Kasar Indiya Ta Yi Luguden Makamai Masu Linzami Kan Kasar Pakistan
Published: 7th, May 2025 GMT
Gwamnatin kasar Indiya ta yi luguden makamai masu linzami kan kasar Pakistan, yayin da Pakistan ta sha alwashin mayar da martani
Gwamnatin Indiya ta kai hare-haren makamai masu linzami kan wasu wurare a kasar Pakistan da yammacin jiya Talata, kuma sojojin Pakistan sun sha alwashin mayar da martini, yayin da ake ci gaba da samun takun saka tsakanin kasashen biyu masu karfin nukiliya.
Gwamnatin Indiya ta kai hare-hare da makamai masu linzami guda uku kan wasu wurare a yankin Kashmir da Punjab na kasar Pakistan, yayin da daya daga cikin makaman ya afkawa tsohon filin jirgin sama na Muzaffarabad a yankin Kashmir da Pakistan ke iko da shi.
A nata bangaren, gwamnatin Indiya ta sanar da cewa ta kaddamar da wani farmaki kan abin da ta kira ababen more rayuwa na ‘yan ta’adda a Pakistan da Jammu da Kashmir, ta kuma ce sojojinta sun kai hare-hare kan wasu wurare 9 na Pakistan.
Indiya ta kara da cewa: Hare-haren sun fi mayar da hankali zuwa wasu wurare da aka tantance, kuma ba tare da nufin janyo wani tashin hankali ba, don haka ba a kai hare-haren kan wasu cibiyoyin sojin Pakistan ba.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Pakistan kai hare hare wasu wurare
এছাড়াও পড়ুন:
Yawan Kudin Da Aka Kashe Na Zamantakewa A Watan Agusta A Kasar Sin Ya Kai RMB Triliyan 3.97
Na hudu, an yi ta samu ci gaban sayayya sakamakon masu yawon bude ido daga ketare. Bisa ga manufar rage haraji lokacin barin kasa da kasar Sin ke gudanarwa, an shirya shirin “Sayayya a Sin” yadda ya kamata, wanda hakan ya canza fa’idar yawan baki daga ketare da suke yawon shakatawa a kasar zuwa habaka kudin da ake kashewa. (Bilkisu Xin)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp