Kashi Na Biyu Na Maniyyata 415 Daga Jihar Kwara Sun Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
Published: 15th, May 2025 GMT
Kashi na biyu na maniyyata 415 daga jihar Kwara sun tashi zuwa kasar Saudiyya domin gudanar da aikin hajjin shekarar 2025.
Da yake jawabi ga maniyyatan jihar kafin tafiyarsu, Amirul-Hajj na Jiha, Olupo na Ajase-Ipo, Oba Ismail Yahaya- Alebiosu ya shawarce su da su kasance jakadu nagari na jihar yayin da suke kasar Saudiyya.
Oba Yahaya- Alebiosu ya ce gwamnatin jihar ta samar da matakai daban-daban don tabbatar da annashuwa da kare lafiyar alhazai a tafiyar da suke yi a kasa mai tsarki.
Mai baiwa gwamnan jihar Kwara shawara ta musamman kan harkokin addini, Alhaji Ibrahim Dan-Maigoro ya jagoranci tawagar maniyyata guda 415 zuwa kasar Saudiyya.
An dauke Mahajjatan ne a jirgin Max Airline daga filin jirgin sama na Babatunde Idi-Agbon dake Ilorin.
Ya zuwa yanzu dai an jigilar alhazai 975 daga jihar Kwara zuwa kasar Saudiyya.
COV/ALI MUHAMMAD RABIU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kwara zuwa kasar Saudiyya jihar Kwara
এছাড়াও পড়ুন:
An Kaddamar da Shirin Karfafa Matasa Don Noman Kasuwanci A Kwara
Gwamnatin jihar Kwara ta ce ta kammala shirye-shiryen kaddamar da wani shiri na sana’ar kiwon dabbobi da ya maida hankali kan matasa, wanda aka tsara domin horarwa da samar da kayan aiki da kuma samar da kudade ga masu son noma a fadin jihar.
Kwamishiniyar Raya Dabbobi ta jihar, Misis Oloruntoyosi Thomas ta bayyana haka a lokacin da ta ziyarci sansanin wayar da kan matasa masu yi wa kasa hidima (NYSC) da ke Yikpata, karamar hukumar Edu ta jihar.
Ta ce shirin wani bangare ne na kokarin da Gwamnatin Jihar ke yi na mayar da jihar ta zama wata matattarar kirkire-kirkire da kuma dabbobi.
Kwamishinan ya bayyana cewa, ma’aikatar ta hada kai da hukumar NYSC domin samar da sansanin a matsayin filin horas da ‘yan kungiyar da sauran matasa masu sha’awar noman kiwo.
Mrs Thomas ta ce hangen nesan a fili yake wajen sauya matasa daga masu neman aikin yi zuwa masu samar da ayyukan yi a wuraren kiwo.
“Wannan haɗin gwiwar da NYSC za ta ba mu damar ba da horo kan aikin kiwon dabbobi, bunƙasa kasuwanci da samun kuɗin shiga, duk a cikin tsari.
Kwamishinan ya bayyana cewa shirin zai fara a watanni hudu na karshen shekarar 2025, za a gudanar da shi ta hanyar hadin gwiwar jama’a da masu zaman kansu, wanda gwamnatin jihar ta riga ta samu.
Ta lura cewa mahalartan za su sami horo na tsawon watanni uku bayan haka za su sami jarin farawa da tallafin shigar da su don ƙaddamarwa ko haɓaka ayyukansu.
A nasa bangaren, kodinetan NYSC na jihar, Mista Onifade Joshua, ya bayyana cewa sansanin yana da kyau da ya dace don biyan bukatun shirin.
Ya bukaci gwamnatin jihar da ta ba da fifiko ga tsaro a kewayen wurin. END
COV/ALI MUHAMMAD RABIU