Gazawar Gwamnati Kan Kiyaye Rayuka Da Dukiyoyi: Gwamnan Filato Ya Nemi Yafiyar Al’ummar Jihar
Published: 16th, April 2025 GMT
Ya kuma jaddada cewa, “An yi duk wani shiri don kauce wa hakan, amma duk da haka mun gaza, a madadin gwamnati da hukumomin tsaro ku yafe mana”.
Gwamnan ya yi Allah-wadai da ci gaba da hare-haren da suka addabi yankin Irigwe, ya kuma yi alkawarin sabunta alkawarin kawo karshen tashe-tashen hankula a jihar.
Mutfwang ya bukaci al’umma da su dawo da tsare-tsaren tsaro na iyaye da kakanni, ya kuma yi kira ga matasa da su sa ido sosai, musamman a lokacin damuna mai zuwa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Tinubu ya gana da Janar Christopher CG Musa bayan Ministan Tsaro ya yi murabus
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi wata ganawar sirri da tsohon Babban Hafsan Tsaron Najeriya, Janar Christopher Gwabin Musa a Fadar Shugaban Kasa.
Ganawar Tinubu da Janar CG Musa ya auku ne a ranar Litinin da dare, jim kadan kafin sanarwar murabus din Ministan Tsaro, Alhaji Muhammad Badaru Abubakar.
Majiyoyi na cewa gananawar shugaban kasa da Janar CG Musa na da nasaba da shirin shugaban kasar na cike gurbin da Badaru ya bari da kuma garambawul a shugabancin tsaron Najeriya.
Mai magana da yawun shugaban kasa Bayo Onanuga ya sanar cewa Badaru ya yi murabus ne saboda dalilai na rashin lafiya.
An kama ’yan bindiga 4 a Kano MAAUN: Ƙungiyar iyaye ta musanta zargin ƙara ƙudin yaye ɗalibai a jami’arBadaru ya ajiye aiki ne a daidai lokacin da Najeriya ke fama da karuwar matsalar tsaro musammana a shiyyar Arewa lamarin da ya sa Shugaba Tinubu ya ayyan dokar ta-baci kan sha’anin tsaro.
A cikin ’yan watannin nan ’yan ta’adda a hare-harensu, suka kashe wani Janar din soja, Kwamandan Birget na 25 da ke Jihar Borno, Birgediya-Janar Uba Musa da dakarunsa a Jihar Borno, inda kuma suka yi garkuwa da wasu mata a gona.
A kwanan nan ’yan ta’adda sun tsananta kai hare-hare a Jihar Kano, baya ga sace daruruwan dalibai a jihohin Kebbi da Neja da kuma yin garkuwa da masu ibada a Jihohin Kwara da Kogi da kuma sace wasu mata a Borno.