Sudan ta katse hulda da Hadaddiyar Daular Larabawa bisa goyon bayan dakarun RSF
Published: 7th, May 2025 GMT
Gwamnatin Sudan ta katse dangantakar diflomasiyya da (UAE), bisa zarginta da goyan bayan dakarun RSF.
A cikin jawabin da aka watsa a talabijin, Ministan Tsaron Sudan, Yassin Ibrahim ya bayyana cewa Sudan ta “katse dangantakar diflomasiyya da UAE,” tare da janye jakadanta da rufe ofishin jakadanci da konsulat dinta a kasar .
Da yake magana a gidan talabijin na gwamnatin kasa, ministan tsaron Sudan, Yassin Ibrahim Yassin, ya zargi Abu Dhabi da keta hurumin ‘yancin Sudan ta hanyar mara baya ta fuskar soji ga RSF, ciki har da samar da makamai, da jiragen yaki marasa matuka, da makamai masu linzami wadanda aka kai hari da su a baya-bayan nan a tashar jiragen ruwa, da filin jiragen sama, da kuma tashoshin wutar lantarki na Sudan.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An yi wa sojoji ɗaurin rai da rai kan sayar wa ’yan ta’adda makamai a Borno
Wata Kotun Soji ta yanke wa wasu sojoji uku hukuncin ɗaurin rai da rai kan sayar da makamai da harsasai ba bisa ka’ida ba a Maiduguri, Jihar Borno.
Kotun sojin ƙarƙashin jagorancin Birgediya-Janar Mohammed Abdullahi, ta bayyana cewa an yanke wa mutum uku daga cikin sojojin huɗu hukuncin ɗaurin rai da rai yayin da aka ɗaure mutum ɗaya shekaru 15 a gidan yari.
Sanata Natasha ta koma Majalisar Dattawa Yarima Salman ya jagoranci jana’izar babban mai ba da fatawa na SaudiyyaSojojin da abin ya shafa sun haɗa da Raphael Ameh da Ejiga Musa masu muƙamin sajan, da kuma Patrick Ocheje mai muƙamin kofura.
Binciken kotun ya nuna cewa Ameh ya karɓi sama da ₦500,000 daga harƙallar sayar da harsasai kafin daga bisani a kama shi yana ƙoƙarin sayar da wasu ƙarin makaman.
Da yake yanke hukunci, Janar Abdullahi ya bayyana su a matsayin “ƙwayaye bara-gurbi” da suka ci amanar rundunar soji, suka karya ƙa’idar ladabi da biyayya, tare da wulaƙanta mutuncin da ake tsammani daga jami’an soja a yaƙin da ake yi da ta’addanci.
Bayanai sun ce wannan hukuncin na zuwa ne bayan amincewar su kan aikata laifuffukan da suka haɗa da “sata da cinikin makamai ba bisa ka’ida ba, da taimaka wa maƙiya” wanda duka laifuka ne ƙarƙashin dokar sojojin Najeriya.
Kotun ta bayyana cewa “irin wannan safarar da ba bisa ƙa’ida ba na zama haɗari ga sojoji da ayyukansu, da kuma tsaron ƙasa, don haka yana nufin taimaka wa maƙiyan ƙasar.”
Shugaban Kotun, Brigadier Janar Abdullahi, ya ce waɗannan laifuka da sojojin suka aikata ba matsala ce kawai ta karya doka ba, har ma da cin amana, da martabar da ake sa ran sojoji su riƙe.
Rundunar sojin Najeriya ta bayyana cewa ba za ta lamunci irin waɗannan rashin ɗa’a da halayen damfara ko rashin ƙwarewa ba.
Babu shakka Jihar Borno ce cibiyar rikicin Boko Haram a Najeriya wadda ta kwashe kimanin shekara 15 tana fama da shi, lamarin da ya laƙume rayukan dubban mutane da haifar da matsalar jin-ƙai.