Kasar Yemen Ta Kakaba Takunkumi Kan Amurka A harkokin Fitar Da Man Fetur Din Kasarta
Published: 4th, May 2025 GMT
Kasar Yemen ta haramta fitar da man da Amurka ke fitarwa a matsayin mayar da martani ga wuce gona da irin sojojin Amurka kan kasarta
Cibiyar kula da ayyukan jin kai da ke birnin Sana’a na kasar Yemen ta sanar da dakatar da fitar da mai da Amurka ke fitarwa daga ranar 17 ga watan Mayu, a matsayin martani ga hare-haren da Amurka ke kaiwa kasar Yemen.
Cibiyar daidaita ayyukan jin kai da ke birnin Sana’a ta sanar a safiyar ranar Asabar, matakin hana fitar da danyen mai da Amurka ke yi daga cibiyoyin man fetur na kasar, wanda zai fara aiki daga ranar 17 ga watan Mayun wannan shekara ta 2025.
Wannan shawarar dai ta zo ne a matsayin martani ga hare-haren da Amurka ke kaiwa kan fararen hula da ababen more rayuwa a Yemen. A cikin wata sanarwa da cibiyar ta fitar ta ce: Kamfanonin da suka karya dokar, za a sanya su cikin jerin wadanda aka kakaba musu takunkumin da aka sanyawa masu ta’addanci kan kasar Yemen.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Yemen
এছাড়াও পড়ুন:
PLA Reshen Kudancin Kasar Ta Yi Sintiri Na Hadin Gwiwa A Tekun Kudancin Sin
Kakakin yada labarai na rundunar sojin ‘yantar da jama’ar kasar Sin ko PLA reshen kudancin kasar, babban kanar na sojojin sama Tian Junli, ya bayyana cewa, jiya Asabar rundunar sojin ta gudanar da sintiri na hadin gwiwa a ruwan teku da kuma sama a yankin tekun kudancin Sin.
Tian ya kara da cewa, sitirin hadin gwiwa a teku da sama da Philippines ta gudanar tare da wasu kasashen duniya, ya kawo barazanar tsaro ga yankin tekun kudancin Sin, kuma ya lalata zaman lafiya da kwanciyar hankali na yankin. Don haka, rundunar za ta ci gaba da kasancewa cikin shirin ko-ta-kwana tare da kiyaye ikon mulkin kan kasar Sin, da hakki da moriyarta a tekun.(Safiyah Ma)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp