Iran Ta Yaba Da Sadaukarwar Da ‘Yan Jarida Suka Bayar Kan Watsa Wahalhalun Falasdinawa
Published: 4th, May 2025 GMT
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya yaba da sadaukarwar da ‘yan jarida suka bayar da suke ba da labaran irin wahalhalun da Falasdinawa ke ciki
A wani sako da ya wallafa a shafinsa na twitter na ranar ‘yancin ‘yan jarida ta duniya, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya bayyana jin dadinsa ga irin sadaukarwar da ‘yan jarida suka yi, wadanda suka rubuta irin wahalhalun da al’ummar Falastinu suke yi da kuma laifukan da yahudawan sahayoniyya suka yi a tsawon shekaru biyu da suka yi a zirin Gaza.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Iran ya rubuta a shafin sada zumunta na “X” a jiya Asabar cewa: Ranar ‘yancin ‘yan jarida ta duniya ta tuna da jarumtakar ‘yan jarida da masu daukar hoto da suka sadaukar da rayukansu cikin shekaru biyu da suka gabata don bayyana hakikanin yakin da ake yi a Gaza da kuma fallasa irin kisan kiyashin da ‘yan sahayoniyya suka yi wa Falasdinawa.
Baqa’i ya kara da cewa: A wannan karon, muna gaishe da kwararrun kafafen yada labarai sama da 200 wadanda suka rubuta irin wahala da radadin da Falasdinawan suke ciki, da kuma laifuffukan ‘yan mamaya, gami da shirin shafe wata al’umma daga kan doron kasa da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila take dauke da shi.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ma’aikatar Lafiya Ta Falasdinu Ta Tabbatar Da Karuwan Falasdinawan Da Suka Yi Shahada
Ma’aikatar lafiya ta Falasdinu ta tabbatar da cewa: Adadin wadanda suka yi shahada sakamakon ayyukan ta’addancin ‘yan sahayoniyya ya karu zuwa 52,495
Ma’aikatar lafiya ta Falasdinu ta sanar a jiya Asabar 3 ga watan Mayu, shekara ta 2025 cewa: Falasdinawa 77 ne da suka yi shahada da suka hada da gawarwakin mutane 7 da aka gano, da kuma wasu mutane 275 da suka jikkata an kai asibitoci a zirin Gaza cikin sa’o’i 24 da suka gabata.
Ma’aikatar lafiya ta Falasdinu a cikin rahotonta na kididdiga ta yau da kullum kan adadin shahidai da jikkata sakamakon hare-haren da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ke kai wa a Zirin Gaza: Har yanzu akwai adadin wadanda abin ya rutsa da su a karkashin baraguzan gine-gine da kuma kan tituna, kuma motocin daukar marasa lafiya da jami’an tsaron farar hula sun kasa kai musu dauki.
An ba da rahoton cewa adadin wadanda suka yi shahada a harin ta’addancin haramtacciyar kasar Isra’ila ya karu zuwa shahidai 52,495 da kuma jikkata 118,366 tun daga ranar 7 ga watan Oktoban shekara ta shekara 2023.
Ma’aikatar ta yi nuni da cewa adadin wadanda suka yi shahadada jikkata tun a ranar 18 ga watan Maris, 2025 ya kai (Shahidai 2,396, da jikkatan 6,325).