Aminiya:
2025-11-08@20:45:42 GMT

Dalilin da ya sa aka samu fashewar abubuwa a barikin Maiduguri – Sojoji

Published: 1st, May 2025 GMT

A ranar Alhamis ɗin nan ne rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da cewa, an samu fashewar wani abu a wurin ajiyar makamai da ke barikin Giwa a Maiduguri wanda ya faru sakamakon tsananin zafi da aka samu a yankin.

A cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Alhamis mai ɗauke da sa hannun muƙaddashin daraktan hulɗa da jama’a na rundunar, Kaptin Reuben Kovangiya, a hedkwatar rundunar haɗin gwiwa ta shiyyar Arewa maso gabas ta Operation HAƊIN KAI.

’Yan fashin teku sun sace mata 4 a hanyar ruwa ta Bayelsa NAJERIYA A YAU: Dalilan Kamuwa Da Cutar Hawan Jini Da Hanyoyin Magance Ta

Ya fayyace cewa fashewar ta faru ne ba sakamakon wani harin maƙiya ba, illa dai lamarin ya faru ne sakamakon yanayin zafi da ake fama da shi a halin yanzu da ya shafi makaman da aka ajiye a cikin ginin.

“Fashewar ta faru ne saboda yanayin zafi da ake ciki a Maiduguri, wanda ya kai ga fashewar wasu alburusai,” in ji Koɓangiya.

Ya ƙara da cewa, tuni an shawo kan lamarin ba tare da ɓata lokaci ba ta hanyar haɗin gwiwa da jami’an hukumar kashe gobara ta jihar Borno da sauran sassan bayar da agajin gaggawa daga jami’an tsaro.

Sanarwar ta ƙara da cewa, “An tura dakarun Operation HAƊIN KAI domin kare jama’a da kuma hana miyagu yin amfani da abin da ke faruwa.”

Don haka rundunar ta buƙaci mazauna yankin da su yi watsi da duk wani jita-jita na kai hari a ƙaramar hukumar Maiduguri kuma su kwantar da hankalinsu akan hakan.

“Don haka ana kira ga jama’a da su yi watsi da duk wani hasashe na harin… kuma su kwantar da hankula,” in ji Koɓangiya.

Rundunar Operation HAƊIN KAI dai na ci gaba da yaƙi da ’yan ta’adda a yankin Arewa maso Gabas ba dare ba rana.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Operation Haɗin Kai

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta

 

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an November 6, 2025 Daga Birnin Sin CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST November 6, 2025 Daga Birnin Sin Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya November 6, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iraki Na Samu Zaman Lafiya Kuma Tana Kokarin Kawo Karshen Zaman Sojojin Ketare A Kasar
  • An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa
  • An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi
  • Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Ta Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Ayyukan Cigaban Jihar Jigawa
  • Matsalar Tsaro: Mun samu gagarumin ci gaba a shekaru biyu – Tinubu
  • Matsalar Tsaro: Mun sami gagarumin ci gaba a shekaru biyu – Tinubu
  • Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna
  • Gwamnatin tarayya ki amince damu a matakin ƙasa – Bijilanti
  • Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta
  • Hafsan sojin sama ya umarci a yawaita yi wa ’yan ta’adda ruwan bama-bamai