HausaTv:
2025-06-23@05:54:51 GMT

An Bude Kasuwar Baje Koli Na Man Fetur Da Gas Karo Na 29 A Nan Tehran

Published: 8th, May 2025 GMT

A yau ne aka bude kasuwar baje koli na kayakin da suka shafi man fetur da gasa wadanda aka kera a JMI karo na 29  a yau a nan birnin Tehran.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa kasuwar zata ci ne daga yau 8-11 ga wannan watan na mayu da muke ciki.

Labarinn ya kara da cewa kamfanoni fiye da 2000 daga ciki da kuma wasu kasashen duniya  14 ne suka halarta ta.

Baje kolin yana nuna matsayin JMI a fagen makamashi a duniya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An kashe matar aure, manomi ya jikkata a wani sabon hari a Kaduna

Wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sun kai hari wasu ƙauyuka biyu da ke Ƙaramar Hukumar Kajuru a Jihar Kaduna.

A yayin harin, wata matar aure ta rasu, yayin da wani manomi ya samu rauni.

’Yan bindiga sun sace babban alƙali a Bayelsa  Dole a ɗauki mataki kan waɗanda suka kashe ’yan ɗaurin aure a Filato — Uba Sani

Harin farko ya faru ne da misalin ƙarfe 2 na daren ranar Asabar, 21 ga watan Yuni, 2025, a ƙauyen Ungwan Sarkin Hausa da ke Rimau.

Ana zargin maharan sun gudu da shanun da suka sato daga Ƙaramar Hukumar Kauru.

A lokacin harin, sun kashe wata mata mai suna Misis Alheri Danzaria.

Sun kuma sace wasu mutum biyu, amma daga baya suka sake su.

Hari na biyu ya faru ne da safiyar ranar Lahadi da misalin ƙarfe 7 a ƙauyen Kallah.

A nan ne suka harbi wani manomi mai suna Mista Iliya Barde, yayin da yake kan hanyarsa ta zuwa gona.

An garzaya da shi asibiti inda yake samun kulawar likitoci.

Shugaban gundumar Kufana, Mista Stephen Maikori, ya ce hare-haren da ake yawan kai wa sun haddasa tsoro da damuwa a tsakanin mazauna yankin.

Ya buƙaci gwamnati da ta ɗauki matakin gaggawa wajen ƙara tsaro a yankin.

Da aka tuntuɓi kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Mansir Hassan, ya ce zai bincika lamarin sannan ya bayar da amsa, amma har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto bai yi ƙarin haske ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe matar aure, manomi ya jikkata a wani sabon hari a Kaduna
  • Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra’ila?
  • Za mu sake gina kasuwar waya ta Farm Center — Abba
  • FIRS Ta Umarci A Rika Bude Ofishoshin Karbar Haraji A karshen Mako
  • CMG Ya Ja Hankulan Baki A Dandalin Tattaunawar Tattalin Arziki Na Kasa Da Kasa Na St. Petersburg Karo Na 28 
  • An kashe uban ango da ɗan uwansa a harin Filato
  • Mahara sun kashe ’yan ɗaurin aure 12 daga Zariya a Filato
  • Me Ya Kamata Mai Yaron Ciki Ta Kula Da Shi?
  • Matsayin Sin Na Bude Kofar Tattalin Arzikinta Ga Duniya Ba Zai Canza Ba
  • Katolika ta horar da shugabannin al’umma da na addini kan zaman lafiya