Ma’aikatar harkokin wajen Iran ta yi tsokaci kan jita-jitar cewa: Shugaban kasar Iran zai gana da shugaban kasar Amurka

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Isma’il Baqa’i ya yi watsi da jita-jitar da ake yadawa game da batun cewa shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian zai yi wata ganawa da shugaban Amurka Donald Trump a mako mai zuwa, da rashin gamsuwar bangaren Amurka da Iran da shiga tsakanin masarautar Oman, da kuma cewa Iran ta gabatar da shawarar gudanar da shawarwari kai tsaye da Amurka, da sauran da’awar karya a matsayin batutuwa na jita-jita maras asali da tushe.

Dangane da wata tambaya game da jerin jita-jita da ake yadawa a kafafen yada labarai game da matsayin tattaunawar da ake yi tsakanin Iran da Amurka, kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya jaddada cewa duk wadanda batutuwa da suke fitowa daga majiyoyi marassa tushe da asali kuma mafi yawansu labarai ne na karya na bogi da ba su da wata madogara mai tushe. Baqa’i ya jaddada cewa: Ma’aikatar harkokin wajen kasar ita ce ke da alhakin ba da bayanai dangane da ayyukan jami’an diflomasiyya, ciki har da batun tattaunawar da ba na kai tsaye ba tsakanin Iran da Amurka, cikin gaskiya, kwarewa, da kuma lokacin da ya dace.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: aikatar harkokin wajen

এছাড়াও পড়ুন:

Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya: Akwai Babban Aiki A Gaban Nijeriya

Abbas ya kuma jaddada bukatar da dauki matakai, kan aukuwar sauyin yanayi, musamman duba da matsalar talauci da kuma ci gaba da fuskantar kalubalen rashin tsaro, da kasar nan, ke fuskanta.

Bugu da kari, Hukumar kula da ‘yan cirani ta duniya wato IOM ta sanar da cewa, gurbata muhalli da robobin da aka sarrafa zuke haifarwa, suna taka gudunmwa, wajen aukuwar dumamar yanayi da kuma gurbata muhalli.

A cewar Hukumar, matsalar na kuma lalata kasar noma da lalata hanyoyin ruwa, tare da kuma tilasta alumma, tashi daga matsugunan su, zuwa wasu gurare, domin su ci gaba da gudanar da rayuwarsu.

Hakazalika,  a cikin wasu rahotanni da Majalisar Dinkin Duniya ta fitar, sun bayyana cewa, a fadin duniya, ana yin amfani da Lidojin da suka kai, yawan miliyan 500 a duk shekara, wanda kusan tan miliyan 13, suke kwarara zuwa cikin Tekuna, a duk shekara.

Ana kuma yin amfani da Gangunan Mai miliyan 17, da aka sarrafa, aka kuma zuba a cikin Gangunan, inda kuma a fadin duniya, mutane ke sayen Kwalaben Man da suka kai miliyan daya.

An kiyasata cewa, a duk shekara, daobboin da ke rayuwa a cikin Tekuna  guda 100,000 ne, irin wadannan Robobin da aka zuba a cikin Tekunan, suke hallaka su.

Bugu da kari, wasu bincike da aka gudanar, sun nuna cewa, Ruwan sha da ake sarrafawa a sanya a cikin Robobin Shan Ruwa, sun kai kaso 90 a cikin dari, inda kuma Ruwan da ake samu daga Fanfuna, suka ke da kaso  83 a ckin dari, wadanda kuma suke dauke da sanadaran microplastic, da ke makalewa, a cikin Robobin, inda wannan sanadarin, ke shafar kiwon lafiyar bil Adama.

A Nijeriya za a iya cewa, kalubalen na muhalli sun kasance iri-iri, musamman duba da annobar ambaliyar ruwan sama da kasar ke fuskanta a duk lokacin damina da Fari da gurrbatar muhalli da kuma rashin samar da kyakyawan tsarin zubar da shara, musamman na bolar Robobin da aka gama amfani da su.

Misali, a ranar 28 na watan Mayun 2025, garin Mokwa, da ke a jihar Neja, an fuskanci, mummunar ambaliyar ruwan sama, inda jami’ai suka sanar da cewa, sama da mutane 200 da iftila’in ya aukwa, suka rasu tare da kuma bacewar mutane da yawansu ya kai sama da 1,000, wasu 121 suka samu raunuka, gidaje 2,000 suka lalace.

Irin wannan iftila’in na Mokwa, na daya daga cikin rin wadanda suka auku a shekarun baya a wasu sannan kasar.

Ana nan, muma mun goyi bayan furucin da Ministar Kula da Jindadi da Walwalar Mata Hajiya Imaan Sulaiman-Ibrahim ta yi, na ciwar kalubalen na gurbatar muhlaii, na janyo tarwatsa alumomin kasar, daga matsugunan su, musamman duba da yadda iftila’in, yafi shafar mata da yara.

Batun da ake yi na samar da wadataccen abincin a kasar, zai kasance ne tamkar wani mafarki, matukar mahukutna kasar, ba su yi gaggawar daukar matakan da suka kamata, kan batun na gurbatar muhalli, a kasar ba.

Domin samar da tsarin rage zubar da bola, musamman ta Robobi a kasar Gwamnatin Tarayya ta gabatar da wani tsari na  NPPWM.

Sai dai, wannan tsarin ya hadu da cikas, musamman duba da cewa, wanzar da tsarin daga bangaren Gwamnatin, ba ta mayar da hankali akansa ba, inda sai dai kawai, daidaikun ‘yan kasar ne a kashin kansu suke ci gaba da tsaftace guraren da ake jibge bola, musamman a birane da wasu guraren.

Shugabar Babban Majalisi a Majalisar Dinkin Duniya Maria Fernanda Espinosa Garcés, ta bayar da shawarar cewa, batun na gurbar muhalli, abu ne, da ya wajaba a sake tunani akai.

A daukacin jihohi 36 na kasar, Legas da Ekiti ne kawai, suka dauki matakan da suka kamata, kan kare gurbatar muhalli, a jihohinsu.

Kazalika, a matakin Majalisa, Shugaban Kwamiti kan Yada Labarai da Kula da Hudda da Jama’a Hon. Akin Rotimi ya shelanta cewa, daga cikin kudurori 899 da Majalisar ta gabatar a cikin shekaru biyu, guda 27 ne kacal, Majalisar ta mayar da hankali kan na kula da muhalli.

Sai dai, an ruwaito cewa, wani Majalisar na kan kokrin samar da wasu tsare-tsare na yakar yawan amfani da Robobin barkatai a kasar, musamman a biranen kasar.

A ra’ayin wannan Jaridar, muna goyon bayan cewa, ba zai yuwa a bar Nijeriya a baya, wajen shiga cikin kokarin da ake yi, a fadin duniya, na yakar gurbata muhalli ba.

Ya zama wajbi, bikin na wannan shekarar, ya kasance mataki na farko, na yakar gurbata muhalli, ba wai kawai tatsuniya ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Yi Matukar Allah Wadai Da Hare-Haren Da Amurka Ta Kaiwa Iran
  • Kiran Gwamnatin Tarayya Ga ‘Yan Jarida: Ku Zama Jigo Wajen Gina Dimokuraɗiyyar Nijeriya
  • Amurka ta ƙaddamar da hare-hare kan Iran
  • Za mu ci gaba da yi wa Isra’ila luguden wuta — Shugaban Iran
  • Ministan Harkokin Wajen Iran ya isa taron Kungiyar OIC a Turkiyya
  • Iran Ta Bayyana Sharaɗin Sasantawa Da Isra’ila – Ministan Harkokin Waje
  • Majalisa Na Binciken Yadda Aka Kashe Naira Tiriliyan 1.12 Na Tallafin Manoma
  • 2027: ‘Sai bayan babban taron APC Tinubu zai bayyana wanda za su yi takara tare’
  • Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya: Akwai Babban Aiki A Gaban Nijeriya
  • Nan da mako biyu za mu yanke shawara kan shigar wa Isra’ila yaƙi — Trump