Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hizbullah ta kasar Lebanon ta yi Allah wadai da harin wuce gona da irin da ‘yan sahayoniyya suke yi kan kasar Siriya

Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hizbullah ta kasar Lebanon ta yi Allah-wadai da harin bam da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta kai a Siriya a ranar Asabar.

A cikin wata sanarwa da kungiyar ta Hizbullahi ta fitar ta ce: Tana jaddada tofin Allah tsine da yin Allah wadai da zaluncin yahudawan sahayoniyya da suka addabi kasar Siriya a wani mummunan hari da suka kai kan yankunan kasar, tare da fakewa da munanan kalamai da take-take na aiwatar da ayyukanta na fadadawa da wargaza kasar Siriya da nufin rusa hadin kan kasar da kuma haifar da fitina a tsakanin al’ummarta.”

Kungiyar ta kuma jaddada cewa: Wannan wuce gona da iri na yahudawan sahayoniyya wani yunkuri ne karara na gurgunta zaman lafiyar kasar Siriya da raunana karfinta, kuma hakan na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da kai hare-hare a kan kasar Lebanon da zirin Gaza.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Siriya

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Isra’ila sun kaddamar da sabbin hare-hare kan Siriya

Sojojin Isra’ila sun kaddamar da sabbin hare-hare ta sama kan yankuna daban-daban na kasar Siriya a yammacin Juma’a.

Rahotanni cikin gida sun ruwaito cewa jiragen yakin Isra’ila sun kai hare-hare akalla 20 a wajen garuruwan Damascus, Daraa da Hama, inda suka auna wuraren sojoji da ma’ajiyar kaya.  

Hare-haren sun hada da wani sansanin sojojin Syria da ke kusa da kauyen Shatha da ke Hama, hedkwatar tsohuwar bataliyar sojojin Syria da ke arewacin Damascus, da kuma sansanonin soji a Dera.

Fashe-fashe sun afku a Damascus da kewaye, ciki har da Harasta, inda wani farar hula ya mutu.

Kafofin yada labaran Isra’ila sun ruwaito cewa an kai hari a wasu yankuna a babban birnin kasar a karon farko.

Tun bayan faduwar gwamnatin Bashar al-Assad a watan Disambar 2024, kasar Siriya ta kasance karkashin mamayar Isra’ila.

Da sanyin safiyar Juma’a ne jiragen yakin Isra’ila suka kai hari a yankin da ke kusa da fadar shugaban kasa a Damascus, wanda shi ne hari na biyu da sojojin gwamnatin sahyoniyawan suka kai a cikin wannan mako.

Hukumomin Isra’ila sun kare harin a matsayin goyon baya ga al’ummar Druze, wadanda ke fafatawa da wasu masu dauke da makamai da HTC ke marawa baya a kusa da Damascus a wani sabon tashin hankali na kabilanci a karkashin mulkin HTC.

Rikicin ya yi sanadiyar mutuwar mutane da dama tare da jikkata.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Iran Ta Yi Allawadai Da Hare-haren HKI Akan Syria Da Nufin Rusa Kasar
  • Sojojin Isra’ila sun kaddamar da sabbin hare-hare kan Siriya
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Yi Kakkausar Suka Kan Hare-Haren Jiragen Saman Amurka Kan Kasar Yemen
  • Jiragen Saman Yakin Sojojin Isra’ila Sun Kai Hare-Haren Wuce Gona Da Iri Kan Kasar Siriya
  • Ministan Tsaron Iran Ya Bayyana Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya A Matsayar Alamar Yan Ta’adda
  • Kungiyar Ansarullahi Ta Yemen Ta Jaddada Goyon Baynata Ga Kungiyar Hizbullahi Ta Kasar Lebanon
  • Hamas Ta Yi Allah Wadai Da Matsayin Amurka Na Goyon Bayan Haramta Hukumar Kula Da ‘Yan Gudun Hijiran Falasdinawa Ta UN
  • Masifar Gobara Tana Kara Bunkasa A Haramtacciyar Kasar Isra’ila Tare Da Fara Raba Yahudawa Da Muhallinsu
  • Iran ta yi Allah-wadai da sabon takunkumin da Amurka ta lafta mata