Sudan ta katse dangantakar diflomasiyya da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa
Published: 7th, May 2025 GMT
Gwamnatin Sudan da ke da goyon bayan sojoji ta katse dangantakar diflomasiyya da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE), tana bayyana ƙasar a matsayin mai katsalandan, a cewar Ministan Tsaron Sudan, Yassin Ibrahim.
A cikin jawabin da aka watsa a talabijin ranar Talata, Ibrahim ya bayyana cewa Sudan ta “katse dangantakar diflomasiyya da UAE,” tare da janye jakadanta da rufe ofishin jakadanci da konsulat ɗinta a ƙasar Gulf ɗin.
Ya zargi UAE da take hurumin Sudan ta hanyar “ƙawarta”, wato Rundunar RSF, wacce ke yaƙi da sojojin Sudan tun watan Afrilu 2023.
“Dukkan duniya ta shaida, fiye da shekaru biyu, laifin kai hari kan hurumin Sudan, cikakken yankinta da kuma tsaron ‘yan ƙasarta da UAE ke yi ta hanyar ƙawarta ta cikin gida, wato ƙungiyar ‘yan ta’adda ta RSF,” in ji ministan.
Gwamnatin Sudan ta sha zargin UAE da samar wa RSF makamai — zarge-zargen da Abu Dhabi ya musanta.
Matakin da gwamnatin Sudan ta ɗauka ya biyo bayan harin jirage marasa matuƙa a Port Sudan — wanda yanzu ya zama babban birnin ƙasar na wucin gadi — wanda aka kai har sau uku a jere.
Ibrahim ya ce UAE ta ƙara tsananta shiga cikin rikicin ta hanyar samar wa RSF “makamai masu ci gaba na zamani” bayan nasarorin da sojojin Sudan suka samu a filin daga, inda suka sake karɓe iko da babban birnin Khartoum a watan Maris.
Ya ƙara da cewa Sudan za ta “mayar da martani ga wannan hari ta kowace hanya da ta dace don kare hurumin ƙasar” da kuma “kare fararen hula.”
Yaƙin da ya yi sanadin mace-maceYaƙin da ke gudana a Sudan ya kashe dubban mutane, ya raba mutane miliyan 13 da muhallansu, kuma ya haifar da babbar matsalar gudun hijira da yunwa a duniya.
Rikicin ya raba ƙasar gida biyu, inda sojojin ke iko da arewa, gabas da tsakiyar ƙasar, yayin da RSF ke mamaye mafi yawan yankin Darfur na yamma da wasu sassan kudu.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Groosi: Masu Binciken Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Suna Hanyar Zuwa Iran
Babban daraktan hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa ya sanar da cewa: Masu binciken hukumarsa suna kan hanyarsu ta zuwa Iran
Babban daraktan hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa Rafael Grossi ya bayyana cewa: Masu sa ido na hukumar IAEA na kan hanyarsu ta zuwa Iran.
Rafael Grossi ya bayyana cewa: Masu sa ido na hukumar kula da makamashin nukiliya ta IAEA na kan hanyarsu ta zuwa Iran, amma shigarsu ta dogara ne da manufofin siyasar Iran.
Ya ce: “Damar da suke da shi tana da kunci sosai, don haka tawagar hukumar IAEA tana da ‘yan sa’o’i kadan ko ‘yan kwanaki don sanin ko yarjejeniya da bangarorin biyu suka rattaba hannu a kai za ta yiwu, kuma wannan ita ce hanyar da dukan bangarorin biyu suke nema.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kasashen Afirka Uku Sun Sanar Da Ficewa Daga Kotun Hukunta Manyan Laifuka Ta Duniya September 24, 2025 Imam Khamenei Zai Yi Jawabi Ga mutanen Iran A Cikin Makon Tsaro Da Ya Shigo September 23, 2025 Lebanon: A yau Ne Aka Yi Jana’izar Shahidan Bitij Bail Wadanda HKI Ta Kai Ga Shahada A Ranar Lahadi September 23, 2025 Pezeshkiyan Ya Ce Tattaunawa Da Kasashe Masu Nuna Karfi Kan Wasu Ba Zai Taba Yi Yuwa Ba September 23, 2025 Sauye-Sauyen Siriya A hannun Amurka Da Aika’ida September 23, 2025 Jakadan Amurka Ya Amince Da Cewa Amurka Tana Nufin Hada Yaki Tsakanin Sojojin Lebanon Da Hizbullah September 23, 2025 ‘Yan Gwagwarmaya Sun Kashe Sojojin Mamaya Biyu A Wani Kwanton Bauna A Arewacin Gaza September 23, 2025 Kasar Afirka Ta Kudu Ta Jaddada Yin Kiran A Bai Wa Falasdinawa Kasarsu September 23, 2025 HKI Tana Ci Gaba Da Yi Wa Mutanen Gaza Kisan Kiyashi September 23, 2025 Nato Na Yin Taron Tattaunawa Keta Hurumin Samaniyar Kasar Estonia Da Rasha Ta Yi September 23, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci