Fiye Da Falasdinawa 80 Ne Su Ka Yi Shahada Daga Safiyar Yau Alhamis
Published: 15th, May 2025 GMT
Tashar talabijin din almayadin ta watsa labarin dake cewa, daga safiyar yau Alhamis zuwa yanzu, adadin Falasdinawan da su ka yi shahada sun haura 40,mafi yawancinsu daga yankin Khan-Yunus.
Tun da safiyar yau Alhamis ne dai sojojin HKI su ka fara kai hare-hare a yankuna mabanbanta na Gaza da su ka hada da Khan-Yunus.
Adadin wadanda aka tabbatar da sun yi shahada ya zuwa yanzu sun haura 40.
Sai dai wasu rahotannin da suke fitowa daga Gaza din sun ce, adadin shahidan ya karu zuwa 82.
Jiragen HKI suna kai wa yankin na Gaza hare-hare daga kduancinsa zuwa arewacinsa cikin hauka.
A Khan-Yunus ‘yan Sahayoniyar sun kai hari akan wasu gidaje 8 da mutane suke ciki, da ya yi sanadiyyar shahadar mutane 30 daga cikinsu har da kananan yara. Rahotannin da suke fitowa daga yankin sun ce an kai wasu kananan yara zuwa asibitin “Nasir” domin yi musu magani daga raunukan da su ka samu.
Wasu garuruwan da jiragen yakin HKI su ka kai wa hare-hare sun hada da “Khaza’a, Abisan alkabhirah, sai yankin Sanadhi’ da kuma kusa da sha-tale-talen Sadhra.
Sojojin mamayar HKI sun kuma kai wasu hare-haren akan sansanin ‘yan hijirar Falasdinawa a yankin Mawasi da yankin Abu Haddaf da garin alqararah.
A arewacin Gaza, sojojin HKI sun kai wasu hare-haren a kan wani gida na iyalan Shihab a garin Jabaliyah, da ya yi sanadiyyar shahadar mutane 7 da kuma jikkata wasu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda ISWAP ta kashe sojoji ta kwashe makamai a sansanin soji a Borno
Mayaƙan Boko Haram sun kashe sojoji da ba a san adadinsu ba tare da yin awon gaba da wasu da dama bayan wani ƙazamin hari da suka kai a sansanin soji da ke yankin Marte a Jihar Borno.
Majiyoyin soji sun ce mayaƙan ƙungiyar sun fi karfin sojojin, inda suka kwashi makamai masu tarin yawa sa’annan suka cinna wa ma’ajiyar makamai da ke sansanin sojin wuta.
Mazauna yankin sun bayyana cewa da misalin ƙarfe 3 na asuba, kafin wayewar garin ranar Asabar ne Boko Haram ta ƙaddamar da harin.
Wani soja da ya nemi a ɓoye sunansa ya ce, “ISWAP ta ƙwace Marte, an kashe sojoji da dama, an kama wasu, amma wasu sun samu sun tsere zuwa Dikwa, inda runduna ta 24 take.
Ya kashe abokinsa saboda hula a Kano NAJERIYA A YAU: Matsalar lantarki: ’Yan Najeriya sun yi tir da biyan diyya ga ’yan Band A“’Yan ta’addan sun ƙona tankokin yaƙi kuma sun kwashi makamai daga sansanin sojin,” in ji shi.
Wani mazaunin Marte, gari mai nisan kilomita 38 daga Dikwa, hedikwatar Ƙaramar Hukumar Dikwa, ya ce sun ji karar harbe-harben kuma daga bisani suka ga jirgin soji yana shawagi.
Ya ce, “mun samu labarin cewa an tura ƙarin jami’an tsaro kuma an ƙwato sansanin sojin, amma ’yan ta’addan sun sun sace makamai kuma sun koma motoci da rumbun makaman sojin da ke wurin.”
Ya ci gaba da cewa, “abin takaici mayaƙan sun tsare mata da ƙananan yara da dama a Sabon Marte, amma wasu da dama sun samu tserewa zuwa Dikwa domin tseratar da rayuwarsu.
“Ba a daɗe ba da ’yan ƙungiyar suka kai hari a Malam Fatori, inda suka kashe sojoji 21 da wani daga cikin kwamdojinmu.”
Daga watan Janairu zuwa yanzu an kai wa sansanonin soji da dama hare-hare a yankin Tafkin Chadi da kuma Dutsen Mandara da ke Dajin Sambisa a jihohin Borno da Yobe.