Fiye Da Falasdinawa 80 Ne Su Ka Yi Shahada Daga Safiyar Yau Alhamis
Published: 15th, May 2025 GMT
Tashar talabijin din almayadin ta watsa labarin dake cewa, daga safiyar yau Alhamis zuwa yanzu, adadin Falasdinawan da su ka yi shahada sun haura 40,mafi yawancinsu daga yankin Khan-Yunus.
Tun da safiyar yau Alhamis ne dai sojojin HKI su ka fara kai hare-hare a yankuna mabanbanta na Gaza da su ka hada da Khan-Yunus.
Adadin wadanda aka tabbatar da sun yi shahada ya zuwa yanzu sun haura 40.
Sai dai wasu rahotannin da suke fitowa daga Gaza din sun ce, adadin shahidan ya karu zuwa 82.
Jiragen HKI suna kai wa yankin na Gaza hare-hare daga kduancinsa zuwa arewacinsa cikin hauka.
A Khan-Yunus ‘yan Sahayoniyar sun kai hari akan wasu gidaje 8 da mutane suke ciki, da ya yi sanadiyyar shahadar mutane 30 daga cikinsu har da kananan yara. Rahotannin da suke fitowa daga yankin sun ce an kai wasu kananan yara zuwa asibitin “Nasir” domin yi musu magani daga raunukan da su ka samu.
Wasu garuruwan da jiragen yakin HKI su ka kai wa hare-hare sun hada da “Khaza’a, Abisan alkabhirah, sai yankin Sanadhi’ da kuma kusa da sha-tale-talen Sadhra.
Sojojin mamayar HKI sun kuma kai wasu hare-haren akan sansanin ‘yan hijirar Falasdinawa a yankin Mawasi da yankin Abu Haddaf da garin alqararah.
A arewacin Gaza, sojojin HKI sun kai wasu hare-haren a kan wani gida na iyalan Shihab a garin Jabaliyah, da ya yi sanadiyyar shahadar mutane 7 da kuma jikkata wasu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Yemen Ta Gargadi Isra’ila Kan Fuskantar Hare-Hare Idan Ta Karya Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta
Kasar Yemen ta gargadi gwamnatin mamayar Isra’ila kan fuskantar hare-hare masu zafi idan har ta karya yarjejeniyar Gaza
A ranar Lahadin da ta gabata, Hazam al-Assad, mamba a ofishin siyasa na kungiyar Ansarullahi ta Yemen, ya gargadi gwamnatin mamayar Isra’ila kan karin fuskantar hare-hare masu zafi idan ta karya yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Gaza.
A wata sanarwa da ya fitar ta hanyar gidan radiyo Sputnik ta kasar Rasha, Hazam al-Assad ya tabbatar da cewa: Yemen za ta dakatar da kai hare-hare kan gwamnatin mamayar Isra’ila, idan har ta yi aiki da yarjejeniyar tsagaita bude wuta a zirin Gaza.
Tun da farko dai shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da cewa: Gwamnatin mamayar Isra’ila da kungiyar Hamas sun rattaba hannu kan matakin farko na shirinsa na zaman lafiya.
A nata bangaren, Kungiyar Hamas ta sanar da yarjejeniyar tsagaita wuta a zirin Gaza, wadda ta hada da shigar da kayan agaji da musayar fursunoni. Ta yi kira ga shugaban kasar Amurka Donald Trump da kasashen da suka amince da yarjejeniyar, da kuma kasashen Larabawa, da na Musulunci, da na kasa da kasa, da su tilastawa haramtacciyar kasar Isra’ila aiwatar da yarjejeniyar gaba daya.
A yau litinin ne za a gudanar da shawarwarin a Sharm el-Sheikh a birnin Alkahira, tare da halartar shugaban Amurka Donald Trump da kasashe masu shiga tsakani, domin kafa dukkanin sharuddan da suka dace domin samun nasara da kuma ci gaba da aiwatar da shirin, wanda bangarorin Falasdinu da gwamnatin mamayar Isra’ila suka amince da shi.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Cibiyar Lafiya Ta Nasser Ta Ce: Yaran Gaza 5,500 Suna Bukatar Agajin Gaggawa A Kasashen Waje October 13, 2025 Shugaban Amurka Ya Yi Barazanar Aikewa Ukraine Makamai Masu Linzami Kirar Tomahawk October 13, 2025 Trump, da Al’Sisi za su jagoranci taron zaman lafiya kan Gaza October 12, 2025 ‘Yan Kamaru na kada kuri’a a zaben shugaban kasar October 12, 2025 Wata Kotu a Faransa ta yi watsi da rufe wata makarantar musulmi a birnin Nice October 12, 2025 Gwamnatin Cuba ta yi watsi da zargin da Amurka ke yi na hannu a yakin Ukraine October 12, 2025 Arachi: HKI Ba Abar Amincewa Ba Ce, Falasdinawa Su Yi Hattara October 12, 2025 Iran Ta Yi Allawadai Da HKI Kan Hare-Haren Da Take Kaiwa Kudancin Lebanon October 12, 2025 An Gudanar Da Taron ‘Farkawar Musulmi’ A Nan Tahren Inda Aka Tattauna Batun Falasdinu October 12, 2025 Amurka Da Masar Ne Zasu Jagoranci Taron Rattaba Hannu Tsakanin HKI Da Falasdin A Sharm Sheikh October 12, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci