Dalilin da ya sa aka samu fashewar abubuwa a barikin Maiduguri – Sojoji
Published: 1st, May 2025 GMT
A ranar Alhamis ɗin nan ne rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da cewa, an samu fashewar wani abu a wurin ajiyar makamai da ke barikin Giwa a Maiduguri wanda ya faru sakamakon tsananin zafi da aka samu a yankin.
A cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Alhamis mai ɗauke da sa hannun muƙaddashin daraktan hulɗa da jama’a na rundunar, Kaptin Reuben Kovangiya, a hedkwatar rundunar haɗin gwiwa ta shiyyar Arewa maso gabas ta Operation HAƊIN KAI.
Ya fayyace cewa fashewar ta faru ne ba sakamakon wani harin maƙiya ba, illa dai lamarin ya faru ne sakamakon yanayin zafi da ake fama da shi a halin yanzu da ya shafi makaman da aka ajiye a cikin ginin.
“Fashewar ta faru ne saboda yanayin zafi da ake ciki a Maiduguri, wanda ya kai ga fashewar wasu alburusai,” in ji Koɓangiya.
Ya ƙara da cewa, tuni an shawo kan lamarin ba tare da ɓata lokaci ba ta hanyar haɗin gwiwa da jami’an hukumar kashe gobara ta jihar Borno da sauran sassan bayar da agajin gaggawa daga jami’an tsaro.
Sanarwar ta ƙara da cewa, “An tura dakarun Operation HAƊIN KAI domin kare jama’a da kuma hana miyagu yin amfani da abin da ke faruwa.”
Don haka rundunar ta buƙaci mazauna yankin da su yi watsi da duk wani jita-jita na kai hari a ƙaramar hukumar Maiduguri kuma su kwantar da hankalinsu akan hakan.
“Don haka ana kira ga jama’a da su yi watsi da duk wani hasashe na harin… kuma su kwantar da hankula,” in ji Koɓangiya.
Rundunar Operation HAƊIN KAI dai na ci gaba da yaƙi da ’yan ta’adda a yankin Arewa maso Gabas ba dare ba rana.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Operation Haɗin Kai
এছাড়াও পড়ুন:
Matashi ya yi wa maraya ɗan shekara 10 kisan gilla a Zariya
Ana zargin wani ɗan shekaru 18 da kashe wani maraya ɗan shekara 10 a yankin Ƙaramar Hukumar Zariya ta Jihar Kaduna.
’Yan sanda sun kama matashin ne kan zargin sa da yi wa ɗan yaron, wanda ɗan baffansa ne, ɗaurin goro tare da azabtar da shi saboda yaron ya ƙi amincewa ya yi lalata da shi.
Lamarin ya faru ne a ranar Alhamis da ta gabata a unguwar Iyan Juma da ke Karamar Hukumar Zariya.
Mahaifiyar marigayin mai suna Asama’u Mohammed ta shaida wa Aminiya cewa, “Na dawo wajen aikatau kamar yadda na saba yi don na samo abin da zan ba su su ci tare da ’yan uwansa, sai ga yayansa ya shigo a guje ya ce ga Idris can a kwance cikin jini kuma fuskarsa a kumbure, wai sun yi faɗa da wani duk an ji mishi ciwo, nan da nan na yafa hijabi ni da ɗan uwar gidana muka tafi inda yake.”
Mahaifiyar Babban Editan jaridar Daily Trust ta rasu Koriya ta Arewa za ta taimaka da gyara tashoshin nukiliyan Iran —MasaniAminiya ta garzaya Babban Ofishin ’yan sanda da ke Ƙofar Fada cikin birnin Zariya domin ji daga bakin babban jima’i, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin kuma ya shaida wa wakilinmu, cewa sun tattara bayanai yadda lamarin ya kasance kuma sun tura zuwa babban ofishinsu da ke Kaduna
Kakakin rundunar ’yan sandan jihar Kaduna DSP Mansur Hassan ya tabbatar wa wakilin namu da faruwar lamarin, da kama wanda da ake zargi.
Ya ƙara da cewa bayan sun kammala bincike za su tora zuwa kuto.