

69.

Sabon Hari: An kashe makiyayi da shanu sama da 100 a Filato Wuta ta kashe ɓarawon wayar lantarki a Jigawa

Wannan ragi da aka samu a watan Afrilu ya kai kusan kashi 10.

Har ila yau, hukumar ta ce hauhawar farashi daga wata zuwa wata ya ragu a watan Afrilu, inda aka samu kashi 1.86, ƙasa da kashi 3.90 da aka samu a watan Maris.

Wannan na nuna cewar hauhawar farashin kaya bai yi tsada da yawa ba a watan Afrilu idan aka kwatanta da watan Maris.

Farashin kayan abinci, wanda yafi shafar rayuwar yau da kullum, ya tsaya a kashi 21.26 a watan Afrilu, idan aka kwatanta da kashi 40.53 a bara.

Wannan ragin ya faru ne sakamakon sauyin yadda ake ƙididdigar bayanai.

A matakin wata-wata, hauhawar farashin kayan abinci ya kasance kashi 2.06 a watan Afrilu, wanda ya ragu daga kashi 2.18 da aka samu a watan Maris.

Ragi farashin wasu kayayyaki kamar garin masara, hatsi, kuɓewa busasshiya, garin doya, wake, da shinkafa ya taimaka wajen samun wannan sauƙi.

A tsaka-tsaki kuwa, hauhawar farashin abinci a cikin shekara guda zuwa watan Afrilu 2025 ya tsaya a kashi 31.43, wanda ya ragu da kashi 1.31 idan aka kwatanta da shekara da ta gabata wanda yake a kashi 32.74.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hauhawar Farashi Kayan abinci Kayan Masarufi Kayayyaki idan aka kwatanta da da aka samu a watan hauhawar farashi a watan Afrilu a watan Maris

এছাড়াও পড়ুন:

Bom ya kashe mutum hudu da raunata 21 a Yobe

A ranar Juma’ar nan ne wasu abubuwa da ake kyautata zaton bom ne ya kashe mutane huɗu tare da raunata wasu 21 a hanyar Katarko zuwa Goniri a Ƙaramar hukumar Gujba a Jihar Yobe.

Kamar yadda rahoton ke nunawa, waɗanda lamarin ya rutsa da su, galibi ’yan ƙabilar Gotala ne, suna kan hanyarsu ta zuwa babbar kasuwar Buni yadi ne a lokacin da motarsu ta taka wani abin fashewa da ake zargin bam ne.

Tirela ta afka cikin kasuwa ta kashe mutum da raunata 5 a Taraba Ƙudan zuma ya tarwatsa ɗaliban da ke jarrabawar NECO

A rahoton da ya fito daga babban asibitin ƙwararru na Damaturu ya nuna cewa an kai gawarwakin mutane huɗu da suka mutu a fashewar bam ɗin zuwa gida domin yi musu jana’iza yayin da sauran ke jinya a asibitin ƙwararru da kuma asibitin koyarwa na Jami’ar Yobe da ke Damaturu.

Al’ummar Gotala dai na can ne a bakin dajin Sambisa inda ’yan ta’addan da ake kyautata zaton ’yan Boko Haram ne suka shafe shekaru suna gudanar da ayyukansu.

Wata majiya da ba a tabbatar da ita ba ta shaida wa wakilinmu cewa, ‘yan banga da motocin soji ma sun bi ta kan wannan hanya jiya ba tare da wani abu ya faru ba.

Har zuwa lokacin cika wannan rahoto, rundunar sojin ba ta fitar da wata sanarwa ba.

‘Yan uwan waɗanda abin ya shafa da aka zanta da su a asibitoci sun yi kira ga gwamnatin Jihar Yobe da ta gaggauta sake gina hanyar da ta lalace domin daƙile ayyukan ’yan tada ƙayar baya da ke addabar al’umma.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu
  • Babu wanda zai manta da gudunmawar da Wike ya ba ni — Fubara
  • Van Nistelrooy ya ajiye aikin horas da Leicester City
  • Faransa Tace Za’a Maida Takunkuman Tattalin Arziki Kan Kasar Iran Idan Taki Yarda Da Yarjeniyar da Trump Yake
  • Monaco ta dauki Paul Pogba
  •   Ka’a’ni: Nasarar Da Mu Ka Samu Za Ta Ci Gaba Da Dorewa
  • Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi
  •  Arakci:  Idan Aka Kai Iran Bango Za Ta Fito Da Hakikanin Karfin Da Take Da Shi
  • Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko
  • Bom ya kashe mutum hudu da raunata 21 a Yobe