Fiye Da Falasdinawa 80 Ne Su Ka Yi Shahada Daga Safiyar Yau Alhamis
Published: 15th, May 2025 GMT
Tashar talabijin din almayadin ta watsa labarin dake cewa, daga safiyar yau Alhamis zuwa yanzu, adadin Falasdinawan da su ka yi shahada sun haura 40,mafi yawancinsu daga yankin Khan-Yunus.
Tun da safiyar yau Alhamis ne dai sojojin HKI su ka fara kai hare-hare a yankuna mabanbanta na Gaza da su ka hada da Khan-Yunus.
Adadin wadanda aka tabbatar da sun yi shahada ya zuwa yanzu sun haura 40.
Sai dai wasu rahotannin da suke fitowa daga Gaza din sun ce, adadin shahidan ya karu zuwa 82.
Jiragen HKI suna kai wa yankin na Gaza hare-hare daga kduancinsa zuwa arewacinsa cikin hauka.
A Khan-Yunus ‘yan Sahayoniyar sun kai hari akan wasu gidaje 8 da mutane suke ciki, da ya yi sanadiyyar shahadar mutane 30 daga cikinsu har da kananan yara. Rahotannin da suke fitowa daga yankin sun ce an kai wasu kananan yara zuwa asibitin “Nasir” domin yi musu magani daga raunukan da su ka samu.
Wasu garuruwan da jiragen yakin HKI su ka kai wa hare-hare sun hada da “Khaza’a, Abisan alkabhirah, sai yankin Sanadhi’ da kuma kusa da sha-tale-talen Sadhra.
Sojojin mamayar HKI sun kuma kai wasu hare-haren akan sansanin ‘yan hijirar Falasdinawa a yankin Mawasi da yankin Abu Haddaf da garin alqararah.
A arewacin Gaza, sojojin HKI sun kai wasu hare-haren a kan wani gida na iyalan Shihab a garin Jabaliyah, da ya yi sanadiyyar shahadar mutane 7 da kuma jikkata wasu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Falasdinu: Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kai Hare-hare A Yammacin Kogin Jordan
Sojojin mamayar HKI suna ci gaba da kai hare-hare a yammacin kogin Jordan, inda a safiyar yau lahadi su ka kutsa cikin wani gida a garin Jenin,kamar kuma yadda ‘yan share wuri zauna su ka kutsa gidan wani bafalasdine a kudancin Nablus.
Rahotanni da suke fitowa daga Falasdinu suna cewa; an yi taho mu gama a tsakanin Falasdinawa da ‘yan mamaya a garin Tal a kudancin Nablus.
A sansanin ‘yan hijira na Jenin sojojin na mamaya sun tarwatsa wani gida na Bafalasdine wanda ya haddasa tashin hayaki da kuma jin kara mai tsanani a sassa mabanbanta na garin Jenin.
Haka nan kuma ‘yan mamayar sun yi amfani da motar Buldoza wajen rusa wasu gidaje a sansanin na Jenin.
A makon da ya shude ma dai ‘yan mamayar sun rusa wasu gidaje masu yawa na Falasdinawa a yammacin Kogin Jordan a karkashin shirinsu na rusa gidaje 95.
A garin Tubas da yake a wannan yankin Iyalai da dama sun yi hijira saboda kaucewa hare-haren da ‘yan share wuri zauna suke kai musu.
Tun bayan 7 ga watan Oktoba na 2023 Amurka take goyon bayan HKI a yi wa Falasdinawan Gaza, kisan kiyashi da kuma kwacewa Falasdinawan yammacin Kogin Jordan gidajensu da zummar korarsu daga yankin.