Gwamnatin Sudan ta katse dangantakar diflomasiyya da (UAE), bisa zarginta da goyan bayan dakarun RSF.

A cikin jawabin da aka watsa a talabijin, Ministan Tsaron Sudan, Yassin Ibrahim ya bayyana cewa Sudan ta “katse dangantakar diflomasiyya da UAE,” tare da janye jakadanta da rufe ofishin jakadanci da konsulat dinta a kasar .

Da yake magana a gidan talabijin na gwamnatin kasa, ministan tsaron Sudan, Yassin Ibrahim Yassin, ya zargi Abu Dhabi da keta hurumin ‘yancin Sudan ta hanyar mara baya ta fuskar soji ga RSF, ciki har da samar da makamai, da jiragen yaki marasa matuka, da makamai masu linzami wadanda aka kai hari da su a baya-bayan nan a tashar jiragen ruwa, da filin jiragen sama, da kuma tashoshin wutar lantarki na Sudan.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ansarullah: Yarjejeniya da Amurka ba za ta dakatar da hare-haren da Yemen ke kaiwa Isra’ila ba

Kungiyar gwagwarmaya ta Ansarullah ta bayyana cewa yarjejeniyar tsagaiat wutar da ta cimma da Amurka, ba ta sauya matsayin kasar ba na kai wa Isra’ila hari.

Kakakin kungiyar Ansarullah Mohammed Abdul-Salam ya jaddada cewa Dakarun Yeman za su ci gaba da kai hare-hare kan Isra’ila domin goyan bayan Falasdinawa a zirin Gaza.

Yarjejeniyar da Amurka ba ta da alaka da matsayinmu na goyan bayan Gaza, inji Abdul-Salam.

A jiya ne masarautar Oman ta sanar cewa Amurka da kungiyar Ansarullah da aka fi sani da ta ‘yan Houtshis a Yeman suka cimma yarjejeniyar tsagaita wuta.

Ma’aikatar harkokin wajen kasar Oman ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ta fitar cewa: Bayan tattaunawa da tuntubar juna da aka yi a baya-bayan nan da kuma tuntubar juna tsakanin masarautar Oman ta Amurka da hukumomin da abin ya shafa a birnin Sana’a na jamhuriyar Yeman, an samu cimma yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin bangarorin biyu.

Sanarwar ta kara da cewa: A nan gaba, ko wanne bangare ba zai kai hari kan daya ba, ciki har da jiragen ruwan Amurka a tekun Bahar Rum da Bab al-Mandab, domin tabbatar da ‘yancin zirga-zirgar jiragen ruwa da kuma tafiyar da harkokin kasuwancin kasa da kasa cikin sauki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ansarullah: Yarjejeniya da Amurka ba za ta dakatar da hare-haren da Yemen ke kaiwa Isra’ila ba
  • Sudan ta katse dangantakar diflomasiyya da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa
  • Kasar Sudan Ta Yanke Huldar Jakadancinta Da Kasar Hadaddiyar Daular Larabawa
  • AU, ta yi tir da harin baya bayan nan a tashar ruwan Sudan
  • Tarayyar Turai: Muna Goyon Bayan Warware Batun Nukiliyar Iran Ta Hanyar Diplomasiyya
  •  Kotun Duniya Ta Wanke HDL Akan Zargin Kisan Kiyashi A Sudan
  • Yau Kotun ICJ ke yanke hukunci kan zargin da Khartoum ke wa UEA
  • Iran Ta Jaddada Cewa: Kungiyoyin Gwagwarmaya Ba Su Karbar Umarni Daga Wani Bangare, Gashin Kansu Suke Ci
  • Sojojin Sudan Da ‘Yan Tawayen Kasar Suna Ci Gaba Da Gwabza Fada A Wasu Saasan Kasar