Sudan ta katse dangantakar diflomasiyya da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa
Published: 7th, May 2025 GMT
Gwamnatin Sudan da ke da goyon bayan sojoji ta katse dangantakar diflomasiyya da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE), tana bayyana ƙasar a matsayin mai katsalandan, a cewar Ministan Tsaron Sudan, Yassin Ibrahim.
A cikin jawabin da aka watsa a talabijin ranar Talata, Ibrahim ya bayyana cewa Sudan ta “katse dangantakar diflomasiyya da UAE,” tare da janye jakadanta da rufe ofishin jakadanci da konsulat ɗinta a ƙasar Gulf ɗin.
Ya zargi UAE da take hurumin Sudan ta hanyar “ƙawarta”, wato Rundunar RSF, wacce ke yaƙi da sojojin Sudan tun watan Afrilu 2023.
“Dukkan duniya ta shaida, fiye da shekaru biyu, laifin kai hari kan hurumin Sudan, cikakken yankinta da kuma tsaron ‘yan ƙasarta da UAE ke yi ta hanyar ƙawarta ta cikin gida, wato ƙungiyar ‘yan ta’adda ta RSF,” in ji ministan.
Gwamnatin Sudan ta sha zargin UAE da samar wa RSF makamai — zarge-zargen da Abu Dhabi ya musanta.
Matakin da gwamnatin Sudan ta ɗauka ya biyo bayan harin jirage marasa matuƙa a Port Sudan — wanda yanzu ya zama babban birnin ƙasar na wucin gadi — wanda aka kai har sau uku a jere.
Ibrahim ya ce UAE ta ƙara tsananta shiga cikin rikicin ta hanyar samar wa RSF “makamai masu ci gaba na zamani” bayan nasarorin da sojojin Sudan suka samu a filin daga, inda suka sake karɓe iko da babban birnin Khartoum a watan Maris.
Ya ƙara da cewa Sudan za ta “mayar da martani ga wannan hari ta kowace hanya da ta dace don kare hurumin ƙasar” da kuma “kare fararen hula.”
Yaƙin da ya yi sanadin mace-maceYaƙin da ke gudana a Sudan ya kashe dubban mutane, ya raba mutane miliyan 13 da muhallansu, kuma ya haifar da babbar matsalar gudun hijira da yunwa a duniya.
Rikicin ya raba ƙasar gida biyu, inda sojojin ke iko da arewa, gabas da tsakiyar ƙasar, yayin da RSF ke mamaye mafi yawan yankin Darfur na yamma da wasu sassan kudu.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Atiku Da Wasu Sun Kafa Sabuwar Jam’iyya, Sun Nemi INEC Ta Musu Rajista
A cikin takardar, ƙungiyar ta bayyana cewa ta yanke shawarar kafa sabuwar jam’iyya maimakon haɗaka da wasu.
Sun bayyana cewa sun zaɓi suna All Democratic Alliance (ADA) kuma taken jam’iyyar shi ne “Justice for All” wato “Adalci ga Kowa.”
Sun kuma haɗa da adireshin babban ofishin jam’iyyar a cikin takardar.
Sun gabatar da wasu muhimman takardu da suka haɗa da tambarin jam’iyya, tsarin kundin mulki, tutar jam’iyyar, da manufofinta.
Tambarin jam’iyyar ya ƙunshi kayan hatsi irin su masara da launuka masu ma’ana.
Kundin tsarin mulki kuma ya ƙunshi manufofi, tsari da dokokin jam’iyyar, bisa ga tsarin dokokin Najeriya da ƙa’idar dimokuraɗiyya ta duniya.
Takardar ta ƙare da girmamawa, inda ta ke roƙon INEC da ta ɗauki mataki na gaba wajen kammala rijistar jam’iyyar.
Sauran manyan ‘yan siyasa da ke cikin wannan haɗaka sun haɗa da Tsohon Gwamnan Jihar Ribas, Rotimi Amaechi, Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa David Mark, da Dakta Umar Ardo, wanda ya kafa ƙungiyar League of Northern Democrats.
A baya, ƙungiyar ta yi la’akari da shiga wata jam’iyya, kamar African Democratic Congress (ADC) da Social Democratic Party (SDP).
Sai dai daga sun fasa bayan sun lura da rikice-rikicen cikin gida da shari’o’i da waɗannan jam’iyyu ke fuskanta.
Saboda haka, suka zaɓi kafa sabuwar jam’iyya da za su fara daga tushe tare da daidaita tsakanin mambobinta.
Yanzu suna jiran matakin da INEC za ta ɗauka yayin da suke shirin tunkarar zaɓen 2027.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp