Kasar Indiya Ta Yi Luguden Makamai Masu Linzami Kan Kasar Pakistan
Published: 7th, May 2025 GMT
Gwamnatin kasar Indiya ta yi luguden makamai masu linzami kan kasar Pakistan, yayin da Pakistan ta sha alwashin mayar da martani
Gwamnatin Indiya ta kai hare-haren makamai masu linzami kan wasu wurare a kasar Pakistan da yammacin jiya Talata, kuma sojojin Pakistan sun sha alwashin mayar da martini, yayin da ake ci gaba da samun takun saka tsakanin kasashen biyu masu karfin nukiliya.
Gwamnatin Indiya ta kai hare-hare da makamai masu linzami guda uku kan wasu wurare a yankin Kashmir da Punjab na kasar Pakistan, yayin da daya daga cikin makaman ya afkawa tsohon filin jirgin sama na Muzaffarabad a yankin Kashmir da Pakistan ke iko da shi.
A nata bangaren, gwamnatin Indiya ta sanar da cewa ta kaddamar da wani farmaki kan abin da ta kira ababen more rayuwa na ‘yan ta’adda a Pakistan da Jammu da Kashmir, ta kuma ce sojojinta sun kai hare-hare kan wasu wurare 9 na Pakistan.
Indiya ta kara da cewa: Hare-haren sun fi mayar da hankali zuwa wasu wurare da aka tantance, kuma ba tare da nufin janyo wani tashin hankali ba, don haka ba a kai hare-haren kan wasu cibiyoyin sojin Pakistan ba.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Pakistan kai hare hare wasu wurare
এছাড়াও পড়ুন:
Jami’an tsaro sun ƙwato makamai da kama mutane 398 a Kaduna
Tawagar jami’an tsaron haɗin gwaiwa ta musamman da Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani ya kafa domin yaƙi da ayyukan ’yan daba da sace-sacen waya a jihar, ta samu nasarar ƙwato makamai tare da cafke mutane 398 da ake zargi a wurare daban-daban.
Wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sanda (PPRO), DSP Hassan Mansir ne ya fitar, na bayyana cewa, an kai samamen ne cikin gaggawa tare da wasu sahihan bayanan sirri.
Wani ya kashe mahaifiyarsa mai shekara 71 a Akwa Ibom Yin sulhu da ’yan bindiga dabara ce ba gazawa ba — Gwamnatin SakkwatoSamamen ya sanya wasu da dama daga cikin masu aikata laifuka tserewa daga Jihar Kaduna saboda fargabar kama su.
Sanarwar ta kuma bayyana cewa, a cikin kwanaki tara na farko da rundunar take gudanar ayyukanta, ta kama wani mutum mai suna Mathew Adamu, wanda ya shahara wajen aikata ta’addancin cikin al’umma.
Sanarwar ta ce, rundunar ta ƙunshi rundunar ’yan sandan Najeriya ne a matsayin hukumar da ke jagorantar hukumar, tare da sojoji da Jami’an tsaron farin kaya DSS da Sibil defens da jami’an shige da fice na Najeriya da hukumar gyaran hali da hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi (NDLEA) da hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa (FRSC) da Hukumar Kwastam ta Najeriya, ciki har da hukumar ’yan banga ta Jihar Kaduna (KADVIS).
DSP Hassan ya bayyana cewa, an samu wata ƙaramar bindiga ƙirar gida daga hannun wani mutum mai suna Adamu Umar, wani fitaccen mai sayar da miyagun ƙwayoyi, wanda za a miƙa ƙararsa ga Hukumar NDLEA mai yaƙi da miyagun ƙwayoyi a Najeriya domin ci gaba da bincike da gurfanar da shi.