Aminiya:
2025-09-24@16:06:49 GMT

Dalilin da ya sa aka samu fashewar abubuwa a barikin Maiduguri – Sojoji

Published: 1st, May 2025 GMT

A ranar Alhamis ɗin nan ne rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da cewa, an samu fashewar wani abu a wurin ajiyar makamai da ke barikin Giwa a Maiduguri wanda ya faru sakamakon tsananin zafi da aka samu a yankin.

A cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Alhamis mai ɗauke da sa hannun muƙaddashin daraktan hulɗa da jama’a na rundunar, Kaptin Reuben Kovangiya, a hedkwatar rundunar haɗin gwiwa ta shiyyar Arewa maso gabas ta Operation HAƊIN KAI.

’Yan fashin teku sun sace mata 4 a hanyar ruwa ta Bayelsa NAJERIYA A YAU: Dalilan Kamuwa Da Cutar Hawan Jini Da Hanyoyin Magance Ta

Ya fayyace cewa fashewar ta faru ne ba sakamakon wani harin maƙiya ba, illa dai lamarin ya faru ne sakamakon yanayin zafi da ake fama da shi a halin yanzu da ya shafi makaman da aka ajiye a cikin ginin.

“Fashewar ta faru ne saboda yanayin zafi da ake ciki a Maiduguri, wanda ya kai ga fashewar wasu alburusai,” in ji Koɓangiya.

Ya ƙara da cewa, tuni an shawo kan lamarin ba tare da ɓata lokaci ba ta hanyar haɗin gwiwa da jami’an hukumar kashe gobara ta jihar Borno da sauran sassan bayar da agajin gaggawa daga jami’an tsaro.

Sanarwar ta ƙara da cewa, “An tura dakarun Operation HAƊIN KAI domin kare jama’a da kuma hana miyagu yin amfani da abin da ke faruwa.”

Don haka rundunar ta buƙaci mazauna yankin da su yi watsi da duk wani jita-jita na kai hari a ƙaramar hukumar Maiduguri kuma su kwantar da hankalinsu akan hakan.

“Don haka ana kira ga jama’a da su yi watsi da duk wani hasashe na harin… kuma su kwantar da hankula,” in ji Koɓangiya.

Rundunar Operation HAƊIN KAI dai na ci gaba da yaƙi da ’yan ta’adda a yankin Arewa maso Gabas ba dare ba rana.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Operation Haɗin Kai

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kano Ta Tabbatar Ɓullar Cutar Mpox A Jihar

Ya ce Kano na cikin hatsari saboda cunkoson jama’a da kuma zirga-zirgar mutane daga wurare daban-daban.

KNCDC ta gudanar da cikakken bincike a Ungogo, inda aka duba unguwar da marar lafiyan yake da kuma asibitocin da ya ziyarta.

Duk wanda aka bincika yana cikin ƙoshin lafiya kuma babu wanda ya kamu da cutar.

Farfesa Abbas ya jaddada muhimmancin wayar da kan jama’a don hana yaɗuwar cututtuka.

Ya nemi kafafen watsa labarai su ci gaba da yaɗa bayanan lafiya ga al’umma.

Ya kuma buƙaci jama’a su kasance masu lura, inda ya tabbatar da cewa Kano tana da tsarin sa ido da shiri don shawo kan kowace irin cuta nan gaba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yada labaran karya a intanet babban laifi ne a Musulunci – Sheikh Ibrahim Khalil
  • An kama ɗan sandan bogi a Kano
  • An yi wa sojoji ɗaurin rai da rai kan sayar wa ’yan ta’adda makamai a Borno
  • Sojoji Sun Daƙile Hare-haren ISWAP, Sun Bai Wa Magidanta 10,000 Kariya A Borno
  • Gwamnatin Kano Ta Tabbatar Da Ɓullar Cutar Mpox A Jihar
  • Gwamnatin Kano Ta Tabbatar Ɓullar Cutar Mpox A Jihar
  • Taron Canada: Haɗin Gwiwa Afirka Ke Buƙata Ba Agaji Ba – Gwamnan Zamfara 
  • Dalilin da muke goyon bayan Tinubu kan karɓo bashi — Majalisar Wakilai
  • Dalilin da muke goyon bayan tsare-tsaren Tinubu na karɓo bashi — Majalisar Wakilai
  • Yadda Ƴan Agbero’ Ke Cin Karensu Ba Babbaka A Abuja