An gabatar da sabbin shaidu kan Nnamdi Kanu
Published: 7th, May 2025 GMT
Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta saurari sabuwar shaida kan tuhumar da ake yi wa shugaban ƙungiyar ‘yan a waren Biafra (IPOB), Nnamdi Kanu.
A zaman kotun na ranar Laraba, an tuhumi Kanun da aikata laifuka bakwai, kuma Mai Shari’a James Omotosho ya bayar da damar gabatar da na’urar adana bayanai ta ‘flash’ mai ɗauke da bidiyoyi da wasiƙa mai kwanan wata 17 ga watan Yunin 2021 a matsayin sabbin shaidu.
A ɗaya daga cikin bidiyon da aka kunna a kotun, an ga Kanun na bai wa mabiyansa umarnin afka wa jami’an tsaro, su kuma ƙone ofisoshin ‘yan sanda.
Lauyan masu ƙara, Adegboyega Awomolo (SAN), ne ya gabatar da shaidun ta hannun sashin rundunar tsaron sirri (DSS).
A cikin bidiyon dai ya sanar da kafa ƙungiyar tsaron gabashin ƙasar (ESN), tare da neman magoya bayansa su kare garuruwansu daga abin da ya kira mamayar al’ummar Fulani.
A hannu guda kuma, wasiƙar da ta fito daga hannun Antoni Janar na ƙasa ta bai wa DSS umarnin binciken Kanu kan aikata laifukan haɗin baki, kisa, ƙone-ƙone, da kisan jami’an tsaro.
Wasiƙar ta kuma zayyano wata wallafar bidiyo da ya yi a shafinsa na Facebook lokacin zanga-zangar EndSARS a Legas, in da ya bai wa mabiyansa umarnin shirya jerin gwanon hare-hare.
A cikin bidiyon an kuma jiyo muryar da ake zargin ta Kanu ce yana ba da umarnin kashe duk wani ɗan sanda da aka yi ido huɗu da shi, a kuma ƙone ofisoshinsu.
“Ku fara kashe sojoji yanzu, ku rutsa su, ku haƙa ramuka a titi motocinsu su faɗa su mutu,” in ji muryar.
Ya kuma gargaɗi jagororin yankin tare da ba su umarnin korar Fulani makiyaya inda ya ce za su ɗauki fansar duk ɗan Biafran da ya rasa ransa.”
A wani bidiyon kuma an ga Kanu na bayyana hana zirga-zirga a yankin gabashin ƙasar baki ɗaya, domin tunawa da ‘yan Biafra da suka mutu, tare da bayyana hukuncin kisa ga duk wanda ya saɓawa umarnin.
Daga nan ne Alƙalin kotun ya sanya 8 ga watan Mayu domin ci gaba da sauraron shari’ar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan awaren Biyafara yan IPOB
এছাড়াও পড়ুন:
Karramawar LEADERSHIP Gare Ni, Zaburantarwa Ce Ga Ci Gaba Da Kyawawan Manufofin Mu – Gwamna Lawal
Ya ƙara da cewax gwamnatinsa ta fara gyara daga tushe, inda ilimi ya zama ginshiƙin farko. “Shekaru takwas kafin mu hau mulki, ɗalibanmu ba su samun takardun WAEC, sannan tsawon shekaru biyu suna fama da matsalar NECO. Na biya Naira Biliyan huɗu don magance wannan matsala,” inji shi.
Gwamnan ya bayyana irin matsalolin da ya gada, yana mai cewa: “Na samu asusun gwamnati da naira miliyan huɗu kacal. Ma’aikata suna karɓar albashi cikin rashin tabbas, babu ruwa, asibitoci kuwa suna cikin mummunan yanayi.”
Lawal ya ce, ya sake fasalin tsarin gwamnati, inda ya rage yawan kwamishinoni da manyan sakatarorin don rage ɓarna da ƙara inganci. “Yanzu muna daga cikin jihohi mafi ci gaba wajen tara haraji, inda kuɗaɗen shiga suka ƙaru da fiye da kaso 300 cikin 100,” inji shi.
Ya bayyana cewa gwamnatin sa ta gina ko ta gyara makarantu sama da 500, tare da aiwatar da ayyukan da kuɗinsu ya kai biliyan N10 a kowace ƙaramar hukuma. Duk da cewa ana cire biliyan 1.2 a kowane wata daga kuɗaɗen gwamnati don biyan basussuka, an biya bashin fansho da giratuti na fiye da biliyan N13.6 da aka tara tun shekarar 2011.
A ɓangaren tsaro, Lawal ya ce jihar ta ɗan sami sauƙi bayan kafa rundunar tsaron gida, yayin da gwamnati ke ƙoƙarin tabbatar da amfanin mulki ya kai ga talaka.
A nasa jawabin, Babban Editan LEADERSHIP, Azu Ishiekwene, ya ce an bai wa gwamnan wannan lambar yabo ne saboda irin nasarorin da ya samu a fannonin tsaro, ilimi, lafiya da gine-gine, yana mai cewa “jarida tana da alhakin duba gwamnati, amma kuma tana da haƙƙin yabawa idan ana yin daidai.”
ShareTweetSendShare MASU ALAKA