Aminiya:
2025-06-29@14:22:09 GMT

An kashe sojoji, fararen hula da dama a Borno

Published: 18th, April 2025 GMT

Wasu ’yan ta’adda da ake kyautata zaton ’yan Boko Haram ne sun kai hari a sabuwar unguwar Yamtake da ke Ƙaramar hukumar Gwoza a Jihar Borno, inda suka kashe sojoji biyu tare da wasu fararen hula da ba a bayyana adadinsu ba.

Majiyoyin tsaro da na cikin gida sun tabbatar da harin, inda suka ce maharan sun mamaye unguwannin ne da misalin ƙarfe 11:15 na daren Alhamis.

Gwamnatin Yobe ta sayo hatsi don tunkarar kakar bana Matan da suka tsira daga Boko Haram na buƙatar tallafin musamman

Ɗaya daga cikin majiyar sojojin ta ce, kafin a aike da wata tawagar sojoji daga Gwoza, maharan sun riga sun afkawa jama’a  da sansanin sojan Yamtake.

“Muna jiran tawagar masu ƙarfafa musu su dawo, amma mun sami labarin cewa mutane biyu daga cikin jami’anmu da wasu fararen hula harin ya shafe su. Ina ba da shawarar mu jira har sai sun dawo,” in ji shi.

Sai dai Sanata Ali Ndume, ya ce tun lokacin da lamarin ya faru yana tuntuɓar al’ummar unguwar Yamtake.

“Abin takaici ne cewa mutanenmu a ƙauyen Yamtake sun fuskanci mummunan harin Boko Haram a daren ranar Alhamis, ɗaya ne daga cikin unguwannin da suka karɓi ’yan gudun hijirar kwanan nan, gwamnatin Jihar Borno ta sake tsugunar da su.

“Abin baƙin ciki ne yadda sojoji biyu suka rasa ransu a bakin aiki, yayin da wasu fararen hula da ba a san ko su wanene ba na daga cikin waɗanda suka jikkata, Allah Ya gafarta musu.

“Amma kuma na yabawa Birgediya Janar Nasir Abdullahi, Birgediya Kwamanda na runduna ta 26 Task Force da jiga-jigan sojojinsa kan sadaukarwar da suka yi ba tare da ƙaƙƙautawa ba wajen daƙile hare-hare da dama, musamman waɗanda aka yi yunƙurin kaiwa farmakin a garin Gwoza.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram Yamtake fararen hula

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Shigar Da Korafi A Hukumar Kare Hakkin Bil’adama Ta MDD

Gwamnatin kasar Iran ta kai korafi a gaban hukumar kare hakkin bil’adama ta MDD dangane da yakin da HKI da kuma Amurka suka kaiwa kasar na tsawon kwanaki 12, wanda yayi sanadiyyar rasa rayukan mutane fiye da 600.

Nasir Siraj wani jami’in ofishin jakadancin Iran a MDD ya mikawa kwamitionan hukumar Volker Türk  a jiya Jumma’a .

Kafin haka dai ministan kiwon lafiya na kasar Iran ya bayyana cewa mutane 627 suka rasa rayukansu a yayinda wasu 4,870 suka ji rauni a yakin kwanaki 12 wanda wadannan kasashe biyu suka keta hurumin sararin samaniyar kasar.  Yakin ya zo karshe ne bayan da HKI ta shelanta tsaida yaki ita kadai.

Korafin ya bayyan cewa abinda wadannan kasashe biyu suka yi ya sabawa dokokin kasa da kasa da dama, daga ciki har da dokar kasa da kasa ta kare hakkin bil’adama.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Nijeriya ce kasa ta 12 mafi talauci a duniya — IMF
  • Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
  • Mangu: Gwamnatin Filato ba ta aiko da wakilai don yin ta’aziyya ba — Sarkin Zazzau 
  • Fararen hulan Isra’ila sun kai wa sojojin ƙasarsu hari
  • ‘An kashe ’ya’yana da mijina da ’yan uwana a hanyar ɗaurin auren ɗana’
  • Iran Ta Shigar Da Korafi A Hukumar Kare Hakkin Bil’adama Ta MDD
  • Tirela ta afka cikin kasuwa ta kashe mutum da raunata 5 a Taraba
  • Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC
  • Sojoji sun yi wa ’yan bindiga luguden wuta a Neja
  • ’Yan sanda sun kashe ‘yan fashi da ƙwato makamai a Kaduna