Manyan Cibiyoyin Kudi Na Duniya Sun Yi Gargadai Akan Sabbin Kudaden Fito Na Amurka
Published: 4th, April 2025 GMT
Kungiyar kasuwanci ta duniya ( WTO) da asusun bayar da lamuni ( IMF) sun yi gargadi akan sakamakon dake tattare da Karin kudaden fito na kasuwanci da gwamnatin shugaban kasar Amurka Donald Trump ta yi a jiya Alhamis.
Kungiyar kasuwancin ta duniya, ta yi hasashen cewa ci gaban harkokin kasuwanci a duniya zai sami koma baya da kaso 1% a cikin 2025, wanda hakan yake nufin akasin yadda aka yi hasashe tun da fari.
Babbar daraktar kungiyar kasuwancin ta duniya Ngoz Okonjo-Iweala ta yi gargadin cewa, Karin kudaden fito da aka yi zai iya jefa duniya cikin yakin kasuwanci, idan kuwa kasashe su ka dauki matakin mayar da martani, to za a sami tsaiko a cikin harkokin kasuwanci a duniya.
Shi kuwa asusun bayar da lamuni na duniya ( IMF) ta bakin shugabarsa Kristalina Ivanova Georgieva, ya bayyana cewa; Wadannan matakan da aka dauka za jawo hatsari mai girma wajen ci gaban da tattalin arzikin duniya yake yi, musamman ma a wannan lokacin da dama ake fama da tafiyar hawainiyar da tattalin arzikin na duniya yake yi.
A gobe Asabar ne dai sabon harajin na Amurka zai fara aiki, wanda ya fara daga Karin 10% akan kayan da ake shigar da su Amurka, zuwa fiye da haka gwargwadon yadda ake da gibi a tsakanin kowace kasa da Amurkan.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kasar Holland Ta Hana MInistocin HKI Biyu Shiga Cikin Kasarta
A jiya Litinin ne dai gwamnatin kasar Holland ta sanar da hana wa minstocin tsaron kasa Itmir Bin Gafir, da na kudi, Bitsirael Smotrich shiga cikinta.
Kasar ta Holland ta zargi wadannan mutanen biyu da cewa suna ingiza sojojin HKI da yi wa Falasdinawa kisan kiyashi da kuma fadada yawan matsugunan ‘yan sahayoniya a yankunan da aka ce nan ne za a kafa Daular Falasdinawa.
Haka nan kuma gwamnatin kasar ta Holland ta kira yi jakadan HKI a birnin Hauge domin gargadinsa akan yanayin da ake ciki a Gaza, da cewa babu yadda za a iya ci gaba da jurewa akansa, ko kare dalilin jefa yankin cikin wannan halin.”
Wannan matakin na kasar Holland ya zo ne gabanin wani taro da tarayyar turai za ta yi a yau Talata domin jingine aikin tare da HKI a fagen nazari da bincike na ilimi, saboda ta ki tsagaita wutar yaki a Gaza.
Tun da fari, Fira ministan kasar Holland Dick Schoof ya wallafa a sharin X cewa; A yayin taron da kasashen turai za su yi, Kasarsa za ta yi matsin lamba akan ganin an dakatar da yarjejeniyar kasuwanci da HKI, haka nan kuma kakaba takunkumai akan shigar da kayanta na kasuwanci zuwa kasuwannin turai.
Fira ministan na kasar Holland ya ce, ya fada wa shugaban HKI Ishaq Herzog wannan matakin da suke son dauka ta hanyar tarayya turai.