Mazauna gari sun kori Boko Haram bayan kashe kyaftin ɗin soja
Published: 7th, May 2025 GMT
Al’ummar garin Izge da ke Ƙaramar Hukumar Gwoza ta Jihar Borno sun fatattaki ’yan ƙungiyar Boko Haram bayan kai musu hari a ranar Laraba.
Ƙungiyar ‘yan ta’addan ta kuma kashe wani kaftin ɗin soji a harbin na ba zata.
Jami’an tsaro na ba da gudunmawar aikata miyagun laifuka a Nijeriya — Zulum Jami’an tsaro na ba da gudunmawar aikata miyagun laifuka a Nijeriya — ZulumSarkin Gwoza Mohammed Shehu Timta ya ce ’yan ta’addan sun afka musu ne da ƙarfe 1:00 na dare.
“Da gaske ne Boko Haram sun afka wa garinmu. Kuma an yi rashin sa’a wani kaftin ɗin soja ya rasa ransa.
“Jami’an tsaronmu na sa-kai sun samu nasarar kashe ‘yan ta’addan uku. Sauran sun gudu sun bar babura 10 da wasu makamai,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Boko Haram
এছাড়াও পড়ুন:
Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp