A cikin jawabin sa a taron, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana wasu manyan fa’idoji da kuma irin barazanar da ke tattare wajen amfani da AI a cikin ɗakunan buga labarai.

 

Ya ce duk da cewa AI na taimaka wa ‘yan jarida a Nijeriya wajen saurin bayar da rahoto, da nazarin bayanai da gudanar da bincike, yana da matuƙar muhimmanci a yi amfani da wannan sabuwar fasahar cikin hankali da bin ƙa’idoji.

 

Ya ce: “A yayin da muke rungumar aikin jarida da fasahar AI, dole ne mu tabbatar da cewa ba za a tauye ‘yancin jarida ba, illa ma a ƙara ƙarfafa shi.”

 

Ministan ya kuma ba da sanarwar cewa Nijeriya za ta kafa Cibiyar Ilimin Kafafen Watsa Labarai ta UNESCO a Buɗaɗɗiyar Jami’ar Nijeriya (NOUN), inda Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya riga ya amince da kuɗin kafa cibiyar.

 

Ana sa ran wannan cibiyar za ta kasance cibiyar ƙasa da ƙasa da za ta inganta aikace-aikacen kafafen watsa labarai cikin gaskiya da tunani mai zurfi a fannin dijital.

 

Haka kuma, ya bayyana cewa Nijeriya tana kan hanyar ƙaddamar da tsarin dokar ƙasa kan amfani da AI a cikin aikin jarida.

 

Wannan tsari zai ƙarfafa ƙirƙire-ƙirƙire amma ba tare da tauye ‘yancin jarida ko karya ƙa’idojin aikin ba.

 

Idris ya buƙaci haɗin gwiwa tsakanin ‘yan jarida, da masana fasaha, da kafafen yaɗa labarai, da ‘yan siyasa da ƙungiyoyin farar hula domin samar da ƙa’idojin amfani da AI, da koyar da sababbin dabaru, da tabbatar da gaskiya, da kuma faɗakar da al’umma.

 

A nata jawabin, Marija Peran, wakiliyar KAS a Nijeriya, ta jaddada irin damar da AI ke bayarwa ga aikin jarida, tare da yin kashedi kan haɗurran da ke tattare da hakan.

 

Ta ce: “Yana da muhimmanci mu kare ‘yancin kafafen yaɗa labarai a duk duniya, musamman yanzu da AI ke ƙara shiga aikin jarida.

 

“A matsayin ta na ƙungiya mai kishin dimokiraɗiyya da doka da oda, KAS tana tare da kafafen yaɗa labarai wajen fuskantar wannan sabon yanayi.”

 

Taron ya samu halartar mutane daban-daban, ciki har da Shugaban Kwamitin Harkokin Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a na Majalisar Wakilai, Honarable Akintunde Rotimi Jr.; da wakilan kafafen yaɗa labarai, da ƙungiyoyin farar hula da kuma abokan hulɗa na ƙasa da ƙasa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: aikin jarida

এছাড়াও পড়ুন:

Abokin Takarar Tinubu: Rikici ya ɓarke a APC bayan Ganduje ya ƙi goyon bayan Shettima

An samu saɓani a wani taron shugabannin jam’iyyar APC a yankin Arewa Maso Gabas da aka gudanar a Jihar Gombe.

Rikicin ya fara ne bayan da Kwamared Mustapha Salihu, Mataimakin Shugaban APC na ƙasa mai kula da Arewa Maso Gabas, ya bayyana goyon bayansa ga takarar Shugaba Bola Tinubu don ya sake tsayawa takara a karo na biyu.

Yadda wani ɗan sanda ya rasu a hanyar zuwa ɗaurin aurensa HOTUNA: Yadda aka yi sulhu da ƙasurgumin ɗan fashin daji Ado Aliero a Katsina

Sai dai bai ambaci mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima ba.

Manyan jiga-jigan jam’iyyar APC daga yankin sun halarci taron, ciki har da gwamnoni, ministoci, da ‘yan majalisa.

Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Ganduje, shi ma ya halarci taron.

Bayan Salihu ya gama jawabi, wasu daga cikin mahalarta taron sun fusata.

Take suka fara yi masa ihu, wasu ma suna barazanar kai masa hari.

Sai jami’an tsaro sun fito da shi daga ɗakin taron don kare lafiyarsa.

Don kwantar da rikicin da ya taso, Mataimakin Shugaban jam’iyyar na ƙasa, Bukar Dalori, ya fito ya bayyana goyon baya ga Tinubu da kuma Shettima don su ci gaba da mulki.

Amma lamarin ya ƙara dagulewa bayan da Ganduje ya yi jawabi, inda ya ayyana goyon bayansa ga Tinubu kaɗai, ba tare da ya ambaci Shettima ba.

A yayin jawabin da ya yi na kusan minti 10, bai ambaci sunan Shettima ba.

Shi ma sai da jami’an tsaro suka fita da shi daga wajen taron saboda gudun rikicin da zai je ya dawo.

Shettima dai ɗan Jihar Borno ne, ɗaya daga cikin jihohin yankin Arewa Maso Gabas.

Mutane da dama sun ji ba ɗadi kan rashin ambaton sunan a wajen taro da aka yi a yankinsa.

Taron ya kare cikin gaggawa saboda tashin hankali.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kwaso ‘Yan Nijeriya Da Suka Maƙale A Isra’ila Da Iran
  • Ma’aikatan Kwalejin Ilimi ta jihar Kaduna za su tsunduma yajin aiki
  • Ambaliyar Mokwa – Har yanzu muna neman mutum 700 – Gwamnatin Neja
  • Sin Ta Cimma Sabuwar Nasarar Bincike Duniyar Wata
  • Buni ya bai wa manoma 1,000 tallafin aikin gona
  • An garzaya da ’yan Isra’ila 154 asibiti bayan harin Iran
  • Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga
  • Rundunar Sojin Ruwa Ta Nijeriya Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 5 A Ribas
  • Takarar Tinubu: Rikici ya ɓarke a APC bayan Ganduje ya ƙi goyon bayan Shettima
  • Abokin Takarar Tinubu: Rikici ya ɓarke a APC bayan Ganduje ya ƙi goyon bayan Shettima