Gwamnatin Jigawa Ta Bukaci Jami’an Tsaro Mata Su Rika Sanya Hijabi Yayin Aiki
Published: 16th, April 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da amfani da Hijabi ga jami’an tsaro mata a fadin jihar.
Kwamishinan Yada Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu, Alhaji Sagir Musa Ahmed ne ya bayyana haka jim kadan bayan kammala taron majalisar zartarwa da aka gudanar a fadar gwamnatin jihar da ke Dutse.
A cewarsa, majalisar ta bayar da umarni ga kamfanonin tsaro guda uku da ke aiki a jihar, su bai wa jami’an tsaro mata daga cikin matasa 9,969 da aka dauka aiki, damar sanya Hijabi yayin aiki, a matsayin girmamawa ga addini da al’adu.
Alhaji Sagir Musa Ahmed ya ce, wannan matsaya ta biyo bayan rahoton da kwamitin majalisar kan tsaron makarantu, asibitoci da kotuna ya gabatar, kuma aka sake jaddada kudurin gwamnatin na tabbatar da tsarin aiki mai cike da mutuntaka, da daidaito.
Ya ce, majalisar zartarwar ta kuma amince da kaddamar da makon kirkira da kere-kere na jihar (JISCIW) daga shekarar 2025.
Ya jaddada cewa, wannan tsari na nuna jajircewar gwamnatin wajen bunkasa basira da hazakar matasa, da kuma inganta kirkire-kirkire da tunani mai zurfi a fadin jihar.
Sagir ya bayyana cewa, JISCIW zai kara zaburar da matasa a fannoni daban-daban kamar fasaha, zane, kasuwanci da kuma harkokin fasaha.
Ya kara da cewa, majalisar ta amince da fitar da sama da Naira miliyan 516 domin sayen tikitin jirgi ga daliban jihar Jigawa 185 da ke karatu a fannin likitanci da kimiyyar kiwon lafiya a Jami’ar Near East dake kasar Cyprus, domin shirye-shiryen zangon karatu na shekarar 2024/2025.
Kwamishinan ya kara da cewa, wannan tallafi ya nuna yadda gwamnatin ke ci gaba da daukar nauyin ilimi da jin dadin daliban da ke karatu a kasashen waje, musamman a muhimman fannoni kamar likitanci da kiwon lafiya.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
N750,000 kuɗin bikin yaye ɗaliban Jami’ar MAAUN ya tayar da ƙura a Kano
Ana ci gaba da ta ƙaddama kan Naira dubu ɗari bakwai da hamsin da Jami’ar Amurka ta Maryam Abacha (MAAUN) da ke Jihar Kano ta wajabta wa ɗalibanta da suka kammala karatu biya a matsayin kuɗin bikin yaye ɗalibai.
Jami’ar MAAUN ta sanya wa kowane ɗalibin da ya kammala karatu biyan Naira dubu ɗari bakwai da hamsin a matsayin kuɗin bikin yaye ɗalibai, kafin ta ba shi takardar shaidar kammala karatu da gabatar da bayanansa domin samun damar halartar aikin yi wa ƙasa hidima (NYSC).
Sai dai kuma, Hukumar Karɓar Ƙorafi ta Jihar Kano (PCACC) ta umarci iyayen ɗaliban cewa su dakata da biyan kuɗin har sai ta kammala bincike kan ƙorafin da suka gabatar mata a kan lamarin.
Sanarwar da Shugaban Sashen Ayyuka na PCACC, Salisu Saleh, ya fitar bayan samun ƙorafi daga iyayen ɗaliban, ta umarci hukumar gudanarwar Jami’ar MAAUN da ta jingine shirinta na riƙe takardar kammala karatun ɗaliban ko tura sunayensu domin shirye-shiryen NYSC, saboda rashin biyan kuɗin.
’Yan bindiga sun sace amarya da ƙawenta 14 a Sakkwato Sojoji sun ceto mutum 7 da ’yan bindiga suka sace a Kano Sojoji sun ceto ’yan mata 12 da ISWAP suka sace a BornoA gefe guda kuma, hukumar gudanarwar Jami’ar MAAUN ta dage a kan cewa, za ta gudanar da bikin yadda ta riga ta tsara, wanda bai gamsu ba ya tafi kotu.
Mai mallakar Jami’ar MAAUN, Farfesa Abubakar Adamu Gwarzo, ya shaida wa wakilinmu cewa jami’ar za ta gudanar da taron bikin yaye ɗaliban nata kamar yadda ta tsara a cikin wannan wata na Disamba, 2025.
Ya jaddada cewa jami’ar zaman kanta take, don haka tana da ikon sanya kuɗin bikin yaye ɗalibanta.
A cewarsa, kuɗin da MAAUN ta sanya bai kai abin da wata jami’a mai zaman kanta a Jihar ba ta sanya, amma bai ambaci suna ba. Don haka ya kalubalanci Hukumar kan rashin dakatar da biyan kuɗaɗen a ɗaya jami’ar ba.
Ya ce, “Za mu gudanar da bikin a watan Disamba a kamar yadda muka tsara, kuma za mu gayyaci ’yan jarida su ɗauki rahoto.”
Wata wasiƙar ƙorafi a madadin ɗalibai ta nuna damuwa kan yunƙurin tattaunawa da ɗalibai a ɗaiɗaikunsu domin neman ragin kuɗin da jami’ar ta sanya.
Ta bayyana cewa wannan ya saɓa wa abin da aka tsara cewa tattaunawar za ta ƙunshi iyayen ɗalibai da hukumomin jami’ar da kuma wakilan gwamnati.
A yayin da iyaye ke jiran samun tabbacin tsarin da aka yi a hukumance, hukumar gudanarwar Jami’ar MAAUN ta nace cewa babu gudu, babu ja da baya wajen gudanar da taron kamar yadda ta riga ta tsara — duk wanda bai gamsu ba ya tafi kotu.