Aminiya:
2025-11-08@21:53:47 GMT

Mazauna gari sun kori Boko Haram bayan kashe kyaftin ɗin soja

Published: 7th, May 2025 GMT

Al’ummar garin Izge da ke Ƙaramar Hukumar Gwoza ta Jihar Borno sun fatattaki ’yan ƙungiyar Boko Haram bayan kai musu hari a ranar Laraba.

Ƙungiyar ‘yan ta’addan ta kuma kashe wani kaftin ɗin soji a harbin na ba zata.

Jami’an tsaro na ba da gudunmawar aikata miyagun laifuka a NijeriyaZulum Jami’an tsaro na ba da gudunmawar aikata miyagun laifuka a Nijeriya — Zulum

Sarkin Gwoza Mohammed Shehu Timta ya ce ’yan ta’addan sun afka musu ne da ƙarfe 1:00 na dare.

“Da gaske ne Boko Haram sun afka wa garinmu. Kuma an yi rashin sa’a wani kaftin ɗin soja ya rasa ransa.

“Jami’an tsaronmu na sa-kai sun samu nasarar kashe ‘yan ta’addan uku. Sauran sun gudu sun bar babura 10 da wasu makamai,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Boko Haram

এছাড়াও পড়ুন:

Uwargidan Gwamnan Gombe ta nemi a tsawaita hutun haihuwa na mata ma’aikata

Uwargidan Gwamnan Jihar Gombe, Hajiya Asma’u Muhammadu Inuwa Yahaya, ta jagoranci wani yunƙuri na ganin an tsawaita hutun haihuwa na mata ma’aikata daga watanni uku zuwa shida.

Ta jagoranci manyan jami’an lafiya zuwa majalisar dokokin jihar domin neman goyon bayan doka kan wannan shiri.

Barau ya nemi Trump ya janye kalamansa, ya nemi afuwar Najeriya Matsalar Tsaro: Mun samu gagarumin ci gaba a shekaru biyu — Tinubu

A yayin taron wayar da kai a majalisar, Hajiya Asma’u ta bayyana cewa shayar da jarirai nono har watanni shida yana da matuƙar amfani wajen rage mace-macen jarirai, inganta garkuwar jikinsu, da bunƙasa ƙwaƙwalwarsu.

Uwargidan ta roƙi majalisar, ƙarƙashin jagorancin Kakakin Majalisar, Abubakar Mohammed Luggerewo, da su samar da doka da za ta tabbatar da wannan shiri.

Kakakin Majalisar, ya yaba da ƙoƙarin Uwargidan Gwamnan, inda ya ce wannan ziyarar “ta tarihi ce” kuma ya tabbatar da goyon bayan majalisar wajen ganin an aiwatar da ƙudirin.

Haka kuma, wakiliyar Ƙungiyar Gwamnonin Najeriya (NGF), Miss Omowumi Gbamis, ta ce wannan doka zai taimaka wa mata su ci gaba da aiki lafiya tare da inganta lafiyar jarirai.

Kodinetan CS-SUNN a Gombe, Misis Comfort Mukollo, ta bayyana cewa suna aiki tare da UNICEF da ma’aikatun gwamnati don tallafa wa shirye-shiryen kula da abincin uwa da jariri tare da wayar da kan jama’a kan muhimmancin shayar da nono.

Daga cikin manyan jami’an da suka nuna goyon baya akwai Kwamishiniyar Harkokin Mata, Asma’u Mohammed Iganus, da Shugaban Kwamitin Lafiya na Majalisar, Siddi Buba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ban taɓa zargin Shettima da ƙirƙiro Boko Haram ba — Sheriff
  • Yaran Bello Turji sun kashe mutum 5, sun sace 9 a Sakkwato
  • Ban ɓata zargin Shettima da ƙirƙiro Boko Haram ba — Sheriff
  • Uwargidan Gwamnan Gombe ta nemi a tsawaita hutun haihuwa na mata ma’aikata
  • An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano
  • Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump
  • Kamfanin wutar lantarki na Abuja ya salami ma’aikata 800
  • Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji
  • Ajax ta kori kocinta John Heitinga
  • Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari