Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da amfani da Hijabi ga jami’an tsaro mata a fadin jihar.

Kwamishinan Yada Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu, Alhaji Sagir Musa Ahmed ne ya bayyana haka jim kadan bayan kammala taron majalisar zartarwa da aka gudanar a fadar gwamnatin  jihar da ke Dutse.

A cewarsa, majalisar ta bayar da umarni ga kamfanonin tsaro guda uku da ke aiki a jihar, su bai wa jami’an tsaro mata daga cikin matasa 9,969 da aka dauka aiki, damar sanya Hijabi yayin aiki, a matsayin girmamawa ga addini da al’adu.

Alhaji Sagir Musa Ahmed ya ce, wannan matsaya ta biyo bayan rahoton da kwamitin majalisar kan tsaron makarantu, asibitoci da kotuna ya gabatar, kuma aka sake jaddada kudurin gwamnatin na tabbatar da tsarin aiki mai cike da mutuntaka, da daidaito.

Ya ce, majalisar zartarwar ta kuma amince da kaddamar da makon kirkira da kere-kere na jihar (JISCIW) daga shekarar 2025.

Ya jaddada cewa, wannan tsari na nuna jajircewar gwamnatin wajen bunkasa basira da hazakar matasa, da kuma inganta kirkire-kirkire da tunani mai zurfi a fadin jihar.

Sagir ya bayyana cewa, JISCIW zai kara zaburar da matasa a fannoni daban-daban kamar fasaha, zane, kasuwanci da kuma harkokin fasaha.

Ya kara da cewa, majalisar ta amince da fitar da sama da Naira miliyan 516 domin sayen tikitin jirgi ga daliban jihar Jigawa 185 da ke karatu a fannin likitanci da kimiyyar kiwon lafiya a Jami’ar Near East dake kasar Cyprus, domin shirye-shiryen zangon karatu na shekarar 2024/2025.

Kwamishinan ya kara da cewa, wannan tallafi ya nuna yadda gwamnatin ke ci gaba da daukar nauyin ilimi da jin dadin daliban da ke karatu a kasashen waje, musamman a muhimman fannoni kamar likitanci da kiwon lafiya.

 

Usman Muhammad Zaria 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Jihar Kebbi Ta Kammala Shirye-shiryen Aikin Hajjin 2025

Hukumar Jin Daɗin Alhazai a Jihar Kebbi ta bayyana cewa ta kammala dukkan shirye-shiryen gudanar da aikin Hajjin bana a Ƙasa Mai Tsarki.

Amirul Hajji na jihar na shekarar 2025 kuma Sarkin Argungu, Alhaji Samaila Muhammad Mera, ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai a lokacin taron farko da aka gudanar a hedkwatar hukumar da ke Birnin Kebbi.

Ya kuma yi alkawarin tabbatar da jin daɗin mahajjatan jihar yayin da suke a ƙasa mai tsarki.

Amirul Hajjin ya bayyana cewa jimillar mahajjata 3,800 daga jihar ne suka biya kuɗin kujerunsu gaba ɗaya domin aikin hajjin bana, kuma jigilar mahajjatan za ta fara ne ranar 9 ga watan Mayu, inda ya ce da yardar Allah za a ci gaba da jigilar ba tare wani tsaiko ba har sai an kammala.

Ya kuma bayyana cewa, a wannan shekarar, za a yi wa mahajjata canjin kuɗin guzirinsu na BTA zuwa kudin Saudiyya wato riyal  kai tsaye, da nufin dakile ayyukan damfara da kuma kare mahajjata daga asarar kuɗi yayin musayar kuɗaɗe a nan gida da kuma Saudiyya.

Alhaji Muhammadu Mera ya shawarci mambobin tawagar gwamnati da jami’an hukumar jin daɗin mahajjata da su gudanar da ayyukansu bisa tsoron Allah, tare da kare haƙƙoƙin mahajjata, daidai da manufar Gwamna Nasir Idris na gudanar da sahihin aikin Hajji mafi kyau.

Shugaban Hukumar, Alhaji Faruk Musa Yaro, ya yi alkawarin bayar da cikakken haɗin kakaga tawagar gwamnati domin tabbatar da nasarar aikin Hajji da ba a taɓa irin sa ba a tarihin jihar.

Ya ce an riga an samu masauki da sauran abubuwan buƙata ciki har da sufuri da abinci a ƙasa mai tsarki, sannan kuma kamfanin jirgin samsada ya yi jigilar Alhazan jihar a shekarar da ta gabata,  wato Flynas, a bana ma shi ne zau yi jigilar mahajjatan zuwa kasa mai tsarki.

Haka kuma, an an fara yi wa Amirul Hajj da sauran mambobin tawagar gwamnati allurar rigakafi  yayin kaddamar da shirin rigakafin mahajjatan.

 

Daga Abdullahi Tukur

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnan Sokoto Ya Amince Da Sauya Wa Manyan Sakatarori 25 Ma’aikatu A Jihar 
  •  Bom Da Ya Tashi A Arewa Maso Gabashin Najeriya Ya Kashe Mutane 6
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Shirya Fara Tantance ‘Yan Fansho
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Na Iran Ya Ce: Maganar ‘Yan Sahayoniyya Rudu Ne Maras Amfani
  • Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana
  • Jihar Kebbi Ta Kammala Shirye-shiryen Aikin Hajjin 2025
  • Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan uku
  • Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026
  • Iran Da Rasha Sun Jaddada Yin Aiki Tare A Fagen Kiwon Lafiya
  • Yadda matsalar ƙwacen waya da faɗan daba ke addabar Kano