Sojoji sun ceto mafiya 16 da aka yi garkuwa da wasu a Filato
Published: 15th, April 2025 GMT
Sojoji a Jihar Filato sun ceto wasu mutum 16 da ’yan bindiga suka yi garkuwa da su a kan titin Jos zuwa Mangu.
Dakarun Rundunar Operation Safe Haven ne suka ceto mutanen a cikin wata mota da a aka jefar da ita a yankin Mararabar Kantoma da ke Ƙaramar Hukumar Manngu.
Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar, Manjo Samson Zakhom, ya bayyana cewa an ceto mutanen ne da misalin ƙarfe 9 na dare bayan sun tsinci motar a daji babu kowa a ciki.
Ya ce ganin haka ne sojojin rundunar da ke aikin tabbatar da tsaro da zaman lafiya a jihar suka yi zargin sace fasinjojin cikinta aka yi.
An yi garkuwa da masu ibada a Kogi Yadda kisan mutum fiye da 50 a Filato ya tayar da ƙura NAJERIYA A YAU: Dalilan Rikice-Rikice A Jihar FilatoManjo Samson Zakhom ya ce sojojin suna tsaka da bincike sai ’yan bindigar suka buɗe musu wuta, inda bayan arangamar ɓata-garin suka tsere suka bar matafiyan.
Ya bayyana cewa, a cikin fasinjojin 16 da aka ceto har da ƙananan yara guda shida, kuma duk a ba sau taimakon farko saboda raunukan da suka samu, sannan muka raka su, suka ci gaba tafiyarsu.”
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Juyin Mulki: ECOWAS ta ayyana dokar ta-baci a kasashenta
Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) ta ayyana dokar ta-baci a yankin, kwana biyu bayan yunkurin juyin mulki da bai yi nasara ba a kasar Jamhuriyar Benin.
Shugaban Hukumar ECOWAS, Omar Touray, ne ya sanar da haka a yayin zaman majalisar tsaro ta hukumar karo na 55 a Abua.
Touray ya ce daukar matakin ya zama dole domin shawo kan barazanar da juyin mulki ke wa tsarin dimokuradiyya a yankin, wanda ke bukatar matakan zuba jari na gagagwa domin tabbatar da tsaron al’umma.
A yayin jawabinsa ga ministoci da manyan jami’an gwamnati da ke halartar taron, ya bayyana yadda yawaitar samun juyin mulki a Yammacin Afirka ke barazana ga tsaro da zaman lafiya a yankin.
Sojoji sun kashe ’yan bindiga 13, sun ceto ’yan kasuwa a Sakkwato HOTUNA: Yadda dalibai 100 da aka sace a Neja suka dawoYa ce, “Babban barazana ga yankinmu sun haɗa da ci gaba da katsalandan na sojoji (kamar yadda aka gani kwanan nan a Guinea-Bissau da Jamhuriyar Benin); rashin bin ka’idojin sauyin mulki a Guinea inda shugaban soja ke ƙoƙarin zama farar hula; raguwar damar shiga zabe a ƙasashe da dama; ƙara karfin ’yan ta’adda, kungiyoyi masu laifi da ke dauke da makamai; da kuma matsin lamba na siyasar duniya da ke shafar diflomasiyya da haɗin kan ƙasashen mambobi.”
Touray ya jaddada cewa “zabe ya zama babban abin da ke tayar da rikici a cikin al’ummarmu.”
Ya kuma ambaci yunƙurin juyin mulki da aka yi kwanan nan da tattaunawa da ƙasashen AES (Burkina Faso, Mali da Nijar) da suka fice daga ECOWAS, yana mai nanata bukatar gaggawa ta haɗin gwiwar yankin wajen yaki da ta’addanci da laifukan da ke ketare iyaka.
Ya bayyana lamarin a matsayin abin da bai taɓa faruwa ba, yana gargadi da cewa, “Idan aka dubi wannan hali, ya dace mu bayyana cewa al’ummarmu tana cikin yanayin gaggawa.”
Touray ya bukaci a riƙa yin taron Majalisar Sulhu da Tsaro akai-akai a shekara mai zuwa, yana mai cewa ECOWAS dole ta “haɗa ƙarfi da ƙarfi don fuskantar barazanar ta’addanci da ’yan fashi, waɗanda ba sa mutunta iyakokin ƙasashe.”
Ya kuma bayyana muhimman wuraren da ministoci za su riƙa kula da su, ciki har da rikicin Guinea-Bissau, tafiyar da sauyin mulki, magance ƙara yawaitar cire mutane daga siyasa, da kuma kare haɗin kan yankin daga matsin lamba na waje.