Ma’aikatar lafiya ta Falasdinu ta tabbatar da cewa: Adadin wadanda suka yi shahada sakamakon ayyukan ta’addancin ‘yan sahayoniyya ya karu zuwa 52,495

Ma’aikatar lafiya ta Falasdinu ta sanar a jiya Asabar 3 ga watan Mayu, shekara ta 2025 cewa: Falasdinawa 77 ne da suka yi shahada da suka hada da gawarwakin mutane 7 da aka gano, da kuma wasu mutane 275 da suka jikkata an kai asibitoci a zirin Gaza cikin sa’o’i 24 da suka gabata.

Ma’aikatar lafiya ta Falasdinu a cikin rahotonta na kididdiga ta yau da kullum kan adadin shahidai da jikkata sakamakon hare-haren da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ke kai wa a Zirin Gaza: Har yanzu akwai adadin wadanda abin ya rutsa da su a karkashin baraguzan gine-gine da kuma kan tituna, kuma motocin daukar marasa lafiya da jami’an tsaron farar hula sun kasa kai musu dauki.

An ba da rahoton cewa adadin wadanda suka yi shahada a harin ta’addancin haramtacciyar kasar Isra’ila ya karu zuwa shahidai 52,495 da kuma jikkata 118,366 tun daga ranar 7 ga watan Oktoban shekara ta shekara 2023.

Ma’aikatar ta yi nuni da cewa adadin wadanda suka yi shahadada jikkata tun a ranar 18 ga watan Maris, 2025 ya kai (Shahidai 2,396, da jikkatan 6,325).

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Ma aikatar lafiya ta Falasdinu adadin wadanda

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Yau Jumma’a, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun ya gudanar da taron manema labarai na yau da kullum.

Dangane da sanarwar da Amurka ta fitar ta kakaba takunkumi kan jami’an hukumar kare hakkin Falasdinawa da mambobin kungiyar ‘yantar da Falasdinu, Guo Jiakun ya bayyana cewa, Sin ta kadu da hakan, kuma tana nuna takaici da rashin fahimta cewa, Amurka ta yi watsi da kokarin da kasashen duniya ke yi na samar da zaman lafiya ga Falasdinu. Kuma kasar Sin ta dage wajen goyon bayan tsari mai adalci ta al’ummar Falasdinu don maido da halastaccen hakkin al’ummar, kuma za ta ci gaba da yin namijin kokari a wannan fanni tare da sauran kasashen duniya.

Dangane da umarnin da shugaban Amurka Trump ya bayar na kara haraji kan kasashen duniya, Guo Jiakun ya bayyana cewa, matsayin kasar Sin na adawa da cin zarafi na kudaden haraji ba zai canza ba, domin babu wanda zai yi nasara a yakin haraji, kuma ra’ayin amfani da kariyar cinikayya yana cutar da muradun kowane bangare.

Dangane da rahotannin da ke nuni da cewa Amurka ta kaddamar da hare-hare ta yanar gizo kan kasar Sin, Guo Jiakun ya ce, wannan ya fallasa munafuncin Amurkan na koken “kama barawo” a fannin tsaron intanet. Kuma kasar Sin za ta ci gaba da daukar matakan da suka dace don kare tsaron intanet.(Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutum ɗaya ya rasu, an jikkata wasu yayin arangama da ’yan sanda a Abuja
  • Shugaba Pezeshkiyan Ya Yi Juyayin Shahadar Haniya Bayan Shekara Guda Da Shahada
  • Jihar Sakkwato ta ciyo bashin N70.4bn domin inganta kiwon lafiya
  • Jihar Sakkwato ta ciyo bashin N70.4bn N70.4bn domin inganta kiwon lafiya
  • Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu
  • Gaza: Mutane Da Dama Sun Yi Shahada A Yau Wasu Kuma Sun Jikkata
  • Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin
  • Yadda Yajin Aikin Ma’aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato
  • Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka
  • Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.