Har ila yau, kwamitin zai bada shawara akan hukuncin da Jam’iyar za ta dauka Idan har aka sami wanda ake zargi da laifin almundahana da kuma zagon Kasa ga LP a lokacin da yake Shugabantar jam’iyar.

 

Sanata Usman ta zargi Abure da mukarrabansa da aikata laifufuka dake janyo rabuwar Kai ga ‘ya’yan Jamiyar tare da batanci da haddasa rikici.

 

Sanata Usman ta Kara da cewa, Abure yana aikata laifufuka wanda suke kalubalantar mutunci Jam’iyar da kuma yin karo da manufofin dimokuradiyya. Don haka, majalisar zartaswa ta Jam’iyar ta dauki matakin kaddamar da bincike kan wannan munanan halayya.

 

Bugu da Kari Sanata Nenadi Usman tace majalisar zantaswa na Jamiyar Labour bayan dogon nazari akan hukuncin da kotun koli ta Kasa ta yi na ranar 4 ga watan Afrilun 2025, Jam’iyar ta nuna matukar damuwarta akan Yadda Julius Abure yake amfani da sunan shi a matsayin Shugaban Jam’iyar bayan dakatar da shi.

 

Ta ce, abubuwan da Julius Abure yake yi ya sabawa dokar Kasa kuma ya ci mutuncin Jamiyar. A sabo da haka ne tace kundin tsarin mulkin Jamiyar na shekarar  2019 (Wanda aka yi wa Kwaskwarima) ya Basu damar daukan kwararan matakai da hukunci akan Julius Abure.

Daga bisani, Sanata Nenadi Usman ta nuna rashin amincewarta akan Yadda Julius Abure yake cin mutunci jagoran jam’iyar Labour na Kasa, Peter Obi da Gwamna Alex Otti. Tace Abure da mukarabansa wadanda wa’adinsu ya kare, basu da hurumin magana da yawun Jam’iyar kuma baza su iya dakatar da Gwamnan ba ko wani mamban Jamiyar.

 

Ta kuma shaidawa ‘Yan Nijeriya cewa, Jam’iyar ta sanar da Hukumar Zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) akan shirye-shiryenta na gudanar da zabuka a matakai daban-daban tare da gudanar da babban taron Jam’iyar na kasa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kano Ta Karɓi Rahoton Binciken Kwamishinan Sufuri Kan Belin Wanda Ake Zargi Da Safarar Kwayoyi

Gwamnatin Jihar Kano ta karɓi rahoton kwamitin bincike da aka kafa domin bincikar zargin da ake yi wa Kwamishinan Sufuri, Ibrahim Namadi, kan hannu da yake da shi a ceto wani da ake zargi da safarar miyagun kwayoyi, Sulaiman Aminu Danwawu.

Shugaban kwamitin kuma mai bai wa Gwamna Shawara kan Harkokin Shari’a da Tsarin Mulki, Barrister Aminu Hussain, ne ya mika rahoton ga Sakataren Gwamnati na Jiha, Alhaji Umar Farouk Ibrahim.

Barrister Hussain ya bayyana cewa kwamitin ya gudanar da bincike bisa gaskiya da adalci, da kuma bin hujjoji, ba tare da son rai ba.

Ya bayyana cewa an gayyato Kwamishinan Sufuri domin karin bayani, inda ya kuma gabatar da rubutaccen jawabi ga kwamitin.

Sauran da aka tattauna da su sun hada da Abubakar Umar Sharada, Mataimaki na Musamman kan Wayar da Kan Jama’a, da kuma Musa Ado Tsamiya, Mataimaki na Musamman kan magudanan ruwa.

Don tabbatar da ingancin rahoton, kwamitin ya tuntubi hukumomin tsaro da shari’a kamar DSS, NDLEA da Kungiyar Lauyoyi ta Najeriya (NBA). An kuma duba sahihan takardu da suka danganci lamarin tare da sharuddan doka da suka dace.

Barrister Hussain ya yabawa Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa kin tsoma baki da ya yi a lokacin gudanar da binciken, yana mai cewa hakan ya nuna irin shugabanci nagari da girmama tsarin doka.

Da yake karɓar rahoton, Sakataren Gwamnati ya nuna godiya kan yadda kwamitin ya gudanar da aikinsa bisa kwazo da kwarewa, duk da matsin lamba daga jama’a.

Ya jinjina musu kan jajircewa da tsayuwa akan gaskiya, tare da tabbatar da cewa za a mika rahoton ga Gwamna domin nazari da daukar matakin da ya dace.

Ya kara da cewa Gwamnatin Kano za ta duba cikakken rahoton tare da daukar matakan da suka dace bisa shawarar da kwamitin ya bayar.

 

Abdullahi Jalaluddeen

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Neja Ta Raba Motoci Ga Ma’aikata Da Hukumomi
  • Jama’a Suke Tona Asirin Gurɓattun Jami’anmu – Kwamishinan ‘Yansandan Kano
  • Yadda ’yan bindiga suka sace Zamfarawa 150 a cikin kwana 4
  • Kotun Ta Umurci Gwamnatin Neja Ta Janye Hukuncin Da Ta Dauka Akan Gidan Rediyon Badeggi
  • Duk wanda ya haka rijiyar burtsatse a Lekki ruwan masai yake sha – Gwamnatin Legas
  • Iran: An nada Larijani a matsayin sakataren kwamitin koli na tsaron kasa
  • Kotu ta hana jagoran adawa Maurice Kamto takarar shugaban ƙasa a Kamaru
  • Sanata Buba ya ƙaddamar da allurar rigakafin dabbobi kyauta
  • Gwamnatin Kano ta karɓi rahoton binciken Kwamishinan da ya yi belin Danwawu
  • Gwamnatin Kano Ta Karɓi Rahoton Binciken Kwamishinan Sufuri Kan Belin Wanda Ake Zargi Da Safarar Kwayoyi