Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC), Birgediya-Janar Olakunle Oluseye Nafiu, ya yi kira ga mambobin kungiyar a fadin kasar nan da su yi amfani da kafafen sada zumunta na zamani cikin gaskiya da kuma bayar da gudunmawa mai ma’ana ga ci gaban kasa.

 

Ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi ga matasa masu yiwa kasa rukunin A na 2025 Batch a sansanin ‘yan gudun hijira na wucin gadi da ke Gusau babban birnin jihar Zamfara.

 

Birgediya Janar Nafiu ya kuma shawarci matasan su guji bibiyar shaharar shafukan sada zumunta na zamani, maimakon haka su mayar da hankali wajen samar da bayanai masu ma’ana da tasiri.

 

“Bari in yi magana da ku game da amfani da kafofin watsa labarun, wani abu ne da ke tasowa. Dukkanku kuna da wayoyin hannu, duk kuna da bayanai, kuma duk kuna aiki ɗaya ko wani.

 

Ya yi bayanin cewa, ɗan gajeren faifan bidiyo na minti biyu ko uku na iya shiga hoto ko bidiyo mai zagaya yanar gizo da sauri kuma ya jawo hankalin dubban ɗaruruwan ko ma miliyoyin masu kallo ko mabiya ba tare da wani abu ba, ko ƙima mai fa’ida, yana mai cewa, irin wannan shaharar da sauri ta shuɗe.

 

Birgediya-Janar Nafiu ya kuma karfafa gwiwar ‘yan yiwa kasa hidima da su yi amfani da hanyoyin da suka dace wajen kai rahoton duk wata matsala ko damuwa da za su iya fuskanta a lokacin hidimarsu, maimakon yin korafin jama’a ta yanar gizo.

 

Tun da farko, kodinetan NYSC na jihar Zamfara, Malam Lawan Ahmad, ya ce an yi wa masu yi wa kasa hidima 611 wadanda suka hada da maza 414 da mata 196 rajista domin gudanar da aikin yiwa kasa hidima a bana.

 

COV/AMINU DALHATU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

 Rasha Ta Kai Munanan Hare-hare Akan Birnin Kiev Na Ukiraniya

Wani jami’in kasar Ukiraniya ya bayyana cewa, a kalla mutane 8 ne su ka jikkata sanadiyyar munanan hare-haren da Rasha ta kai wa birnin Kiev ta hanyar amfani da makamai masu linzami.

Shugaban sha’anin tafiyar da Mulki na soja a birnin Kiev Taimur Tikatishinko ya wallafa sanarwa a shafinsa na “Telegram’ cewa; A tsakanin wadanda su ka jikkata din da akwai karamin yaro dan shekaru 3, kuma tuni an dauki mutane 4 zuwa asibiti, daya daga cikinsu yana cikin mummunan hali.

Shi kuwa magajin birnin na Kiev Fitali Kikitshiko cewa ya yi, mutanen da su ka jikkata suna zaune ne a cikin gidaje mabanbanta a unguwa daya.

Har ila yau ya kara da cea; Harin ya haddasa fashewa mai karfi wacce ta sa tagogin gidaje su ka fashe, har zuwa gine-gine masu hawa 11.

A wani labarin daga jami’an kasar ta Ukiraniya, Rasha ta kai wasu hare-haren da jirage marasa matuki a garin Kirofifitsky wanda ya haddasa fashewa mai yawa.

A cikin makwannin bayan nan dai Rasha ta tsananta kai hare-hare a fadin kasar  Ukiraniya ta hanyar amfani da makamai masu linzami da kuma jiragen sama marasa matuki.

Tun a 2022 ne dai Rasha ta fara kai wa Ukiraniya hare-hare bisa dalilin cewa tana son shiga cikin kungiyar yarjejeniyar tsaro ta Nato.

Kasar ta Ukiraniya dai tana samun taimakon makamai da bayanai na sirri daga kungiyar ta Nato.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Manyan makarantu 2 ne kacal ke da rajista a Katsina — Gwamnati
  • Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
  • Kwamandan NDA Ya Bukaci Dalibai Su Dage da Karatu a Taron FGC Malali
  •  Girgizar Kasa Mai Karfi Ta Kada Yankin Kamtashatka Na Kasar Rasha
  • Kasashen Iran Da Rasha Sun Tattauna Batun Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai A Tsakaninsu
  • Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Bukaci A Kara Inganta Aikin Titin Gabasawa
  • Lebanon: Za A Yi Jana’izar  FItaccen Mawakin Gwagwarmaya Da Kishin Kasa Ziyad Rahbani A Yau Litinin
  •  Rasha Ta Kai Munanan Hare-hare Akan Birnin Kiev Na Ukiraniya
  • Wulayati: Hanyar Zangezur Wata Shirin Amurka Ne Don Matsa lamba Kan Iran Da Rasha                                                                                                                       
  • Wulayati: Hanyar Zangezur Wata Shirin Amurka Ne Don Matsa lamba Kan Kasashen Iran Da Rasha