Abbas Arakci: Tattaunawa Da Amurka Ta Hanyar Shiga Tsakanin Oman Ta Shiga Sabon Zango
Published: 19th, April 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Jamhuriyar musulunci ta Iran Abbas Arakci ya fada wa kamfanin dillancin labarun “Irna” cewa; An sami cimma matsaya a tsakanin tawagogin Iran da na Amurka akan cewa a ranar Laraba mai zuwa za a dora daga inda akan tsaya a tattaunawar Nukiliya,”
Ministan harkokin wajen na Jamhuriyar Musulunci ta Iran ya kara da cewa; Tattaunawar ta gaba za a yi ta ne a tsakanin kwararru, da zai kai ga shimfida ka’idojin da za a dora yarjejeniyar a kansu.
A yau Asabar ne dai aka yi tattaunawa karo na biyu a tsakanin tawagogin Iran da na Amurka a cikin ofishin jakadancin kasar Oman dake birnin Rome na kasar Italiya.
Ministan harkokin wajen na Iran wanda ya gabatar da taron manema labari a bakin ofishin jakadancin kasar ta Oman a birnin Rome ya amsa tambayoyi mabanbanta da ‘yan jaridu su ka yi masa, da a ciki ya bayyana cewa; An dauki sa’oi 4 ana tattaunawar, kuma a wannan karon ma, tattaunawar ta yi armashi.
Dangane da tattaunawa ta gaba, ministan harkokin wajen na Iran ya bayyana cewa za ayi ta ne a kasar Oman, kuma a ranar asabar mai zuwa za su sake haduwa domin ganin inda nazarin kwararrun ya isa. Ministan harkokin wajen na Iran ya kora kore cewa Amurka ta bijiro da wata Magana idan ba ta makamashin Nukiliya ba. Ya kuma kara da cewa; Batun makamashin Nukiliya ne aka bijiro da shi, kuma akan shi muke Magana.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Ministan harkokin wajen na
এছাড়াও পড়ুন:
Kasar Iran Ta Musanta Yin Katsalandan A Tattaunawar Neman Tsagaita Bude Wuta A Gaza
Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta musanta zargin yin katsalandan a tattaunawar tsagaita bude wuta a Gaza
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran, Ismail Baqa’i, ya musanta zargin katsalandan din Iran a tattaunawar tsagaita bude wuta a Gaza.
A yayin da yake amsa tambaya game da ikirarin da shugaban kasar Amurka ya yi na cewa Iran na tsoma baki a shawarwarin tsagaita bude wuta a zirin Gaza, ya ce: Jamhuriyar Musulunci ta Iran tare da dukkan kasashen duniya tana yin kakkausar suka kan kisan gillar da ake yi a Gaza tare da goyon bayan duk wani tsari da zai kai ga dakatar da aikata laifuka da kuma rage radadin wahalhalun da al’ummar Gaza suke ciki.
Baqa’i ya jaddada cewa; Masu yin shawarwarin Hamas sun fahimci bukatar neman cimma muradun al’ummar Gaza da ake zalunta ta hanyar da ta dace, kuma ba sa bukatar shiga tsakani na bangarori na uku dangane da hakan.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Iran ya yi la’akari da katsalandan din Iran a cikin shawarwarin da suka dace da cewa ba shi da tushe balle makama, yana mai jaddada cewa irin wadannan zarge-zarge wani nau’i ne na neman tauyaye hakki da gujewa hakkin da ya rataya a wuyar mutum da kokarin Amurka na gujewa duk wani mugun aiki da gwamnatin ‘yan sahayoniyya ta aikita kan al’ummar Falasdinu, da suka hada da kisan fararen hula 60,000 da ba su ji ba ba su gani ba, da suka hada da mata da kananan yara da kuma killace Zirin Gaza tsawon watanni. Da hana shigar agajin jin kai da kuma kashe fararen hula da ke fama da yunwa da kishirwa a tarkon kisa a wuraren da ake kira cibiyoyin rarraba kayan agaji da wata cibiyar Amurka ta kafa.