HausaTv:
2025-08-07@13:54:14 GMT

An Bude Kasuwar Baje Koli Na Man Fetur Da Gas Karo Na 29 A Nan Tehran

Published: 8th, May 2025 GMT

A yau ne aka bude kasuwar baje koli na kayakin da suka shafi man fetur da gasa wadanda aka kera a JMI karo na 29  a yau a nan birnin Tehran.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa kasuwar zata ci ne daga yau 8-11 ga wannan watan na mayu da muke ciki.

Labarinn ya kara da cewa kamfanoni fiye da 2000 daga ciki da kuma wasu kasashen duniya  14 ne suka halarta ta.

Baje kolin yana nuna matsayin JMI a fagen makamashi a duniya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kotu ta hana jagoran adawa Maurice Kamto takarar shugaban ƙasa a Kamaru

Kotun tsarin mulkin Kamaru ta haramta wa jagoran adawar ƙasar, Maurice Kamto tsayawa takarar shugaban ƙasa, a babban zaɓe mai zuwa na watan Oktoba, kan abin da ta bayyana rashin cika ka’idojin tsayawa takara.

Lauyansa, Hippolyte Meli Tiakouang ne ya tabbatar wa manema labarai hukuncin kotun wanda ba za a iya ƙalubalanta ba, bayan kammala zamanta na wannan Talata.

A cewarsa, kotun ta yi watsi da ƙarar da suka shigar kan matakin hukumar zaɓen ƙasar na cire shi daga cikin jerin ’yan takarar da za su fafata a zaɓen ranar 12 ga watan Oktoban bana.

Mulkin Tinubu ya fi na Buhari muni — Maina Waziri ’Yan gida ɗaya sun kitsa garkuwar ƙarya domin karɓar N5m a wurin mahaifinsu

Mista Kamto mai shekaru 71, ya yi ƙaurin suna wajen sukar gwamnatin shugaba Paul Biya, kuma shi ne ya yi na biyu a zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2018, bayan tsayawa takara a jam’iyyar MRC.

A wannan karo kuma ya nemi tsayawa takarar a jam’iyyar MANIDEM, inda ya bayyana muradin tsayawar watanni biyar da suka gabata.

Hukumar zaɓen ƙasar ta yanke hukuncin cire Kamto saboda “’yan takara masu yawa,” bayan wani ɗan takara daga wani tsagin jam’iyyar ya miƙa buƙatar makamanciyar wannan, wanda ya sa ake nuna damuwa kan halascin shugabancin jam’iyyar.

Bayan gabatar da hukuncin, Kamto wanda da alama bai ji daɗin hakan ba, ya fice daga harabar kotun ba tare da magana da ’yan jarida ba.

Hukuncin da aka yanke a ranar Talata ya ƙara tayar da fargabar hargitsi.

An jibge jami’an tsaro a kusa da cibiyar taro da ke babban birnin ƙasar, Yaoundé, inda Kwamitin Kundin Tsarin Mulki ya bayyana hukuncin, da kuma manyan titunan birnin.

A ranar da ta gabata, ’yan sanda sun harba hayaƙi mai sa hawaye tare da kama mutane da dama da suka fito zanga-zangar goyon bayan Kamto.

Lauyoyinsa waɗanda ba su yi ƙarin bayani kan mataki da za su ɗauka ba, sun ce Kamto ne zai bayyana matakin da zai ɗauka.

Masu suka na ganin cewa akwai wata maƙarƙashiya ne na kawar da ɗan siyasar daga zaɓen.

Duk da raɗe-raɗin rashin lafiya, yanzu haka shugaba Paul Biya mai shekaru 92, wanda ya shafe tsawon shekaru 43 yana mulkin Kamaru, zai sake neman wa’adi na takwas a kan karagar mulki ba tare da wata ƙwaƙƙwarar adawa ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi
  • Yadda kwacen babur da waya ya maye gurbin garkuwa da mutane a Birnin Gwari
  • An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe
  • Gwamna ya yi wa iyalan ’yan wasan Kano da suka rasu a hatsari goma ta arziki
  • Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza
  • Jihar Zamfara: ‘Yan Sanda 390 Sun Sami Karin Girma
  • Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno
  • Iran: An nada Larijani a matsayin sakataren kwamitin koli na tsaron kasa
  • Kotu ta hana jagoran adawa Maurice Kamto takarar shugaban ƙasa a Kamaru
  • Baghaei : Ziyarar Pezeshkian a Pakistan ta bude wani sabon Shafin alaka