Ma’aikatar kula da harkokin cinikayya ta kasar Sin, ta ce sabuwar gwamnatin Amurka ta dauki jerin matakan kakaba haraji na ba gaira ba dalili, lamarin da ya kawo tsaiko ga dangantakar cinikayya da tattalin arziki tsakanin kasashen biyu da ma tsarin cinikayya da tattalin arziki na duniya, tare da kawo kalubale mai tsanani ga farfadowar tattalin arzikin duniya.

Kuma domin kare hakkoki da muradunta, Sin ta dauki matakan mayar da martani.

A cewar kakakin ma’aikatar, a baya bayan nan, bangaren Amurka ya bayyana shirinsa na tattaunawa kan batun harajin da sauran batutuwa masu nasaba da shi ta hanyoyi da dama. Kuma bayan nazartar sakonnin Amurka, kasar Sin ta yanke shawarar tattaunawa da ita, bisa la’akari da burin al’ummun duniya da muradun kasa, da kuma kiraye kiraye daga masana’antun Amurka da masu sayayya na kasar. Kuma a matsayinsa na jagoran tawagar Sin a tattaunawar harkokin tattalin arziki da cinikayya tsakaninta da Amurka, mataimakin firaministan kasar He Lifeng zai gana da sakataren Baitul malin Amurka Scott Bessent.

Tattalin Arzikin Sin Tamkar Teku Ne Ba Karamin Tabki Ba Korar Ma’aikata: Likitocin Birnin Tarayya Sun Tsunduma Yajin Aikin Gargadi Na Kwanaki 3 

Kakakin ya ce matsayar kasar Sin bata sauya ba, idan aka tilasta mata shiga fada, to a shirye take, idan kuma tattaunawa ake son yi, kofarta a bude take.

Ya kuma yi gargadin cewa, duk wani yunkuri na fakewa da tattaunawar a matsayin wata dama ta matsin lamba ko barazana, toh, kasar Sin ba za ta cimma wata yarjejeniyar da za ta kai ga sadaukar da ka’idojinta, ko lalata tsarin adalci da tsare gaskiya a duniya ba. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sharhin bayan Labarai: Ci Gaban Harkokin Kasuwanci Tsakanin Iran Da Kasashen Waje Duk Tare Da Takunkuman Kasashen Yamma

Assalamu alaikum masu sauraro sharhin bayan labarammu zai yi magana dangane da “Bankasar tattalin arzikin Iran duk tare da takunkuman tattalin arziki masu tsanani wadanda kasashen yamma musamman Amurka suka doramata, wanda ni tahir amin zan karanta.

////…A dai-dai lokacinda gwamnatin kasar Amurka take barazanar zata hana sayan danyen man fetur daga kasar Iran kwatakwata, sannan take barazanar zata farwa kasar da yaki saboda shirin na makamashin nukliya, sabbin rahotanni sun bayyana cewa iran tana gaba a fitar da kayaki kasuwanci zuwa kasar China sannan ita ce ta 9 a duniya wajen samar da kwan kaji da sauran tsuntsaye.

Kamfanin dillancin labaran Parstoday na kasar Iran ya bayyana cewa, yawan danyen man fetur wanda kasar Iran take sayarwa kasar China kadai  ya kai ganga miliyon 1.8 a ko wace rana a cikin watan Mayun da ya gabata na wannan shekara ta 2025.

Labarin ya kara da cewa kasar Iran a halin yanzu tana sayarwa kasashe 110 kayakin abinci na halal, wadanda suka hana da nama da sauran kayakin abincin na dabbobi. Kuma ita ce kasa ta 9 a duniya wajen samar da kwan suntsaye.

A wani labarin kuma yankin ciniki mara shinge na Aras ya samar da kudaden shiga ga kasar wanda ya kai dalar Amurka miliyon $200 a shekara ta 2024 da ta gabata. Hadi Moghaddamzadeh, shugaban yankin ya bayyana cewa yankin nasa ya samar da kudaden shiga hard alar Amurka miliyon 200, a arewa maso yammacin kasar kuma kudaden shigan da aka samu daga kasar Azerbaijan kadai ya kai dalar Amurka miliyon 11.

A lokacinda yake magana da kamfanin dillancin labaran Pars today a gefen kasuwar baje koli na Iran Expo 2025 wanda aka gudanar a nan Tehran Moghaddamzadeh ya kara da cewa yankin ciniki mara shingen na Aras ya fi muhimmanci a kan sauran iran wannan yankunan da ake da su a nan kasar Iran, saboda wuraren yawon bude ido da shakatawa da yankin yake da su.

A bangaren sayar da kayakin abinci wanda ake kira Halal kuma, shi ne kayakin da iran take fitarwa zuwa kashe kimani 110 a duniya, kuma yake gaza da wasu kasashe a wannan bangaren.

Darakta mai kula da wannan bangaren, ya ce kayakin abinci na Halal wadanda suke fita daga kasar Iran suna zuwa kasashen kamar Malaysia, Singapore, kasashen yankin tekun farisa, arewacin Africa da sauransu.

Ya ce a yankin dai kayakin abinci daga Iran suna shiga kasashen Iraq, Turkiyya, UAE, Afghanistan, Russia, da wasu kasashen Turai.

Sannan shugaban kwastom na Jolfa, ya bayyana cewa a watan da ya gabata, kayakin abince na kimani dalar Amurka miliyon 8.5 suka fita da kofar fitar da kayaki kasuwanci a yankinsa a watan da ya gabata kadai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Siriya Tana Neman Tattaunawa Da Gwamnatin Mamayar Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Babban Hafsan Sojan Nijeriya Ya Sha Alwashin Inganta Tsaro A Yobe
  • Jakadan Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Najeriya
  • Sharhin bayan Labarai: Mahangar Iran Dangane Da Tattaunawa Kan Shirinta na Makamashin Nukliya Na Zaman lafiya
  • Aviator Game Craze in India: Why Everyone’s Talking About This High-Flying Trend!
  • Tattalin Arzikin Sin Tamkar Teku Ne Ba Karamin Tabki Ba
  • Iran Ta Bukaci Kasashen Turai Su Shiga Tattaunawar Nukliya Da Take Yi Da Amurka
  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Batun Samun Hadin Kai Tsakanin Al’ummar Kasar
  • Sharhin bayan Labarai: Ci Gaban Harkokin Kasuwanci Tsakanin Iran Da Kasashen Waje Duk Tare Da Takunkuman Kasashen Yamma