Aminiya:
2025-08-06@22:12:44 GMT

Sudan ta katse dangantakar diflomasiyya da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa

Published: 7th, May 2025 GMT

Gwamnatin Sudan da ke da goyon bayan sojoji ta katse dangantakar diflomasiyya da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE), tana bayyana ƙasar a matsayin mai katsalandan, a cewar Ministan Tsaron Sudan, Yassin Ibrahim.

A cikin jawabin da aka watsa a talabijin ranar Talata, Ibrahim ya bayyana cewa Sudan ta “katse dangantakar diflomasiyya da UAE,” tare da janye jakadanta da rufe ofishin jakadanci da konsulat ɗinta a ƙasar Gulf ɗin.

Dalilin faɗuwar ɗalibai a jarabawar JAMB bana — Ministan Ilimi Inter Milan ta kori Barcelona daga Gasar Zakarun Turai

Ya zargi UAE da take hurumin Sudan ta hanyar “ƙawarta”, wato Rundunar RSF, wacce ke yaƙi da sojojin Sudan tun watan Afrilu 2023.

“Dukkan duniya ta shaida, fiye da shekaru biyu, laifin kai hari kan hurumin Sudan, cikakken yankinta da kuma tsaron ‘yan ƙasarta da UAE ke yi ta hanyar ƙawarta ta cikin gida, wato ƙungiyar ‘yan ta’adda ta RSF,” in ji ministan.

Gwamnatin Sudan ta sha zargin UAE da samar wa RSF makamai — zarge-zargen da Abu Dhabi ya musanta.

Matakin da gwamnatin Sudan ta ɗauka ya biyo bayan harin jirage marasa matuƙa a Port Sudan — wanda yanzu ya zama babban birnin ƙasar na wucin gadi — wanda aka kai har sau uku a jere.

Ibrahim ya ce UAE ta ƙara tsananta shiga cikin rikicin ta hanyar samar wa RSF “makamai masu ci gaba na zamani” bayan nasarorin da sojojin Sudan suka samu a filin daga, inda suka sake karɓe iko da babban birnin Khartoum a watan Maris.

Ya ƙara da cewa Sudan za ta “mayar da martani ga wannan hari ta kowace hanya da ta dace don kare hurumin ƙasar” da kuma “kare fararen hula.”

Yaƙin da ya yi sanadin mace-mace

Yaƙin da ke gudana a Sudan ya kashe dubban mutane, ya raba mutane miliyan 13 da muhallansu, kuma ya haifar da babbar matsalar gudun hijira da yunwa a duniya.

Rikicin ya raba ƙasar gida biyu, inda sojojin ke iko da arewa, gabas da tsakiyar ƙasar, yayin da RSF ke mamaye mafi yawan yankin Darfur na yamma da wasu sassan kudu.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

An sace jaririya sa’o’i kaɗan bayan haihuwarta a asibitin Ekiti

An nemi wata jaririya sa’o’i kaɗan bayan haihuwarta an rasa a Cibiyar Lafiya ta Okeyinmi da ke Ado-Ekiti, babban birnin Jihar Ekiti, a ranar Litinin.

Wani ganau ya ce an gano ɓatan jaririyar ne lokacin da ma’aikatan jinyar da ke bakin aiki suka je su duba lafiyarta da safiyar wannan Litinin ɗin.

Za a samu ruwan sama kamar da bakin ƙwarya na kwanaki uku a faɗin Nijeriya — NiMet Shirin kashe N712bn kan gyaran filin jirgin Legas ya tayar da ƙura

Lamarin na ba-zato-ba-tsammani ya haifar da fargaba musamman yadda ɗimauta uwar jaririyar da kuma wasu daga cikin mutanen da ke cikin harabar asibitin.

Tuni dai an garzaya da ma’aikatan da ke kula da ɗakin haihuwa da uwar jaririyar da mai gadi da wasu da ake zargi zuwa ofishin ’yan sanda domin ci gaba da bincike.

Aminiya ta ruwaito cewa wasu masu neman na abinci a kusa da asibitin sun shiga ɗimuwa matuƙa dangane da faruwar lamarin.

Mai magana da yawun rundunar ’yan sanda na jihar, SP Sunday Abutu, ya ce yanzu haka akwai mutum huɗu da ake zargi da suka shiga hannu, “kuma suna bayar da bayanai masu amfani da za su taimaka a binciken.”

Abutu ya ce Kwamishinan ‘yan sanda na jihar, Mista Joseph Eribo, ya umurci sashen bincike na musamman (CID) da su gudanar da cikakken bincike domin tabbatar da dawo da jaririyar cikin ƙoshin lafiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dakarun Kai Daukin Gaggawa Na Sudan Sun Kashe Fararen Hula 14 Tare Da Jikkata Wasu Na Daban
  • Ministocin Ghana biyu sun rasu a hatsarin jirgin sama
  • Ministan tsaron Ghana da wasu sun rasu a hatsarin jirgin sama
  • Hatsarin Mota: Yadda hanyar Lambata ke laƙume rayuka a Neja
  • Malaman Jami’o’in Isra’ila Sun Nemi Jamus Ta Tilasta Dakatar Da Yakin Gaza
  • An sace jaririya sa’o’i kaɗan bayan haihuwarta a asibitin Ekiti
  • Za a samu ruwan sama kamar da bakin ƙwarya na kwanaki uku a faɗin Nijeriya — NiMet
  • Sojojin Isra’ila Sun Kashe Falasɗinawa A Wurin Rabon Abinci A Gaza
  • Gwamnan Neja Ya Bada Umarnin Sake Bude Jami’ar Ibrahim Badamasi Babangida, Lapai.
  • Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara Ta Kai Ziyara Ta Ta’aziyya Ga Sabon Sarkin Gusau