Aminiya:
2025-06-20@17:12:56 GMT

Lakurawa sun kashe ’yan bijilanti 11 a Sakkwato

Published: 4th, May 2025 GMT

Wasu ’yan bindiga da ake fargabar mayaƙan Lakurawa ne sun kashe wasu ’yan bijilanti da ke aikin sintiri a Jihar Sakkwato.

Aminiya ta ruwaito cewa lamarin ya faru ne a ranar Juma’ar da ta gabata bayan musayar wuta da mayaƙan suka yi da ’yan sintiri a Ƙaramar Hukumar Tangaza a jihar ta Sakkwato.

Ya kamata a zuba jari a harkar noman rani — Zulum Wa zai cire wa Real Madrid kitse a wuta?

Bayanai sun ce kawo yanzu akwai ragowar gawawwakin ’yan bijilantin da ke hannun Lakurawan a dajin da suka yi sansani.

Sai dai wakilinmu ya ruwaito cewa rundunar soji na ƙoƙarin ƙwato gawawwakin a dajin Binji da Raka.

Shaidu sun ce tun da farko lamarin ya faru ne yayin da ’yan sintirin suka yi ƙoƙarin hana ’yan bindigar shiga ƙauyen Magonho domin kai hari.

Wannan ce ta sanya aka soma musayar wuta tsakanin ɓangarorin biyu, lamarin da ya kai ga salwantar rayukan ’yan bijilantin.

Rahotanni na cewa ’yan bindigar aƙalla 40 haye a kan babura 20 ne suka kai harin da nufin satar dabbobi kafin a ci ƙarfinsu su tsre.

“Sun kashe mana mutane 11 sun kwashi wasu gawar namu sun tafi da su domin wulaƙanci, zuwa yanzu ba za a ce ga yawan mutanen da suka tafi da su.”

Sai dai sojojin da suka yi sansani a yankin sun kawo ɗauki, inda suka yi nasarar ƙwato wasu dabbobni hannunsu.

Kazalika, daga bisani ’yan bindigar sun koma ƙauyen Magonho inda suka tarwatsa turakun sadarwa na kamfanin MTN.

Aminiya ta yi ƙoƙarin jin ta bakin jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan Jihar Sakkwato, DSP Rufa’i Ahmad, amma lamarin ya ci tura har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan sintiri Lakurawa Sakkwato

এছাড়াও পড়ুন:

Wani ya kashe mahaifiyarsa mai shekara 71 a Akwa Ibom

Rundunar ’yan sandan Jihar Akwa Ibom ta kama wani mutum mai suna Alexander Peter bisa zarginsa da kashe mahaifiyarsa mai suna Madam Atiny Peter mai shekara 71 da adda.

Lamarin ya faru ne a ƙauyen Ikot Inyang da ke ƙaramar hukumar Oruk Anam a Jihar Akwa Ibom.

Yin sulhu da ’yan bindiga dabara ce ba gazawa ba — Gwamnatin Sakkwato Katolika ta horar da shugabannin al’umma da na addini kan zaman lafiya

Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Baba Mohammed Azare ne ya tabbatar da kamen a yayin ganawa da manema labarai a ranar Alhamis, a hedikwatar ’yan sanda da ke Ikot Akpan Abia, a Uyo.

Kwamishinan ’yan sandan ya bayyana cewa, an kama wanda ake zargin Alexander ne a ranar 10 ga watan Yuni, kuma a halin yanzu ana ci gaba da gudanar da bincike don gano musabbabin wannan ɗanyen aikin.

“Mummunan lamarin ya faru ne a ƙauyen Ikot Inyang da ke ƙaramar hukumar Oruk Anam, inda rahotanni suka ce wanda ake zargin ya yi amfani da adda ne wajen yi wa mahaifiyarsa kisan gillar,” in ji Kwamishinan, inda ya ce rundunar ’yan sandan na ƙoƙarin bankaɗo lamarin tare da gano musabbabin wannan aika-aika.

Kwamishinan ya kuma bayyana cewa, an kama mutane 54 da ake zargi a faɗin jihar a cikin makonni shidan da suka gabata bisa aikata laifuka daban-daban.

Bugu da ƙari, rundunar ta ƙwato makamai da alburusai sama da 50 a wannan lokacin.

Kisan ya haifar da damuwa a cikin al’ummar yankin, inda mazauna yankin suka kaɗu matuƙa game da kisan da ɗan tsohuwar ya yi wa mahaifiyarsa da hannunsa.

‘Yan sanda sun ce za a samu ƙarin bayani yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike.

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wani ya kashe mahaifiyarsa mai shekara 71 a Akwa Ibom
  • Yin sulhu da ’yan bindiga dabara ce ba gazawa ba — Gwamnatin Sakkwato
  • Rikicin Filato: An sake kashe mutum 17 a Mangu da Bokkos
  • Majalisa Na Binciken Yadda Aka Kashe Naira Tiriliyan 1.12 Na Tallafin Manoma
  • An Kashe ‘Yan Ta’adda 6,260, An Ceto Mutane 5,365 Acikin Shekaru Biyu – Hedikwatar Tsaro 
  • Lakurawa Sun Sanya Dokar Hana Sayar Da Shanu A Kebbi
  • ’Yan bindiga sun kashe manoma 24 a Katsina
  • Sojojin Nijeriya sun kashe gomman ’yan ta’adda a Tafkin Chadi
  • Mun shirya yin sulhu da ’yan bindiga — Gwamnatin Sakkwato
  • Amurka na iya kashe jagoran addini na Iran don mun san inda yake — Trump