Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da amfani da Hijabi ga jami’an tsaro mata a fadin jihar.

Kwamishinan Yada Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu, Alhaji Sagir Musa Ahmed ne ya bayyana haka jim kadan bayan kammala taron majalisar zartarwa da aka gudanar a fadar gwamnatin  jihar da ke Dutse.

A cewarsa, majalisar ta bayar da umarni ga kamfanonin tsaro guda uku da ke aiki a jihar, su bai wa jami’an tsaro mata daga cikin matasa 9,969 da aka dauka aiki, damar sanya Hijabi yayin aiki, a matsayin girmamawa ga addini da al’adu.

Alhaji Sagir Musa Ahmed ya ce, wannan matsaya ta biyo bayan rahoton da kwamitin majalisar kan tsaron makarantu, asibitoci da kotuna ya gabatar, kuma aka sake jaddada kudurin gwamnatin na tabbatar da tsarin aiki mai cike da mutuntaka, da daidaito.

Ya ce, majalisar zartarwar ta kuma amince da kaddamar da makon kirkira da kere-kere na jihar (JISCIW) daga shekarar 2025.

Ya jaddada cewa, wannan tsari na nuna jajircewar gwamnatin wajen bunkasa basira da hazakar matasa, da kuma inganta kirkire-kirkire da tunani mai zurfi a fadin jihar.

Sagir ya bayyana cewa, JISCIW zai kara zaburar da matasa a fannoni daban-daban kamar fasaha, zane, kasuwanci da kuma harkokin fasaha.

Ya kara da cewa, majalisar ta amince da fitar da sama da Naira miliyan 516 domin sayen tikitin jirgi ga daliban jihar Jigawa 185 da ke karatu a fannin likitanci da kimiyyar kiwon lafiya a Jami’ar Near East dake kasar Cyprus, domin shirye-shiryen zangon karatu na shekarar 2024/2025.

Kwamishinan ya kara da cewa, wannan tallafi ya nuna yadda gwamnatin ke ci gaba da daukar nauyin ilimi da jin dadin daliban da ke karatu a kasashen waje, musamman a muhimman fannoni kamar likitanci da kiwon lafiya.

 

Usman Muhammad Zaria 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Tsaro: Na kan yi kuka duk lokacin da na ji an kashe wani — Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya ce gwamnati ce ke da alhakin samar da tsaro da haɗin kai a Jihar Filato da kuma Najeriya baki ɗaya.

Ya ce babu wata ƙasa da za ta shigo don kawo zaman lafiya na dindindin a Najeriya, face ’yan ƙasa sun haɗa kai.

’Yan Bindiga A Kano: Sanusi II ya ziyarci Faruruwa, ya buƙaci a tsaurara tsaro Ba da yawuna PDP ta kori Wike ba — Muftwang

Akpabio, ya yi wannan magana ne a filin Polo na Jos a ranar Asabar yayin taron tarbar sabbin mambobin da suka sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC a Jihar Filato.

Ya kira jama’a da su goyi bayan ƙoƙarin samar da zaman lafiya tare da yin aiki don ƙarshen rikice-rikece.

Ya ce Shugaba Bola Tinubu yana ƙoƙarin kawo ƙarshen kashe-kashe da tabbatar da zaman lafiya a Filato da sauran sassan ƙasar nan.

“Muna roƙon Allah Ya taimaka mana mu samu zaman lafiya a Filato. Duk wanda zai mulki Filato dole ne ya zama mutum mai kishin zaman lafiya. Wannan ita ce jam’iyyar da ta ke kula da ku,” in ji shi.

Akpabio, ya ƙara da cewa: “Na zo a madadin Shugaban Ƙasa domin tabbatar muku cewa za mu yi duk abin da ya kamata domin ku samu zaman lafiya.

“Babu wasu mutane daga waje da za su zo su kawo muku zaman lafiya. Dole mu ne za mu samar da shi. Dole mu zauna lafiya da juna. Najeriya na buƙatar zaman lafiya domin samun ci gaba.”

Ya tabbatar wa al’ummar Jihar Filato cewa gwamnati za ta magance matsalolin da suke fuskanta.

“Ina kuka a duk lokacin da na ji an kashe wani mutum; yaro ko babba. Matsalar da muke fuskanta ba yau ta samo asali ba.

“Mutane da dama sun mutu a Filato. An zubar da jini mai yawa, kuma ba mu farin ciki da haka. Shugaban Ƙasa ma ba ya farin ciki,” in ji shi.

Akpabio ya amince cewa da cewar ana kashe-kashe, tashe-tashen hankula a ƙasar nan, amma ya yi alƙawarin cewa nan da wani lokaci lamarin zai zama tarihi.

Ya roƙi al’ummar Filato da su goyi bayan Shugaba Tinubu da jam’iyyar APC, inda ya jaddada cewar za su samar da ci gaba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsaro: Na kan yi kuka duk lokacin da na ji an kashe wani — Akpabio
  •  An Amince Da  Sauye-sauye A Tsarin Mulkin Kasar Benin
  • ’Yan Bindiga A Kano: Sanusi II ya ziyarci Faruruwa, ya buƙaci a tsaurara tsaro
  • Gwamnatin Gombe ta bai wa alƙalai da Khadi-Khadi kyautar sabbin motoci 16
  • Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje
  • AU da MDD, sun karfafa dabarun tabbatar da zaman lafiya da tsaro
  • Mutum ɗaya ya rasu yayin da ’yan sanda da ’yan bindiga suka yi artabu a Kwara
  • Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa
  • Cin ganda na sa Najeriya tafka asarar $5bn — Gwamnatin Tarayya
  • Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci