Manyan Cibiyoyin Kudi Na Duniya Sun Yi Gargadai Akan Sabbin Kudaden Fito Na Amurka
Published: 4th, April 2025 GMT
Kungiyar kasuwanci ta duniya ( WTO) da asusun bayar da lamuni ( IMF) sun yi gargadi akan sakamakon dake tattare da Karin kudaden fito na kasuwanci da gwamnatin shugaban kasar Amurka Donald Trump ta yi a jiya Alhamis.
Kungiyar kasuwancin ta duniya, ta yi hasashen cewa ci gaban harkokin kasuwanci a duniya zai sami koma baya da kaso 1% a cikin 2025, wanda hakan yake nufin akasin yadda aka yi hasashe tun da fari.
Babbar daraktar kungiyar kasuwancin ta duniya Ngoz Okonjo-Iweala ta yi gargadin cewa, Karin kudaden fito da aka yi zai iya jefa duniya cikin yakin kasuwanci, idan kuwa kasashe su ka dauki matakin mayar da martani, to za a sami tsaiko a cikin harkokin kasuwanci a duniya.
Shi kuwa asusun bayar da lamuni na duniya ( IMF) ta bakin shugabarsa Kristalina Ivanova Georgieva, ya bayyana cewa; Wadannan matakan da aka dauka za jawo hatsari mai girma wajen ci gaban da tattalin arzikin duniya yake yi, musamman ma a wannan lokacin da dama ake fama da tafiyar hawainiyar da tattalin arzikin na duniya yake yi.
A gobe Asabar ne dai sabon harajin na Amurka zai fara aiki, wanda ya fara daga Karin 10% akan kayan da ake shigar da su Amurka, zuwa fiye da haka gwargwadon yadda ake da gibi a tsakanin kowace kasa da Amurkan.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp