Lakurawa sun kashe ’yan bijilanti 11 a Sakkwato
Published: 4th, May 2025 GMT
Wasu ’yan bindiga da ake fargabar mayaƙan Lakurawa ne sun kashe wasu ’yan bijilanti da ke aikin sintiri a Jihar Sakkwato.
Aminiya ta ruwaito cewa lamarin ya faru ne a ranar Juma’ar da ta gabata bayan musayar wuta da mayaƙan suka yi da ’yan sintiri a Ƙaramar Hukumar Tangaza a jihar ta Sakkwato.
Ya kamata a zuba jari a harkar noman rani — Zulum Wa zai cire wa Real Madrid kitse a wuta?Bayanai sun ce kawo yanzu akwai ragowar gawawwakin ’yan bijilantin da ke hannun Lakurawan a dajin da suka yi sansani.
Sai dai wakilinmu ya ruwaito cewa rundunar soji na ƙoƙarin ƙwato gawawwakin a dajin Binji da Raka.
Shaidu sun ce tun da farko lamarin ya faru ne yayin da ’yan sintirin suka yi ƙoƙarin hana ’yan bindigar shiga ƙauyen Magonho domin kai hari.
Wannan ce ta sanya aka soma musayar wuta tsakanin ɓangarorin biyu, lamarin da ya kai ga salwantar rayukan ’yan bijilantin.
Rahotanni na cewa ’yan bindigar aƙalla 40 haye a kan babura 20 ne suka kai harin da nufin satar dabbobi kafin a ci ƙarfinsu su tsre.
“Sun kashe mana mutane 11 sun kwashi wasu gawar namu sun tafi da su domin wulaƙanci, zuwa yanzu ba za a ce ga yawan mutanen da suka tafi da su.”
Sai dai sojojin da suka yi sansani a yankin sun kawo ɗauki, inda suka yi nasarar ƙwato wasu dabbobni hannunsu.
Kazalika, daga bisani ’yan bindigar sun koma ƙauyen Magonho inda suka tarwatsa turakun sadarwa na kamfanin MTN.
Aminiya ta yi ƙoƙarin jin ta bakin jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan Jihar Sakkwato, DSP Rufa’i Ahmad, amma lamarin ya ci tura har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan sintiri Lakurawa Sakkwato
এছাড়াও পড়ুন:
Boko Haram ta kashe sojoji 4 a Yobe
Rahotonni na cewa mayaƙan Boko Haram sun kai kashe dakaru huɗu yayin wani hari da suka kai sansanin soji a Jihar Yobe.
Aminiya ta ruwaito cewa ’yan bindigar sun ƙaddamar da hari kan sansanin soji na “27 Task Force Brigade” da ke garin Buni Yadi, a yankin Ƙaramar Hukumar Gujba da tsakar daren Asabar.
Abin da ya hana ni cika alƙawarin da na yi wa ma’aikata — Gwamnan Sakkwato Lakurawa sun kashe ’yan bijilanti 11 a SakkwatoHarin na zuwa ne kwana guda bayan Ƙungiyar Gwamnonin Arewa maso Gabashin ƙasar sun gudanar da taro a Damaturu, babban birnin jihar da nufin magance matsalolin yankin, ciki har da matsalar tsaro.
A baya-bayan nan mayaƙan Boko Haram da na ISWAP na neman dawo da hare-hare a yankin.
A cikin makon nan ma ƙungiyar ISWAP ta ɗauki alhakin wani hari da yayi sanadin mutuwar mutum 26 a Jihar Borno.
Ko makonni biyu da suka gabata sai da mayaƙan Boko Haram suka kai hari sansanin soji da ke yankin Chalie a Ƙaramar Hukumar Buni Yadi, inda suka kashe dakaru uku.
Sai dai a bayan nan ne Shugaba Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa za ta ƙwato dazukan Arewa da ma sauran sassan ƙasar daga hannun masu garkuwa mtane domin karɓar kuɗin fansa da ‘yan ta’adda