Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Published: 15th, May 2025 GMT
Idris ya jaddada cewa Gwamnatin Tinubu tana da ƙudirin kare ’yancin faɗin albarkacin baki da ’yancin kafafen yaɗa labarai, waɗanda ya ce su ne ginshiƙan dimokiraɗiyya a ƙasar nan.
Ya ce: “Na bayyana ra’ayi na ga Jakaden, kuma na kuma jaddada ƙudirin gwamnati na ci gaba da kare ’yancin faɗin albarkacin baki da kuma rashin takura wa ‘yan jarida wajen gudanar da aikin su.
“Muna ganin aikin jarida da kafafen yaɗa labarai wani muhimmin ɓangare ne na dimokiraɗiyya.
“Babu wata dimokiraɗiyya da za ta yi nasara ba tare da kafafen yaɗa labarai ba.”
Sai dai kuma ministan ya buƙaci ‘yan jarida da su riƙa amfani da ‘yancin da suka samu cikin ƙwarewa da nuna kishin ƙasa.
Ya ce: “Muna kuma amfani da wannan dama wajen ƙarfafa gwiwar ‘yan jarida a Nijeriya cewa yayin da suke amfani da ’yancin kafafen yaɗa labarai, su tabbata suna ɗaukar nauyin aikin da muhimmanci.
“Su ci gaba da kasancewa masu sanin hakki, kuma a gaskiya sun kasance, amma muna buƙatar su ƙara jajircewa wajen yaɗa sahihan labarai da nuna kishin ƙasa, domin hakan ne kaɗai zai tabbatar da ɗorewar dimokiraɗiyyar.”
Ministan ya tabbatar da ci gaba da inganta wayar da kan jama’a kan kafafen yaɗa labarai da bayanai domin daƙile yaɗuwar labaran ƙarya.
A nasa ɓangaren, Jakaden Amurka, Mista Mills, ya ce ganawar sa da ministan ta kasance mai amfani matuƙa, musamman dangane da ’yancin kafafen yaɗa labarai da kuma sake duba Dokar Laifukan Intanet.
Ya ce: “Na yi wata muhimmiyar ganawa da Minista dangane da ’yancin kafafen yaɗa labarai a Nijeriya da kuma ƙudirin sa na kare wannan dama da ke bai wa mutane damar faɗin albarkacin bakin su.
“Na yaba da jawabin da ya fitar a ranar 3 ga Mayu, wato ranar ’Yancin Kafafen Yaɗa Labarai ta Duniya, inda ya jaddada ƙudirin gwamnatin sa na kare wannan ’yanci.
“Mun kuma tattauna batun sake fasalin Dokar Laifukan Intanet da kuma yadda na buƙaci cewa Ma’aikatar Yaɗa Labarai ta taka muhimmiyar rawa a cikin wannan sauyi a Majalisar Dokoki.”
Wannan shi ne karo na biyu da Jakaden Amurkan ya gana da Ministan kan batutuwan da suka shafi ’yancin kafafen yaɗa labarai a Nijeriya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: yancin kafafen yaɗa labarai
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu ya rattaba hannu kan sababbin dokokin haraji
Daga ƙarshe dai Shugaban Kasa Bola Tinubu ya sa hannu kan sababbin dokokin haraji guda hudu da a baya suka jawo cece-kuce da zazzafar muhawara a faɗin Najeriya.
An dai sanya hannun ne a fadar shugaban kasa ta Aso Rock da ke Abuja ranar Alhamis, inda shugaban ya ce dokokin za su bunkasa harkokin hada-hadar kudade da tattara haraji a kasar.
NAJERIYA A YAU: Ko Wadanne Dalilai Ne Ke Hana Mata A Arewa Koyon Ilimin Kimiyya? Sheikh Dahiru Bauchi ya cika shekara 101 a duniyaA kwanan nan ne dai Majalisar Dokoki ta Ƙasa ta amince da kudurorin su zama doka bayan tafka zazzafar muhawara a zaurukan majalisun guda biyu.
Daga cikin waɗanda suka halarci bikin saka hannun akwai Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio da Kakakin Majalisar Wakilai, Tajuddeen Abbas da shugabannin masu rinjaye na majalisun biyu da kuma shugabannin kwamitocin kudi na majalisun.
A ranar Laraba ce dai mai magana da yawun shugaba Tinubu, Bayo Onanuga, ya sanar da cewa da zarar sun fara aiki, kudurorin za su bunkasa hanyoyin tattara kudaden shiga a kasar.
A cewarsa, ana sa ran dokokin za su kuma karan yawan kudaden harajin da Najeriya ke samu sannan sau bunkasa harkokin kasuwanci su kuma haɓaka harkokin zuba jari daga ’yan kasuwar gida da na ƙetare.
Sai dai Hukumar Tattara Haraji ta Kasa (FIRS) ta ce dokokin ba za su fara aiki ba sai a watan Janairun 2026.
A baya dai saɗarorin dokokin da suka fi yamutsa hazo su ne na batun rarraba harajin kuɗaɗen sayen kaya na VAT da yadda za a raba shi.
Sai dai majalisar dattawa da ta wakilai ta gyara saɗarorin kafin ta amince da su tare da samun amincewar akasarin ’yan majalisar.