Lakurawa sun kashe ’yan bijilanti 11 a Sakkwato
Published: 4th, May 2025 GMT
Wasu ’yan bindiga da ake fargabar mayaƙan Lakurawa ne sun kashe wasu ’yan bijilanti da ke aikin sintiri a Jihar Sakkwato.
Aminiya ta ruwaito cewa lamarin ya faru ne a ranar Juma’ar da ta gabata bayan musayar wuta da mayaƙan suka yi da ’yan sintiri a Ƙaramar Hukumar Tangaza a jihar ta Sakkwato.
Ya kamata a zuba jari a harkar noman rani — Zulum Wa zai cire wa Real Madrid kitse a wuta?Bayanai sun ce kawo yanzu akwai ragowar gawawwakin ’yan bijilantin da ke hannun Lakurawan a dajin da suka yi sansani.
Sai dai wakilinmu ya ruwaito cewa rundunar soji na ƙoƙarin ƙwato gawawwakin a dajin Binji da Raka.
Shaidu sun ce tun da farko lamarin ya faru ne yayin da ’yan sintirin suka yi ƙoƙarin hana ’yan bindigar shiga ƙauyen Magonho domin kai hari.
Wannan ce ta sanya aka soma musayar wuta tsakanin ɓangarorin biyu, lamarin da ya kai ga salwantar rayukan ’yan bijilantin.
Rahotanni na cewa ’yan bindigar aƙalla 40 haye a kan babura 20 ne suka kai harin da nufin satar dabbobi kafin a ci ƙarfinsu su tsre.
“Sun kashe mana mutane 11 sun kwashi wasu gawar namu sun tafi da su domin wulaƙanci, zuwa yanzu ba za a ce ga yawan mutanen da suka tafi da su.”
Sai dai sojojin da suka yi sansani a yankin sun kawo ɗauki, inda suka yi nasarar ƙwato wasu dabbobni hannunsu.
Kazalika, daga bisani ’yan bindigar sun koma ƙauyen Magonho inda suka tarwatsa turakun sadarwa na kamfanin MTN.
Aminiya ta yi ƙoƙarin jin ta bakin jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan Jihar Sakkwato, DSP Rufa’i Ahmad, amma lamarin ya ci tura har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan sintiri Lakurawa Sakkwato
এছাড়াও পড়ুন:
‘Za a yi ambaliyar kwana 5 a jihohi 19 na Najeriya’
Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen cewa za a tafka mamakon ruwan sama na tsawon kwana biyar da zai iya haifar da ambaliyar ruwa a wurare 76 da ke jihohi 19 a Najeriya.
Cibiyar Gargadi kan Ambaliya ta Kasa da ke Ma’aikatar Muhalli ta kasa ce ya yi gargadin ranar Talata, inda ta bukaci dukkan masu ruwa da tsaki da ma sauran jama’a da su dauki mataki.
Gargadin na zuwa ne ’yan kwanaki bayan samun wata mummunar ambaliyar a jihohin Legas da Filato da Anambra da Delta.
Kwamishina ya yi murabus kan ƙarbar belin dillalin ƙwayoyi a Kano Ruftawar gini ta kashe uwa da ’ya’yanta 5 a KatsinaAna has ashen samun mamakon ruwan saman ne daga daga biyar zuwa tar aga watan Agustan 2025.
Yankunan jihohin da za a iya samun ambaliyar a cewar cibiyar sun hada da Kano (Bebeji, Gezawa, Gwarzo, Birni da Kewaye, Karaye, Tundun-wada, Wudil, Kunchi); Kebbi (Bagudo, Birnin-Kebbi, Bunza, Gwandu, Jega, Kalgo, Kamba, Kangiwa, Shanga, Ribah, Sakaba, Saminaka, Yelwa, Gauri-Banza); Neja (Kontagora, Rijau, Ringim); Filato (Mangu); Taraba (Donga, Takum); Jigawa (Diginsa, Gumel, Dutse, Gwaram, Hadejia, Miga); Yobe (Machina, Potiskum); Zamfara (Anka); Sakkwato (Sakkwato, Wamakko); Borno (Biu); da kuma Gombe (Bajoga).
Sauran wuraren sun hada da Akwa-Ibom (Edor, Eket, Ikom, Oron, Upenekang); Bauchi (Tafawa-Balewa, Azare, Jama’are, Kari, Misau, Jama’a); Ebonyi (Abakaliki, Echara, Ezilo); Kuros Riba (Ogoja Edor, Obubra); Nasarawa (Keana, Keffi, Wamba); Binuwai (Agaku, Buruku, Gboko, Igumale, Ito, Katsina-Ala, Ugba, Vande-Ikya); Kaduna (Jaji, Kafancha, Birnin-Gwari, Zaria) sai kuma a jihar Katsina (Bindawa, Bakori, Daura, Funtua).
Ambaliyar ruwa dai ta zama wata babbar annoba da ke faruwa a Najeriya a kowacce shekara inda takan lalata dukiyoyin da ma rasa rayukwan jama’a.
Ko a bara, akalla jihohi 31 ne aka samu rahoton ambaliyar ruwa wacce ta kai ga rasa rayukan mutane da dama tare da shafar mutum miliyan daya da dubu 200.