Mazauna gari sun kori Boko Haram bayan kashe kyaftin ɗin soja
Published: 7th, May 2025 GMT
Al’ummar garin Izge da ke Ƙaramar Hukumar Gwoza ta Jihar Borno sun fatattaki ’yan ƙungiyar Boko Haram bayan kai musu hari a ranar Laraba.
Ƙungiyar ‘yan ta’addan ta kuma kashe wani kaftin ɗin soji a harbin na ba zata.
Jami’an tsaro na ba da gudunmawar aikata miyagun laifuka a Nijeriya — Zulum Jami’an tsaro na ba da gudunmawar aikata miyagun laifuka a Nijeriya — ZulumSarkin Gwoza Mohammed Shehu Timta ya ce ’yan ta’addan sun afka musu ne da ƙarfe 1:00 na dare.
“Da gaske ne Boko Haram sun afka wa garinmu. Kuma an yi rashin sa’a wani kaftin ɗin soja ya rasa ransa.
“Jami’an tsaronmu na sa-kai sun samu nasarar kashe ‘yan ta’addan uku. Sauran sun gudu sun bar babura 10 da wasu makamai,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Boko Haram
এছাড়াও পড়ুন:
Tarayyar Turai: Muna Goyon Bayan Warware Batun Nukiliyar Iran Ta Hanyar Diplomasiyya
Jami’ar siyasar waje ta tarayyar turai Kaja Kallas ta bayyana cikakken goyon baya ga warware batun makamashin Nukiliyar Iran ta hanyar diplomasiyya.
Jami’ar ta wallafa a shafinta na X cewa: Na tattauna da ministan harkokin wajen Iran Abbas Arakci domin tabbatar da goyon bayan kungiyar tarayyar turai akan aiki da hanyar diplomasiyya domin warware batun Nukiliyar Iran da kuma rage rikice-rikice a cikin wannan yankin.”
Haka nan kuma Kallas ta jaddada abinda a baya tarayyar turai din ta rika riyawa da ba shi da tushe na cewa, Iran tana bai wa Rasha taimakon soja tana mai cewa: ” Na kuma yi kira ga Iran da ta dakatar da bai wa Rasha taimakon soja.”
Iran dai ta sha yin watsi da wannan irin zargin na cewa tana bai wa kasr Rasha makamai.
Matsayar tarayyar turai din dai ta zo ne bayan yin zango na uku na tattaunawa a tsakanin Iran da Amurka ta hanyar shiga tsakanin kasar Oman wacce aka fara tun a karshen watan Afrilu.