Ansarullah: Yarjejeniya da Amurka ba za ta dakatar da hare-haren da Yemen ke kaiwa Isra’ila ba
Published: 7th, May 2025 GMT
Kungiyar gwagwarmaya ta Ansarullah ta bayyana cewa yarjejeniyar tsagaiat wutar da ta cimma da Amurka, ba ta sauya matsayin kasar ba na kai wa Isra’ila hari.
Kakakin kungiyar Ansarullah Mohammed Abdul-Salam ya jaddada cewa Dakarun Yeman za su ci gaba da kai hare-hare kan Isra’ila domin goyan bayan Falasdinawa a zirin Gaza.
Yarjejeniyar da Amurka ba ta da alaka da matsayinmu na goyan bayan Gaza, inji Abdul-Salam.
A jiya ne masarautar Oman ta sanar cewa Amurka da kungiyar Ansarullah da aka fi sani da ta ‘yan Houtshis a Yeman suka cimma yarjejeniyar tsagaita wuta.
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Oman ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ta fitar cewa: Bayan tattaunawa da tuntubar juna da aka yi a baya-bayan nan da kuma tuntubar juna tsakanin masarautar Oman ta Amurka da hukumomin da abin ya shafa a birnin Sana’a na jamhuriyar Yeman, an samu cimma yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin bangarorin biyu.
Sanarwar ta kara da cewa: A nan gaba, ko wanne bangare ba zai kai hari kan daya ba, ciki har da jiragen ruwan Amurka a tekun Bahar Rum da Bab al-Mandab, domin tabbatar da ‘yancin zirga-zirgar jiragen ruwa da kuma tafiyar da harkokin kasuwancin kasa da kasa cikin sauki.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
2027: ‘Sai bayan babban taron APC Tinubu zai bayyana wanda za su yi takara tare’
Fadar Shugaban Kasa ta ce shugaba Bola Tinubu zai zabi wanda zai yi masa takarar mataimaki a zaben 2027 a hukumance ne kawai bayan a kammala babban taron jam’iyyar APC a 2026.
Kakakin shugaban, Bayo Onanuga ne ya bayyana hakan yayin wata tattaunawarsa da jaridar Daily Trust a ranar Alhamis.
Da yake martani kan dalilin da ya sa fadar shugaban ta yi shiru kan zargin cewa Tinubu na son canza mataimaki a 2027 musamman la’akari da yadda ’yan jam’iyyar ke ta nuna goyon bayansu ga shugaban shi kadai, Onanuga ya ce hakan ba gaskiya ba ne.
Nan da mako biyu za mu yanke shawara kan shigar wa Isra’ila yaƙi — Trump Muna shawartar Trump kada ya shiga yaƙin Iran da Isra’ila — BirtaniyaA cewarsa, “Lokacin da na karanta labarin, na karyata shi saboda ba shi da tushe. A tsarin shugaba mai cikakken iko da Najeriya ke bi, dan takarar shugaban kasa ake fara zaba, shi kuma sai ya zabi wanda zai yi masa mataimaki. Abin da ya faru ke nan a lokacin Buhari – an fara zabensa, sai daga baya shi kuma ya dauki mataimaki. Ba a yin duka biyun a lokaci daya.
“Da zarar INEC ta fitar da jadawalin zabuka, jam’iyya za ta shirya babban taronta, idan aka sake tsayar da shugaban kasa, shi kuma zai zabi mataimakinsa,” in ji Onanuga.
Kazalika, ya kuma yi fatali da tarihin da ake daukowa cewa sau biyu tinubu yana canza mataimaka lokacin da ya yi Gwamna a jihar Legas daga 1999 zuwa 2007, cewa irin haka za ta faru da Kashim Shettima a 2027.
Ya kuma ce jita-jitar da ake yadawa a kan yiwuwar canza Shettima tun ma kafin a fara nuna amincewa da sake takarar Tinubu ba ta da tushe.
Ya ce, “Ba ni da masaniya a kan duk wani sabani tsakanin shugaban kasa da mataimakinsa. Iya abin da na sani shi ne akwai kyakkyawar fahimtar juna da alakar aiki mai kyau a tsakaninsu. Duk maganganun da ake yadawa ba su da maraba da na teburin mai shayi. Mutane na ta fadara maganganun rashin kan gado cewa wai Seyi Tinubu ne ma mataimakin shugaban kasa. Wannan shashanci ne.
“A wannan kasar, mukamin mataimaka ko na gwamna ko na shugaban kasa ba a raba su da ’yan tsegungumin mutane. Ko da ana zaune lafiya babu wata matsala, makunsantansu sai sun kirkiri husuma da labaran karya. Amma iya abin da na sani shi ne babu matsala tsakanin Tinubu da Shettima.