Shin Mataimakin Gwamnan Bauchi ya ‘mari’ Ministan Tinubu?
Published: 19th, April 2025 GMT
Rahotanni na cewa Mataimakin Gwamnan Bauchi, Auwal Mohammed Jatau, ya zabga wa Ministan Harkokin Waje, Yusuf Maitama Tuggar, mari saboda kalaman suka da ya yi kan gwamnatin jihar.
Wasu rahotanni na cewa Ministan ya yi wasu kalamai na caccaka ga Gwamna Bala Mohammed, lamarin da ya fusata mataimakinsa ya ɗauke Ministan da mari.
Bayanai sun ce lamarin ya faru ne a cikin motar da ke dakon wasu manyan jami’an gwamnati, ciki har da Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, yayin da suke kan hanyar zuwa naɗin sarauta da kuma ɗaurin auren ’yar tsohon gwamnan jihar, Muhammad Abdullahi Abubakar SAN.
Aminiya ta ruwaito cewa, a Juma’ar da ta gabata ce manyan jami’an gwamnati suka halarci ɗaurin auren Khadija Muhammad, da kuma naɗin sarautar Makama Babba I da aka gudanar a Fadar Sarkin Bauchi.
Sai dai cikin wata sanarwar mayar da martani kakkausa kan lamarin, kakakin mataimakin gwamnan, Muslim Lawal, ya musanta labarin, yana mai nanata cewa ubangidansa mutum ne mai mutunci da kamala da ba zai taɓa tsoma kansa cikin irin wannan hauragiya ba.
Amma wani da abin ya faru kan idonsa kuma ya buƙaci a sakaya sunansa, ya shaida wa Aminiya cewa, Mataimakin Gwamnan ya fusata ne bayan Ministan Harkokin Wajen ya riƙa jifar Gwamna Bala Mohammed da kalamai marasa daɗi. Majiyar ta ce wannan ce ta sanya rikicin ya hautsine a cikin motar da ke dakon manyan jami’an gwamnatin zuwa Fadar Masarautar Bauchi. Aminiya ta yi ƙoƙarin jin ta bakin Minista Yusuf Tuggar ya ci tura har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton.
Sai dai ɗan gwamnan jihar, Shamsuddeen Bala Mohammed na daga cikin waɗanda suka yi farin ciki da faruwar lamarin wanda ya riƙa tashe a dandalin sada zumunta na X.
Cikin wata wallafa mai tashe da ɗan gwamnan ya ƙara yaɗawa, mai ɗauke da saƙon cewa, “Mataimakin Gwamna na farko da ya mari Minista a Bauchi. Mista Taka ka sha mari….” da sauran saƙonni makamancin wannan da suke tashe.
Ana iya tuna cewa, wannan tsamin dangantaka ya samo asali ne tun bayan da Gwamna Bala Mohammed ya riƙa sukar Shugaba Bola Tinubu kan rashin shugabanci nagari.
A cewar gwamnan, manufofin da gwamnatin Tinubu ta ƙaƙaba sun jefa al’ummar ƙasar nan cikin ƙangin talauci da tsadar rayuwa.
Sai dai a martanin da Ministan ya mayar, ya ce gwamnan na fakewa da manufofin Tinubu domin ɓoye gazawarsa da zummar samun karɓuwa wajen neman kujerar shugabancin Nijeriya a Zaɓen 2027.
Wannan dai na zuwa ne a yayin da ake zargin cewa shi kansa Ministan na fafutikar zama Gwamnan Bauchi a 2027.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Bauchi mari Ministan Harkokin Waje Yusuf Tuggar Mataimakin Gwamnan Mataimakin Gwamna
এছাড়াও পড়ুন:
Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila
Babban daraktan kamfanin dillancin labaran kasar Qatar ya bayyana cewa taron gaggawa na kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC da ke tafe yana nuni da wani muhimmin sauyi na hadin kan kasashen larabawa da musulmi dangane da laifukan da ake aikatawa kan al’ummar Palastinu.
A cewar Pars Today, dukkanin idanuwa a ranakun Lahadi da Litinin (15-16 ga Satumba, 2025) za su kasance a Doha, babban birnin kasar Qatar, wanda zai karbi bakuncin taron gaggawa na shugabannin kasashen Larabawa da na Islama, don ba da amsa ga baki daya kan harin da Isra’ila ta kai kan Qatar.
Ana gudanar da wannan taron gaggawa ne a cikin yanayi na musamman na yanki da na duniya kuma ya biyo bayan harin da Isra’ila ta kai kan Qatar. Ana dai kallonsa a matsayin wani gagarumin sauyi ba wai kawai dangane da batun Falasdinu ba, har ma da sauran ci gaban siyasa a yankin.
A cikin wannan mahallin, masana da kwararru kan harkokin yada labarai na Qatar sun jaddada cewa zaluncin da Isra’ila ke yi wa Qatar ya farfado da ra’ayin kishin kasa na Larabawa tare da sake fasalin wasu muhimman batutuwan yankin.
Hadin kan Matsayin Larabawa da Musulunci
Ahmed Al-Rumaihi, Darakta-Janar na Kamfanin Dillancin Labarai na Qatar, ya ce hanyar shari’a ta kasa da kasa ita ce mafi kyawu kuma zabin da ya dace don tunkarar ci gaba da keta haddin ‘yan mamaya na (Sionist) – na farko daga cikin laifuffukan da aka rubuta da Benjamin Netanyahu, Firayim Ministan Isra’ila ya yi. Kotunan duniya, musamman kotun shari’a ta duniya, sun kafa sharuɗɗa da yawa waɗanda ke tabbatar da girman waɗannan laifuka.
Al-Rumaihi ya kara da cewa, ana ci gaba da yin Allah-wadai da wannan mugunyar ta’addancin da Isra’ila ke yi wa kasar Qatar, a duniya, kuma wannan ba wani abu ba ne, illa dai sakamakon yadda duniya ke kara wayar da kan jama’a game da keta haddin majalisar ministocin Isra’ila.
Farfado da Ra’ayin kishin Kasa
Babban editan jaridar Al-Sharq na kasar Qatar Jaber Al-Harami ya bayyana cewa, ha’incin da Isra’ila ta yi wa Qatar ya farfado da ra’ayin kishin kasa na Larabawa zuwa wani mataki da ba a taba ganin irinsa ba, wanda ke karfafa imanin cewa ba kasa daya ba ce kawai, yankin gaba daya. Al-Harami ya jaddada cewa, Isra’ila ba ta amince da wani jan layi ba, ba ta bi yarjejeniyoyin da aka kulla ko yarjejeniya ba, a maimakon haka tana aiwatar da munanan manufofin ba tare da la’akari da ka’ida ba.
A cewar Al-Harami, ta hanyar wannan wuce gona da iri Isra’ila na neman kafa sabbin sharudda da bukatu a karkashin shirin da ake kira “Isra’ila Babba”, inda ta sanya kasashen Larabawa a gaban wani zabi na wanzuwa. Don haka wajibi ne taron na Doha ya tashi daga kace-nace zuwa aiki na hakika.
Hakazalika, Nasser Al-Azba, wani lauya na kasa da kasa, ya jaddada cewa, lokaci ya yi da ya wuce yin Allah wadai da take-take, maimakon daukar matakai masu amfani da kuma daukar matakai masu inganci a kasa.
Al-Azba ya bayyana cewa, harin da Isra’ila ta kai kan Qatar a baya-bayan nan, ya nuna karara karya ce ga yarjejeniyar Vienna ta 1968, wadda ta kafa tsarin doka na kare jami’an diflomasiyya da masu shiga tsakani na kasa da kasa. A tarihi, manzanni sun kasance suna samun cikakkiyar kariya, kuma wannan ka’ida tana cikin dokokin duniya a yau.
Lauyan dokar kasa da kasa ya kara da cewa mayar da martani bai kamata ya takaita ga matakan shari’a ba, amma kuma dole ne ya hada da kulla kawance da kasashe da ba na yammacin Turai ba kamar su China, Rasha, da kasashen BRICS, yayin da a lokaci guda za a tattara ra’ayoyin jama’a na duniya don fallasa irin ta’addancin Isra’ila.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ministan Tsaron Kasar venezuela Ya Gargadi Amurka Dangane Da Kokarin Juyin Mulki A Kasar September 16, 2025 Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya September 16, 2025 Bayanin Bayan Taron Doha Ya Yi Kira Da A Kafa Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kare Kai September 15, 2025 Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar September 15, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha September 15, 2025 Dan Kasar Iran Mai Kirkira Ya Sami Kyautar Yabo A Kasar China September 15, 2025 Fizishkiyan: Wajibi Ne Musulmi Su Hada Kai Domin Dakatar Da Laifukan HKI September 15, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha September 15, 2025 Kwamitin Kolin Tsron Kasar Iran Ya Amince Da Yarjejeniyar Da Aka Cimma Da Hukumar IAEA September 15, 2025 Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar September 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci