Fiye Da Falasdinawa 80 Ne Su Ka Yi Shahada Daga Safiyar Yau Alhamis
Published: 15th, May 2025 GMT
Tashar talabijin din almayadin ta watsa labarin dake cewa, daga safiyar yau Alhamis zuwa yanzu, adadin Falasdinawan da su ka yi shahada sun haura 40,mafi yawancinsu daga yankin Khan-Yunus.
Tun da safiyar yau Alhamis ne dai sojojin HKI su ka fara kai hare-hare a yankuna mabanbanta na Gaza da su ka hada da Khan-Yunus.
Adadin wadanda aka tabbatar da sun yi shahada ya zuwa yanzu sun haura 40.
Sai dai wasu rahotannin da suke fitowa daga Gaza din sun ce, adadin shahidan ya karu zuwa 82.
Jiragen HKI suna kai wa yankin na Gaza hare-hare daga kduancinsa zuwa arewacinsa cikin hauka.
A Khan-Yunus ‘yan Sahayoniyar sun kai hari akan wasu gidaje 8 da mutane suke ciki, da ya yi sanadiyyar shahadar mutane 30 daga cikinsu har da kananan yara. Rahotannin da suke fitowa daga yankin sun ce an kai wasu kananan yara zuwa asibitin “Nasir” domin yi musu magani daga raunukan da su ka samu.
Wasu garuruwan da jiragen yakin HKI su ka kai wa hare-hare sun hada da “Khaza’a, Abisan alkabhirah, sai yankin Sanadhi’ da kuma kusa da sha-tale-talen Sadhra.
Sojojin mamayar HKI sun kuma kai wasu hare-haren akan sansanin ‘yan hijirar Falasdinawa a yankin Mawasi da yankin Abu Haddaf da garin alqararah.
A arewacin Gaza, sojojin HKI sun kai wasu hare-haren a kan wani gida na iyalan Shihab a garin Jabaliyah, da ya yi sanadiyyar shahadar mutane 7 da kuma jikkata wasu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Isra’ila ta hana ayarin motocin agaji na arewacin Afrika shiga Gaza
Ministan yakin Isra’ila, Israel Katz, ya umarci sojojin kasar da su hana ayarin motocin agaji na arewacin Afirka shiga yankin Zirin Gaza da aka yi wa kawanya.
A cikin wata sanarwa ofishin Katz ya umarci sojojin Isra’ila da su hana “masu fafatuka daga Masar shiga yankin Zirin Gaza.
Katz bukaci “Hukumomin Masar dasu hana zuwan masu fafatukar a kan iyakar Masar da Isra’ila.”
Ministan ya ya bayyana hakan a matsayin hadari ga jami’an tsaron Isra’ila na IDF.”
Wannan dai na zuwa ne bayan ayarin motoci 100 da ya kunshi dubban masu fafatuka daga kasashen Morocco, Aljeriya, Tunisia, Libya da Masar, suka yunkuri anniyar wayar da kan al’ummar duniya kan matsalar jin kai a Gaza, da neman kawo karshen yakin kisan kare dangi, da karya shingen da Isra’ila ke yi da kuma kai muhimman kayayyakin jin kai a Gaza.
Ayarin da ya kunshi kungiyoyin kwadago da masu fafutukar kare hakkin bil’adama da ‘yan wasa da lauyoyi da likitoci da ‘yan jarida da na kungiyoyin matasa da dai sauransu ana sa ran za su shiga Masar a yau Alhamis kafin isa mashigar Rafah da ke kan iyaka a kudancin zirin Gaza.
Kafin hakan dama sojojin Isra’ila sun kwace jirgin ruwan agaji na Madleen da ke kan hanyarsa ta zuwa Gaza domin kai tallafi ga al’ummar Zirin, bayan shafe sama da watanni ashirin na yakin kisan kare dangi da Isra’ila ke yi.
An kama dukkan masu fafutukar na kasa da kasa su 12 da ke cikin jirgin, ciki har da mai fafutukar Sweden Greta Thunberg.