An gabatar da sabbin shaidu kan Nnamdi Kanu
Published: 7th, May 2025 GMT
Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta saurari sabuwar shaida kan tuhumar da ake yi wa shugaban ƙungiyar ‘yan a waren Biafra (IPOB), Nnamdi Kanu.
A zaman kotun na ranar Laraba, an tuhumi Kanun da aikata laifuka bakwai, kuma Mai Shari’a James Omotosho ya bayar da damar gabatar da na’urar adana bayanai ta ‘flash’ mai ɗauke da bidiyoyi da wasiƙa mai kwanan wata 17 ga watan Yunin 2021 a matsayin sabbin shaidu.
A ɗaya daga cikin bidiyon da aka kunna a kotun, an ga Kanun na bai wa mabiyansa umarnin afka wa jami’an tsaro, su kuma ƙone ofisoshin ‘yan sanda.
Lauyan masu ƙara, Adegboyega Awomolo (SAN), ne ya gabatar da shaidun ta hannun sashin rundunar tsaron sirri (DSS).
A cikin bidiyon dai ya sanar da kafa ƙungiyar tsaron gabashin ƙasar (ESN), tare da neman magoya bayansa su kare garuruwansu daga abin da ya kira mamayar al’ummar Fulani.
A hannu guda kuma, wasiƙar da ta fito daga hannun Antoni Janar na ƙasa ta bai wa DSS umarnin binciken Kanu kan aikata laifukan haɗin baki, kisa, ƙone-ƙone, da kisan jami’an tsaro.
Wasiƙar ta kuma zayyano wata wallafar bidiyo da ya yi a shafinsa na Facebook lokacin zanga-zangar EndSARS a Legas, in da ya bai wa mabiyansa umarnin shirya jerin gwanon hare-hare.
A cikin bidiyon an kuma jiyo muryar da ake zargin ta Kanu ce yana ba da umarnin kashe duk wani ɗan sanda da aka yi ido huɗu da shi, a kuma ƙone ofisoshinsu.
“Ku fara kashe sojoji yanzu, ku rutsa su, ku haƙa ramuka a titi motocinsu su faɗa su mutu,” in ji muryar.
Ya kuma gargaɗi jagororin yankin tare da ba su umarnin korar Fulani makiyaya inda ya ce za su ɗauki fansar duk ɗan Biafran da ya rasa ransa.”
A wani bidiyon kuma an ga Kanu na bayyana hana zirga-zirga a yankin gabashin ƙasar baki ɗaya, domin tunawa da ‘yan Biafra da suka mutu, tare da bayyana hukuncin kisa ga duk wanda ya saɓawa umarnin.
Daga nan ne Alƙalin kotun ya sanya 8 ga watan Mayu domin ci gaba da sauraron shari’ar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan awaren Biyafara yan IPOB
এছাড়াও পড়ুন:
DSS ta yi wa Malami tambayoyi kan harin da aka kai masa a Kebbi
Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta yi wa tsohon Ministan Shari’a kuma Antoni-Janar na Gwamnatin Tarayya, Abubakar Malami, tambayoyi a kan harin da aka kai wa ayarin motocinsa a Jihar Kebbi.
An gudanar da tambayoyin ne a ofishin hukumar na Birnin Kebbi a ranar Litinin, inda Malami ya bayyana cewa an yi masa tambayoyin cikin ƙwarewa da mutuntawa.
A ranar 1 ga Satumba, 2025 ne aka kai wa ayarin motocin da ke rakiyar Malami hari a Birnin Kebbi, bayan ya dawo daga gaisuwar ta’aziyya ga iyalan marigayi Babban Limamin Masallacin Dakta Bello Haliru Jumu’a.
Shaidu sun bayyana cewa an lalata motocin rakiyarsa kusan guda 10, sannan da dama daga cikin magoya bayansa sun jikkata.
Burkina Faso, Mali da Nijar sun fice daga Kotun ICC ’Yan sanda sun kama mutum 4 kan kai wa Lakurawa babura a KebbiMalami ya yi zargin cewa harin yana da nasaba da siyasa, duk da cewa jam’iyya mai mulkin jihar — APC, ta nesanta kanta daga lamarin.
Daga bisani Malami ya shigar da ƙorafi zuwa ga hukumomin tsaro, ciki har da ’yan sanda da DSS.
A wani jawabi da ya wallafa a shafinsa na Facebook da yammacin Litinin, Malami ya ce an gudanar da binciken cikin gaskiya da ƙwarewa, tare da nuna masa mutuntawa.
“Na tabbatar cewa DSS ta gayyace ni domin bayar da gudunmawa wajen binciken harin da aka kai mini da ’yan rakiyata a Kebbi a ranar 1 ga Satumba, 2025.
“Ƙorafin ya samo asali ne daga manyan ’yan adawa a jihar. Ina yaba wa hukumar DSS bisa yadda suka gudanar da binciken cikin gaskiya da mutunci.
“An yi min tambayoyi cikin mutuntawa, kuma zan ci gaba da bayar da haɗin kai don tabbatar da kammala binciken yadda ya kamata,” in ji shi.