Kasar Indiya Ta Yi Luguden Makamai Masu Linzami Kan Kasar Pakistan
Published: 7th, May 2025 GMT
Gwamnatin kasar Indiya ta yi luguden makamai masu linzami kan kasar Pakistan, yayin da Pakistan ta sha alwashin mayar da martani
Gwamnatin Indiya ta kai hare-haren makamai masu linzami kan wasu wurare a kasar Pakistan da yammacin jiya Talata, kuma sojojin Pakistan sun sha alwashin mayar da martini, yayin da ake ci gaba da samun takun saka tsakanin kasashen biyu masu karfin nukiliya.
Gwamnatin Indiya ta kai hare-hare da makamai masu linzami guda uku kan wasu wurare a yankin Kashmir da Punjab na kasar Pakistan, yayin da daya daga cikin makaman ya afkawa tsohon filin jirgin sama na Muzaffarabad a yankin Kashmir da Pakistan ke iko da shi.
A nata bangaren, gwamnatin Indiya ta sanar da cewa ta kaddamar da wani farmaki kan abin da ta kira ababen more rayuwa na ‘yan ta’adda a Pakistan da Jammu da Kashmir, ta kuma ce sojojinta sun kai hare-hare kan wasu wurare 9 na Pakistan.
Indiya ta kara da cewa: Hare-haren sun fi mayar da hankali zuwa wasu wurare da aka tantance, kuma ba tare da nufin janyo wani tashin hankali ba, don haka ba a kai hare-haren kan wasu cibiyoyin sojin Pakistan ba.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Pakistan kai hare hare wasu wurare
এছাড়াও পড়ুন:
FG Za Ta Raba Naira miliyan 3.4m Ga Wadanda Suke Amfana Da Shirin ACReSAL
Gwamnatin tarayya ta ce tace a shirin ta sauya wuraren dake bushe a sassan arewacin Nijeriyaza a raba naira miliyan miliyan 3.4 kuma akasarin wadanda zasu amfana da wannan za su kasance mata ta hanyar Shirin ACReSAL.
Da yake jawabi a wajen bude taron kwanaki 10 na masu ruwa da tsaki kan tsarin kula da tsare-tsare (SCMP) na sabbin magudanan ruwa guda 11 a fadin Jihohi bakwai na tarayya a Ilorin, kodinetan ayyukan ACRESAL na kasa, Mista Abdulhamid Umar, ya ce za a gudanar da aikin ne ta hanyar shirin kawo sauyi na dogon lokaci.
Jami’in kula da ayyukan na kasa na ACRESAL Adamu Shettima wanda ya samu wakilcin kwararre a bangaren kula da ayyukan ruwa na gwamnatin tarayya, Adamu Shettima, ya bayyana cewa aikin yana da nasaba da dawo da martabar yankuna da suke bushe, daidaita yanayin muhalli da kuma karfafa miliyoyin al’umma a fadin Arewacin Najeriya.
Umar ya bayyana cewa bankin duniya ne ke taimaka wa aikin ta hannun kungiyar ci gaban kasa da kasa (IDA), ya kara da cewa wannan shi ne karon farko da gwamnatin tarayya ke samar da tsarin kula da ruwa mai girman irin wannan.
Ya yi nuni da cewa, dabarun da masu ruwa da tsaki za su mayar da hankali wajen yin mu’amala da masu ruwa da tsaki a dabarun da suka shafi Kwara, mai masaukin baki, Kaduna, Kebbi, Zamfara, Niger da FCT.
A nata jawabin, kwamishiniyar muhalli ta jihar Kwara, Hajia Nafisat Musa Buge, ta bayyana cewa hadakar masu ruwa da tsaki na daga cikin shirin inganta sha’anin ruwa, da inganta yanayin da ake ciki, da inganta rayuwa mai ɗorewa a yankunan da ke fama da wannan matsala a Najeriya.
Kwamishinan, ta ce sabon Shirin zai kasance ne tsakanin jihohi shida na Najeriya.
A nasa jawabin, Ko’odinetan shirin ACRESAL na jihar Kwara, Alhaji Shamsideen Aregbe, ya bukaci a hada kai da masu ruwa da tsaki wajen samar da tsare-tsare na kula da ruwan.
COV/ALI MUHAMMAD RABIU