Sojoji sun ceto mafiya 16 da aka yi garkuwa da wasu a Filato
Published: 15th, April 2025 GMT
Sojoji a Jihar Filato sun ceto wasu mutum 16 da ’yan bindiga suka yi garkuwa da su a kan titin Jos zuwa Mangu.
Dakarun Rundunar Operation Safe Haven ne suka ceto mutanen a cikin wata mota da a aka jefar da ita a yankin Mararabar Kantoma da ke Ƙaramar Hukumar Manngu.
Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar, Manjo Samson Zakhom, ya bayyana cewa an ceto mutanen ne da misalin ƙarfe 9 na dare bayan sun tsinci motar a daji babu kowa a ciki.
Ya ce ganin haka ne sojojin rundunar da ke aikin tabbatar da tsaro da zaman lafiya a jihar suka yi zargin sace fasinjojin cikinta aka yi.
An yi garkuwa da masu ibada a Kogi Yadda kisan mutum fiye da 50 a Filato ya tayar da ƙura NAJERIYA A YAU: Dalilan Rikice-Rikice A Jihar FilatoManjo Samson Zakhom ya ce sojojin suna tsaka da bincike sai ’yan bindigar suka buɗe musu wuta, inda bayan arangamar ɓata-garin suka tsere suka bar matafiyan.
Ya bayyana cewa, a cikin fasinjojin 16 da aka ceto har da ƙananan yara guda shida, kuma duk a ba sau taimakon farko saboda raunukan da suka samu, sannan muka raka su, suka ci gaba tafiyarsu.”
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Akwai buƙatar samar da sauyin zaman lafiya mai ɗorewa — Maryam Bukar
Sabuwar mai bada shawara kan harkokin lafiya ta Majalisar Ɗinkin Duniya, Maryam Bukar-Hassan (Alhan_islam) ta bayyana cewa samar da dauwamammen zaman lafiya a duniya shi ne fatansu.
Maryam ta bayyana hakan ne a lokacin da babban jami’in kula da ayyukan jin ƙai na Majalisar Ɗinkin Duniya a Nijeriya, Mohammed Malick Fall, ke maraba da ita a ofishin majalisar da ke Abuja.
An kama mai babur ɗauke da ƙoƙunan kan mutane a Ogun Gwamnati ta amince a kafa sabbin jami’o’i masu zaman kansu guda 9Mohammed ya jaddada muhimmancin samar da zaman lafiya, yana mai cewa zaman lafiya wani abu ne da ake buƙata don jin daɗin rayuwar ɗan Adam, kuma idan ba a same shi ba, ci gaban dimokuraɗiyya da kuma ’yancin ɗan Adam ba zai samu ba.
Ya bayyana damuwarsa kan yadda aka sake samun ɓullar tashe-tashen hankula a Nijeriya da ma duniya baki ɗaya, yana mai cewa hakan koma baya ne ga ci gaban da aka samu tun kafuwar MDD shekara 80 da suka gabata.
Da take nata jawabin Maryam Bukar Hassan ta ce, akwai buƙatar a samar da wani shiri na kawo sauyi wajen samar da zaman lafiya mai ɗorewa.
Har ila yau, Mohammed Fall ya yaba da yadda aka naɗa Maryam Bukar-Hassan a matsayin, ya ce hakan yazo a daidai lokacin da ya dace kuma mai mahimmanci, yana mai bayyana irin ƙarfin gwiwar da yake da shi akanta na za ta sauke nauyin da aka ɗora mata, mussaman wajen isa ga al’umma da matasa ta hanyoyin diflomasiya.
Yana mai cewa, “Ku ne muryar matasa, muryar jagorancin mata,” in ji shi. Ya kuma jaddada irin rawar da taka wajen tsara makomar neman zaman lafiya.
Ya kuma bayyana cewa, nauyin da ke kanta ya yi fice a Nijeriya har zuwa ayyukan da duniya ke yi. Duk da irin rawar da take takawa a duniya, Fall ya ba ta tabbacin goyon bayan Majalisar Ɗinkin Duniya.
Hakazalika Maryam Bukar-Hassan ya jaddada cewa, idan har ba zaman lafiya ba, yadda za a iya cimma muradun ci gaba mai ɗorewa (SDGs) kuma zai kasance mara amfani.
“Ba maganar talauci idan zaman lafiya da yin adalci sun tabbata,” in ji ta,
Ta kuma ƙara da cewar, tabbatar da yunƙurin zaman lafiya ta hanyar haɗa harsunan asalin ƙabilu da al’adu na gargajiya ne fatanmu dole mu haɗa da harshen Ingilishi,” in ji ta.
Idan har muna son mu kai ga cimma nasara dole ne, mu komo hanyar yadda da al’ummominmu suka tsara. Wannan hanya na nufin tabbatar da gina zaman lafiya mai ɗorewa, musamman a yankunan da asalin al’adu ke taka muhimmiyar rawa a cikin zamantakewa.