An gabatar da sabbin shaidu kan Nnamdi Kanu
Published: 7th, May 2025 GMT
Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta saurari sabuwar shaida kan tuhumar da ake yi wa shugaban ƙungiyar ‘yan a waren Biafra (IPOB), Nnamdi Kanu.
A zaman kotun na ranar Laraba, an tuhumi Kanun da aikata laifuka bakwai, kuma Mai Shari’a James Omotosho ya bayar da damar gabatar da na’urar adana bayanai ta ‘flash’ mai ɗauke da bidiyoyi da wasiƙa mai kwanan wata 17 ga watan Yunin 2021 a matsayin sabbin shaidu.
A ɗaya daga cikin bidiyon da aka kunna a kotun, an ga Kanun na bai wa mabiyansa umarnin afka wa jami’an tsaro, su kuma ƙone ofisoshin ‘yan sanda.
Lauyan masu ƙara, Adegboyega Awomolo (SAN), ne ya gabatar da shaidun ta hannun sashin rundunar tsaron sirri (DSS).
A cikin bidiyon dai ya sanar da kafa ƙungiyar tsaron gabashin ƙasar (ESN), tare da neman magoya bayansa su kare garuruwansu daga abin da ya kira mamayar al’ummar Fulani.
A hannu guda kuma, wasiƙar da ta fito daga hannun Antoni Janar na ƙasa ta bai wa DSS umarnin binciken Kanu kan aikata laifukan haɗin baki, kisa, ƙone-ƙone, da kisan jami’an tsaro.
Wasiƙar ta kuma zayyano wata wallafar bidiyo da ya yi a shafinsa na Facebook lokacin zanga-zangar EndSARS a Legas, in da ya bai wa mabiyansa umarnin shirya jerin gwanon hare-hare.
A cikin bidiyon an kuma jiyo muryar da ake zargin ta Kanu ce yana ba da umarnin kashe duk wani ɗan sanda da aka yi ido huɗu da shi, a kuma ƙone ofisoshinsu.
“Ku fara kashe sojoji yanzu, ku rutsa su, ku haƙa ramuka a titi motocinsu su faɗa su mutu,” in ji muryar.
Ya kuma gargaɗi jagororin yankin tare da ba su umarnin korar Fulani makiyaya inda ya ce za su ɗauki fansar duk ɗan Biafran da ya rasa ransa.”
A wani bidiyon kuma an ga Kanu na bayyana hana zirga-zirga a yankin gabashin ƙasar baki ɗaya, domin tunawa da ‘yan Biafra da suka mutu, tare da bayyana hukuncin kisa ga duk wanda ya saɓawa umarnin.
Daga nan ne Alƙalin kotun ya sanya 8 ga watan Mayu domin ci gaba da sauraron shari’ar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan awaren Biyafara yan IPOB
এছাড়াও পড়ুন:
Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana
Waɗannan bayanai duk suna ƙunshe ne a cikin jawaban da aka gudanar a gangamin wayar da kai game da wannan cuta, wanda ya gudana a Kaduna.
Lokacin da ta ke zantawa da manema labarai jim kaɗan bayan wannan gangami, Dr. Maimuna Lawal Garba, ƙwararriyar Likita a fannin hanci, kunni da maƙogwaro, ta fara bayanin ta ne da bayyana abubuwan da suke haddasa wannan cuta ta Kansar Maƙogwaro.
Ta ce, “Muna bai wa mutane shawara su kiyayi shan tabar sigari, barasa (giya). Haka kuma akwai yanayin aikin mutane, misali, masu aiki a wurin yankan katako, wannan ƙurar ta katako tana daga cikin abubuwan da za su iya sabbaba ma mutum kamuwa da wannan cuta.
“Haka kuma akwai (radiation), na’urar haske, idan ya shiga ƙwaƙwalwa zai iya haifar da wannan cuta. Haka kuma akwai yawan shekaru na tsufa, akwai kuma ƙwayar cutar HPF, ita ma tana sabbaba kamuwa da wannan cuta. Haka kuma idan mutum yana da gadon wannan cuta, shi ma zai iya zama musabbabin kamuwa.”
Shi kuwa Dr. Muhammad Sani, wanda ya ke shi ma Likita ne a wannan fanni na Hanci, Kunni da Maƙogwaro, cikin jawabin sa, ya ce, abin takaici ne ganin cewa wannan cuta ta Kansar Hanci, Kunne da Maƙogwaro tana ƙara yaɗuwa a duniya, musamman yankin Afrika, wanda kuma Nijeriya na ciki.
Da ya ke ƙarin haske, Dr. Usman Ibrahim Sani, wanda shi ma ƙwararren Likita ne a wannan fanni, ya bayyana cewa ba wai masu shan sigari da giya ne kawai suke kamuwa da wannan cuta ba, “zai iya faruwa da waɗanda ba sa mu’amala da waɗannan abubuawa, amma yana da kyau mutum ya garzaya asibiti tun abin na ɗan ƙarami, ta yadda zai fi sauƙin magancewa,”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp