Kasar Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Tattaunawar Cinikayya Da Za A Yi Tsakanin Babban Jami’inta Da Na Amurka
Published: 7th, May 2025 GMT
Ma’aikatar kula da harkokin cinikayya ta kasar Sin, ta ce sabuwar gwamnatin Amurka ta dauki jerin matakan kakaba haraji na ba gaira ba dalili, lamarin da ya kawo tsaiko ga dangantakar cinikayya da tattalin arziki tsakanin kasashen biyu da ma tsarin cinikayya da tattalin arziki na duniya, tare da kawo kalubale mai tsanani ga farfadowar tattalin arzikin duniya.
Kuma domin kare hakkoki da muradunta, Sin ta dauki matakan mayar da martani.
A cewar kakakin ma’aikatar, a baya bayan nan, bangaren Amurka ya bayyana shirinsa na tattaunawa kan batun harajin da sauran batutuwa masu nasaba da shi ta hanyoyi da dama. Kuma bayan nazartar sakonnin Amurka, kasar Sin ta yanke shawarar tattaunawa da ita, bisa la’akari da burin al’ummun duniya da muradun kasa, da kuma kiraye kiraye daga masana’antun Amurka da masu sayayya na kasar. Kuma a matsayinsa na jagoran tawagar Sin a tattaunawar harkokin tattalin arziki da cinikayya tsakaninta da Amurka, mataimakin firaministan kasar He Lifeng zai gana da sakataren Baitul malin Amurka Scott Bessent.
Tattalin Arzikin Sin Tamkar Teku Ne Ba Karamin Tabki Ba Korar Ma’aikata: Likitocin Birnin Tarayya Sun Tsunduma Yajin Aikin Gargadi Na Kwanaki 3Kakakin ya ce matsayar kasar Sin bata sauya ba, idan aka tilasta mata shiga fada, to a shirye take, idan kuma tattaunawa ake son yi, kofarta a bude take.
Ya kuma yi gargadin cewa, duk wani yunkuri na fakewa da tattaunawar a matsayin wata dama ta matsin lamba ko barazana, toh, kasar Sin ba za ta cimma wata yarjejeniyar da za ta kai ga sadaukar da ka’idojinta, ko lalata tsarin adalci da tsare gaskiya a duniya ba. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
An sallami ƙarin ma’aikata 639 a tashar Muryar Amurka
Hukumar da ke kula da kafar yaɗa labarai ta Muryar Amurka (VOA) ta sallami ƙarin ’yan jarida da sauran ma’aikata 639 a ranar Juma’a.
Hukumar Kula da Harkokin Watsa Labarai ta Duniya ta Amurka (USAGM) ta bayyana cewa kawo yanzu an sallami ma’aikata 1,400 a wani bangare na shirin Shugaban Amurka Donald Trump na rage ma’aikata a hukumar zuwa mafi ƙarancin adadi kamar yadda doka ta tanada.
Hakan na nufin an kori mutum takwas a cikin kowane ma’aikata 10 da ke VOA a wata uku da suka gabata, a sakamakon wannan matakin Hukumar USAGM ta ɗauka.
Babbar Mashawarciya ga Hukumar, Kari Lake, ta bayyana cewa, “An aika wa ma’aikata 639 a VOA da USAGM da takardun kora a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin da ya kamata a yi tun da daɗewa don kawar da dimbin ma’aikata cima-zaune da kuma rashin riƙon amana a hukumar,” in ji sanarwar da ta fitar.
Yadda Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi muhimmanci a Isra’ila 2027: Manyan ’Yan adawa na neman rajistar sabuwar jam’iyyaLake ta kuma tabbatar da cewa hukumar ta kasance “cike da jami’an da ba sa aiki komai, nuna son kai, da ɓarnatar da dukiya.”
Ta bayyana cewa wannan mataki na nufin USAGM yanzu tana aiki kusa da mafi ƙarancin ma’aikata 81 da doka ta tanada.
Ma’aikata 250 kuma za su ci gaba da zama a Ofishin Watsa Labarai na Cuba (OCB), wanda ke watsa labarai zuwa ƙasar Cuba mai mulkin kwaminisanci.
An lura cewa babu ko ɗaya daga cikin ma’aikata 33 na OCB da aka kora.
Wannan mataki mai yiwuwa alama ce ta kusan kawo ƙarshen wannan shahararren gidan rediyo VOA wanda miliyoyin mutane ke saurara tsawon shekara 50 a faɗin duniya.
VOA, wadda aka kafa a 1942 don yaƙar farfagandar Nazi, tana watsa shirye-shirye a kusan harsuna 50 kuma ta mutane miliyan 360 ke sauraron shirye-shiryenta a mako, a faɗin duniya.
A watan Mayu aka kori ma’aikatan kwangila kusan 600 na VOA.
Wasu ’yan jam’iyyar Republican a baya sun zargi tashar da sauran kafofin yaɗa labarai masu samun tallafin gwamnati da nuna son kai ga masu ra’ayin mazan jiya, suna masu kira da a rufe tashar a matsayin wani ɓangare na rage kashe kuɗin gwamnati.
Wata tashar USAGM, Radio Free Asia, wadda tuni aka rage ma’aikatanta sosai, ta sanar a cikin wani sakon imel ga ma’aikata a ranar Juma’a cewa tana aiwatar da karin hutun tilas a sassa daban-daban.
Ana ci gaba da shari’o’i daban-daban kan lamarin korar ma’aikatan na USAGM.