Gwamnatin Jigawa Ta Bukaci Jami’an Tsaro Mata Su Rika Sanya Hijabi Yayin Aiki
Published: 16th, April 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da amfani da Hijabi ga jami’an tsaro mata a fadin jihar.
Kwamishinan Yada Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu, Alhaji Sagir Musa Ahmed ne ya bayyana haka jim kadan bayan kammala taron majalisar zartarwa da aka gudanar a fadar gwamnatin jihar da ke Dutse.
A cewarsa, majalisar ta bayar da umarni ga kamfanonin tsaro guda uku da ke aiki a jihar, su bai wa jami’an tsaro mata daga cikin matasa 9,969 da aka dauka aiki, damar sanya Hijabi yayin aiki, a matsayin girmamawa ga addini da al’adu.
Alhaji Sagir Musa Ahmed ya ce, wannan matsaya ta biyo bayan rahoton da kwamitin majalisar kan tsaron makarantu, asibitoci da kotuna ya gabatar, kuma aka sake jaddada kudurin gwamnatin na tabbatar da tsarin aiki mai cike da mutuntaka, da daidaito.
Ya ce, majalisar zartarwar ta kuma amince da kaddamar da makon kirkira da kere-kere na jihar (JISCIW) daga shekarar 2025.
Ya jaddada cewa, wannan tsari na nuna jajircewar gwamnatin wajen bunkasa basira da hazakar matasa, da kuma inganta kirkire-kirkire da tunani mai zurfi a fadin jihar.
Sagir ya bayyana cewa, JISCIW zai kara zaburar da matasa a fannoni daban-daban kamar fasaha, zane, kasuwanci da kuma harkokin fasaha.
Ya kara da cewa, majalisar ta amince da fitar da sama da Naira miliyan 516 domin sayen tikitin jirgi ga daliban jihar Jigawa 185 da ke karatu a fannin likitanci da kimiyyar kiwon lafiya a Jami’ar Near East dake kasar Cyprus, domin shirye-shiryen zangon karatu na shekarar 2024/2025.
Kwamishinan ya kara da cewa, wannan tallafi ya nuna yadda gwamnatin ke ci gaba da daukar nauyin ilimi da jin dadin daliban da ke karatu a kasashen waje, musamman a muhimman fannoni kamar likitanci da kiwon lafiya.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Neja ta zargi makarantar da aka sace wa dalibai da kin bin umarninta
Gwamnatin Jihar Neja ta tabbatar da sace ɗalibai da ma’aikatan makarantar Katolika ta Saint Mary da ke Papiri, da ke Ƙaramar Hukumar Agwara da jihar.
Aminiya ta rawaito yadda ’yan bindiga suka kutsa cikin makarantar tsakanin ƙarfe 2:00 zuwa 3:00 na safiyar Juma’a.
’Yan bindiga sun sace dalibai a wata makarantar Neja ’Yan bindigar da suka sace masu ibada a cocin Kwara sun nemi a ba su N3bn kafin sakin suShugaban Sashen bayar da Agaji na Ƙaramar Hukumar, Ahmed Abdullahi Rofia, ya tabbatar da harin ta wayar salula, amma bai bayar da cikakkun bayani ba.
Sai dai a cikin wata sanarwa, Sakataren Gwamnatin Jihar Neja, Abubakar Usman, ya ce bayan samun bayanan sirri tun da farko, gwamnati ta bayar da umarnin rufe dukkan makarantun kwana a yankin.
Sai dai ya ce makarantar da abin ya shafa ta ƙi bin umarnin ta kuma buɗe makarantar.
“Gwamnatin Jihar Neja ta yi matuƙar bakin ciki da labarin sace ɗaliban makarantar St. Mary da ke Ƙaramar Hukumar Agwara. Har yanzu ba a tabbatar da adadin ɗaliban da aka sace ba yayin da jami’an tsaro ke ci gaba da tantance lamarin.
“Jihar ta samu bayanan sirri tun da farko da ya nuna ƙaruwa barazanar tsaro a wasu sassan yankin arewa.”
“A kan haka ne Gwamnatin jiha ta bayar da umarnin dakatar da dukkan ayyukan gine-gine tare da rufe dukkan makarantun kwana a yankin da abin ya shafa a matsayin kandagarki
“Sai dai makarantar St. Mary ta ci gaba da zama a buɗe da ci gaba da karatu ba tare da sanarwa ko neman izini daga gwamnati ba.”
“Jami’an tsaro sun riga sun fara cikakken bincike da aikin ceto domin tabbatar da an dawo da ɗaliban gida lafiya.”
“Gwamnatin Jihar Neja tana aiki kai tsaye da dukkan hukumomin tsaro da abin ya shafa kuma za ta ci gaba da bayar da rahotanni yayin da bayani kara fitowa.”
“Gwamnati na kira ga masu makarantu, shugabannin al’umma, da duk masu ruwa da tsaki da su bi ƙa’idojin tsaro da aka bayar domin kare rayukan jama’a. Kariya ga rayuka, musamman na ’ya’yanmu, ita ce babban abin da wannan gwamnatin ta sa a gaba,” in ji shi.
A Jihar Kwara makwabciyar Nejan, gwamnatin jihar ta sanar da rufe makarantu fiye da 50 a kananan hukumomi hudu sakamakon sake ƙaruwar hare-hare a yankunansu.