Kashi Na Biyu Na Maniyyata 415 Daga Jihar Kwara Sun Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
Published: 15th, May 2025 GMT
Kashi na biyu na maniyyata 415 daga jihar Kwara sun tashi zuwa kasar Saudiyya domin gudanar da aikin hajjin shekarar 2025.
Da yake jawabi ga maniyyatan jihar kafin tafiyarsu, Amirul-Hajj na Jiha, Olupo na Ajase-Ipo, Oba Ismail Yahaya- Alebiosu ya shawarce su da su kasance jakadu nagari na jihar yayin da suke kasar Saudiyya.
Oba Yahaya- Alebiosu ya ce gwamnatin jihar ta samar da matakai daban-daban don tabbatar da annashuwa da kare lafiyar alhazai a tafiyar da suke yi a kasa mai tsarki.
Mai baiwa gwamnan jihar Kwara shawara ta musamman kan harkokin addini, Alhaji Ibrahim Dan-Maigoro ya jagoranci tawagar maniyyata guda 415 zuwa kasar Saudiyya.
An dauke Mahajjatan ne a jirgin Max Airline daga filin jirgin sama na Babatunde Idi-Agbon dake Ilorin.
Ya zuwa yanzu dai an jigilar alhazai 975 daga jihar Kwara zuwa kasar Saudiyya.
COV/ALI MUHAMMAD RABIU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kwara zuwa kasar Saudiyya jihar Kwara
এছাড়াও পড়ুন:
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa
Rivers Angels ta lashe gasar cin Kofin Shugaban ƙasa na shekarar 2025 bayan ta doke Nasarawa Amazons da ci 4-2 a bugun fenareti bayan da suka tashi 2-2 a filin wasa na Mobolaji Johnson dake birnin Legas, wannan ne karo na goma da ɓangaren Tosan Blackson ke lashe kofin.
Nasarawa Amazons ce ta jagoranci wasan a farko da ci 2-0 waɗanda Olusola Shobowale ta ci, Olusola ta zura ƙwallon farko a minti na 7 da fara wasan sai kuma ta zura ta biyu a minti na 10, bayan dawowa daga hutun rabin lokaci ne Rivers ta zage damtse, wanda ya kai ta ga farke duka ƙwallaye biyu a cikin mintuna 5 kacal.
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana KishiyaTaiwo Ajibade ce ta ci wa Rivers duka kwallayenta biyu a cikin mintuna 5 da dawowa daga hutun rabin lokaci, hakan ya sa wasan ya kare da ci 2-2 wanda kuma ya sa aka tafi zuwa bugun daga kai sai mai tsaron raga domin fitar da zakaran wasan, kugiyar ta Port Harcourt ya yi nasara a bugun daga kai sai mai tsaron gida bayan ta jefa kwallo 4 yayinda Amazons suka jefa kwallaye 2.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp