Aminiya:
2025-09-24@14:04:53 GMT

Mazauna gari sun kori Boko Haram bayan kashe kyaftin ɗin soja

Published: 7th, May 2025 GMT

Al’ummar garin Izge da ke Ƙaramar Hukumar Gwoza ta Jihar Borno sun fatattaki ’yan ƙungiyar Boko Haram bayan kai musu hari a ranar Laraba.

Ƙungiyar ‘yan ta’addan ta kuma kashe wani kaftin ɗin soji a harbin na ba zata.

Jami’an tsaro na ba da gudunmawar aikata miyagun laifuka a NijeriyaZulum Jami’an tsaro na ba da gudunmawar aikata miyagun laifuka a Nijeriya — Zulum

Sarkin Gwoza Mohammed Shehu Timta ya ce ’yan ta’addan sun afka musu ne da ƙarfe 1:00 na dare.

“Da gaske ne Boko Haram sun afka wa garinmu. Kuma an yi rashin sa’a wani kaftin ɗin soja ya rasa ransa.

“Jami’an tsaronmu na sa-kai sun samu nasarar kashe ‘yan ta’addan uku. Sauran sun gudu sun bar babura 10 da wasu makamai,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Boko Haram

এছাড়াও পড়ুন:

Bayan Sulhu  Da Ƴan Bindiga, An Saki Mutane 70 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina

Mutune 70 da aka yi garkuwa da su sun samu ƴanci a Jihar Katsina, bayan yarjejeniyar sulhu da aka ƙulla da fitaccen shugaban ƴan bindiga, Isiya Kwashen Garwa. A wani faifan bidiyo da ya bayyana, Garwa ya saki mutane 40 a ƙaramar hukumar Faskari, kwanaki biyu bayan ya fara sakin wasu 30, wanda hakan ya kai adadin zuwa 70 gaba ɗaya.

Rahotanni daga mazauna yankin sun ce sakin na baya-bayan nan ya biyo bayan tattaunawa tsakanin shugabannin al’umma da sansanin Garwa, a wani mataki da ake ganin zai rage tashin hankali da hare-hare a yankin. Duk da haka, Garwa ya nuna rashin jin daɗi kan abin da ya kira sumamen Sojoji a unguwar Ruwan Godiya a lokacin Sallar Juma’a, inda ya yi zargin cewa wasu Hausawa da Fulani sun samu raunuka. Ya gargaɗi cewa irin waɗannan hare-hare na iya rusa sulhun da aka ƙulla.

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Sulhu Da Ƴan Bindiga A Katsina An Cafke Wani Magidanci Da Lafin Sojan Gona A Katsina

Hukumomin jihar ba su fitar da wata sanarwa ba kan sumamen da ake zargin ba, sai dai majiyoyin tsaro sun ce an kai hare-haren ne kan maboyar ƴan ta’adda tare da nufin kare rayukan jama’a. Mutanen da aka sako, galibinsu manoma ne da aka sace daga ƙauyukan karkara a Faskari, suna cikin kulawar likitoci da kuma binciken tsaro kafin a mayar da su wurin iyalansu.

Gwamnatin jihar ta ce tattaunawa tana daga cikin dabarun tsaro da ake amfani da su, amma ta jaddada cewa dole ne ƴan bindiga su miƙa makamansu gaba ɗaya tare da fuskantar hukunci kan laifuffukan da suka aikata.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kama Tsohon Ɗan Wasan Super Eagles, Victor Ezeji, Kan Zargin Aikata Zambar ₦39.8m
  • Kasashen Afirka Uku Sun Sanar Da Ficewa DagaKotun Hukunta Manyan Laifuka Ta Duniya
  • Kotun Indiya ta daure dan Najeriya shekara 10 kan safarar miyagun kwayoyi
  • Burkina Faso, Mali da Nijar sun fice daga Kotun ICC
  • NAJERIYA A YAU: Abin Da Doka Ya Ce Kan Kisan Jami’an ‘Yan Sanda
  • Bayan Sulhu  Da Ƴan Bindiga, An Saki Mutane 70 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina
  • Cikin Mako 2, An Kashe Jami’an Tsaro 53 A Faɗin Nijeriya
  • An kashe jami’an tsaro 53 a cikin mako biyu —Bincike
  • Bayan Nesanta Kanta, Jami’ar European American Ta Yi Wa Rarara Tayin Digiri
  • Komai Nisan Dare Gari Zai Waye