Kungiyar Hizbullahi Ta Lebanon Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya Suka Kai Kan Kasar Siriya
Published: 4th, May 2025 GMT
Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hizbullah ta kasar Lebanon ta yi Allah wadai da harin wuce gona da irin da ‘yan sahayoniyya suke yi kan kasar Siriya
Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hizbullah ta kasar Lebanon ta yi Allah-wadai da harin bam da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta kai a Siriya a ranar Asabar.
A cikin wata sanarwa da kungiyar ta Hizbullahi ta fitar ta ce: Tana jaddada tofin Allah tsine da yin Allah wadai da zaluncin yahudawan sahayoniyya da suka addabi kasar Siriya a wani mummunan hari da suka kai kan yankunan kasar, tare da fakewa da munanan kalamai da take-take na aiwatar da ayyukanta na fadadawa da wargaza kasar Siriya da nufin rusa hadin kan kasar da kuma haifar da fitina a tsakanin al’ummarta.”
Kungiyar ta kuma jaddada cewa: Wannan wuce gona da iri na yahudawan sahayoniyya wani yunkuri ne karara na gurgunta zaman lafiyar kasar Siriya da raunana karfinta, kuma hakan na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da kai hare-hare a kan kasar Lebanon da zirin Gaza.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Siriya
এছাড়াও পড়ুন:
Ambaliyar Mokwa – Har yanzu muna neman mutum 700 – Gwamnatin Neja
Gwamnatin jihar Neja ta ce har yanzu akwai sama da mutum 700 da suka bace ba gan su ba tun bayan mummunar ambaliyar ruwan da aka yi a karamar hukumar Mokwa da ke jihar.
Gwamnan jihar, Mohammed Umar Bago ne ya bayyana hakan lokacin da ya karbi babban dogarin tsohon Shugaban Kasa marigayi Janar Sani Abacha, Manjo Hamza Al-Mustapha yayin ziyarar jaje kan ambaliyar a Minna ranar Talata.
Gwamnan, wanda mataimakinsa, Yakubu Garba ya wakilta ya kuma ce akalla mutum 207 ne aka tabbatar da mutuwarsu sannan gidaje sama da 3,000 ne suka rushe.
DAGA LARABA: Ko Kare Kai Daga Harin ‘Yan Ta’adda Zai Kawo Karshen Matsalar Tsaro? Jirgin alhazai ya yi saukar gaggawa kan barazanar harin bom“Sama da mutum 700 ne suka bace kuma ba a san inda suke ba. Wannan ambaliyar ta jawo mana babbar asara,” in ji shi.
Ya kuma yaba wa hukumomi da kamfanoni da ma daidaikun jama’a da suka ba da tallafi, inda ya ce iftila’in annoba ce ta kasa baki daya.
Gwamnan ya kuma ce yanzu haka gwamnatin na dakon sakamakon binciken hukumomi kan musabbabin ambaliyar da hanyoyin kauce mata a nan gaba.
Tun da farko, Al-Mustapha ya ce ya je jihar ne domin jajanta mata kan mummunar ambaliyar ta Mokwa
“Za mu gana da masu rike da sarautun gargajiya da musamman Ciyaman din karamar hukumar ta Mokwa domin mu yi musu addu’ar kare faruwar hakan a nan gaba,” in ji shi.
Ya kuma ce tawagar jajen tasu ta kunshi muhimman mutane daga sassa daban-daban na kasar nan domin jajantawa da bayar da tallafi ga gwamnati da yankunan da ta shafa.