Ministan harkokin wajen Jamhuriyar musulunci ta Iran Abbas Arakci ya fada wa kamfanin dillancin labarun “Irna” cewa; An sami cimma matsaya a tsakanin tawagogin Iran da na Amurka akan cewa a ranar Laraba mai zuwa za a dora daga inda akan tsaya a tattaunawar Nukiliya,”

Ministan harkokin wajen na Jamhuriyar Musulunci ta Iran ya kara da cewa; Tattaunawar ta gaba za a yi ta ne a tsakanin kwararru, da zai kai ga shimfida ka’idojin da za a dora yarjejeniyar a kansu.

A yau Asabar ne dai aka yi tattaunawa karo na biyu a tsakanin tawagogin Iran da na Amurka a cikin ofishin jakadancin kasar Oman dake birnin Rome na kasar Italiya.

Ministan harkokin wajen na Iran wanda ya gabatar da taron manema labari a bakin ofishin jakadancin kasar ta Oman a birnin Rome ya amsa tambayoyi mabanbanta da ‘yan jaridu su ka yi masa, da a ciki ya bayyana cewa; An dauki sa’oi 4 ana tattaunawar, kuma a wannan karon ma, tattaunawar ta yi armashi.

Dangane da tattaunawa ta gaba, ministan harkokin wajen na Iran ya bayyana cewa za ayi ta ne a kasar Oman, kuma a ranar asabar mai zuwa za su sake haduwa domin ganin inda nazarin kwararrun ya isa. Ministan harkokin wajen na Iran ya kora kore cewa Amurka ta bijiro da wata Magana idan ba ta makamashin Nukiliya ba. Ya kuma kara da cewa; Batun makamashin Nukiliya ne aka bijiro da shi, kuma akan shi muke Magana.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Ministan harkokin wajen na

এছাড়াও পড়ুন:

Nazarin CGTN: Ana Kara Bayyana Rashin Gamsuwa Da Sabuwar Gwamnatin Amurka Daga Ciki Da Wajen Kasar

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3
  • Amurka ta sake laftawa wasu kamfaninin mai na Iran takunkumi
  • Yadda ’yan Tifa da baƙin direbobi ke haddasa haɗari a Abuja
  • Iran Da Iraki Sun Ce An Kammala Shimfida Layin Dogo Daga Shalamcheh Zuwa Basra
  • Nazarin CGTN: Ana Kara Bayyana Rashin Gamsuwa Da Sabuwar Gwamnatin Amurka Daga Ciki Da Wajen Kasar
  • Babu Wata Tattaunawa Tsakanin Sin Da Amurka Game Da Batun Haraji
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Ci Gaba Da Killace Gaza Da Kashe Mutane, Laifi Ne Da Ba A Taba Yin Irinsa Ba
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Tattauana Da Shugaban Hukumar IAEA
  • Takht Ravanji: Iran Ba Za Ta Taba Yin Tattaunawa Akan Dakatar Da Tace Sanadarin Uranium Ba