Aminiya:
2025-11-17@05:58:56 GMT

Sojoji sun ceto mafiya 16 da aka yi garkuwa da wasu a Filato

Published: 15th, April 2025 GMT

Sojoji a Jihar Filato sun ceto wasu mutum 16 da ’yan bindiga suka yi garkuwa da su a kan titin Jos zuwa Mangu.

Dakarun Rundunar Operation Safe Haven ne suka ceto mutanen a cikin wata mota da a aka jefar da ita a yankin Mararabar Kantoma da ke Ƙaramar Hukumar Manngu.

Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar, Manjo Samson Zakhom, ya bayyana cewa an ceto mutanen ne da misalin ƙarfe 9 na dare bayan sun tsinci motar a daji babu kowa a ciki.

Ya ce ganin haka ne sojojin rundunar da ke aikin tabbatar da tsaro da zaman lafiya a jihar suka yi zargin sace fasinjojin cikinta aka yi.

An yi garkuwa da masu ibada a Kogi Yadda kisan mutum fiye da 50 a Filato ya tayar da ƙura NAJERIYA A YAU: Dalilan Rikice-Rikice A Jihar Filato

Manjo Samson Zakhom ya ce sojojin suna tsaka da bincike sai ’yan bindigar suka buɗe musu wuta, inda bayan arangamar ɓata-garin suka tsere suka bar matafiyan.

Ya bayyana cewa, a cikin fasinjojin 16 da aka ceto har da ƙananan yara guda shida, kuma duk a ba sau taimakon farko saboda raunukan da suka samu, sannan muka raka su, suka ci gaba tafiyarsu.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Garkuwa Matafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Wasu kasashen duniya sun nuna damuwa game da tsarin mulkin bayan yakin Gaza

Rasha, China, da wasu kasashen Larabawa da dama sun nuna damuwa game da tsarin mulkin bayan yaki da kuma rashin wani muhimmin matsayi ga Hukumar Falasdinu bayan yakin Gaza da aka gabatar a daftarin kudirin shirin tsagaita wuta na Shugaba Donald Trump na Amurka.

Duk da cewa jami’an diflomasiyyar kasashen sun yarda cewa tattaunawa ta kai ga cimma yarjejeniyar, amma rarrabuwar kawuna tsakanin Washington da wasu membobin kwamitin tsaron na Majalisar Dinkin Duniya, bayan fiye da shekaru biyu na kisan kare dangi.

Sakataren Harkokin Wajen Amurka Marco Rubio ya ce ya kamata a amince da kudurin nan take, yana mai jaddada bukatar gaggauta amincewa da shirin.

Daftarin farko na Amurka, wanda aka rarraba a makon da ya gabata, ya yi kira da a samar da babban mataki da zai bai wa rundunar kasa da kasa damar aiki a Gaza har zuwa 2027 tare da wata Hukumar Zaman Lafiya, wadda har yanzu ba a kafa ta ba.

Kasashen Larabawa wadanda suka nuna sha’awar bayar da gudummawar sojoji sun ce irin wannan izini yana da mahimmanci.

Rasha, China, da Aljeriya sun yi watsi da daftarin.

Mahimman abubuwan da ke kawo tarnaki ga shirin su ne rashin wata hanya bayyananna ga samar da kasar Falasdinu da rashin tabbas game da lokacin da sojojin Isra’ila za su janye daga Gaza.

Rasha ta gabatar da nata kudirin kan Gaza, tana kalubalantar kokarin Amurka na ganin Kwamitin Tsaro ya amince da shirin zaman lafiya na Shugaba Donald Trump kan Gaza, a cewar kwafin daftarin da Reuters ta samu gani.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kwamitin Tsaro ya tsawaita da shekara guda wa’adin aikin tawagar MDD a Afrika ta Tsakiya November 14, 2025 Tehran da Ankara sun jaddada muhimmancin zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin November 14, 2025 Iran ta yi tir da G7 kan goyon bayan takunkuman Amurka November 14, 2025 Iran da China na bunkasa alakoki da hadin gwiwa a tsakaninsu November 14, 2025 Abdoulaye Diop: ‘Yan Tawaye Ba Za Su Iya Mamaye Dukkan Kasar Mali Ba November 14, 2025 Ramaphosa Ya Caccaki Trump Kan Kauracewa Taron G20 A Johannesburg November 14, 2025 MDD ta nuna damuwa game da rahotannin kisan gilla a El Fasher November 14, 2025 Rasha Ta yi Gargadin Mayar Da Martani Mai Tsanani Kan Amurka November 13, 2025 Iran Da Qatar Sun Tattauna Kan Dangantakar Dake Tsakaninsu November 13, 2025 Yahudawa Yan Share Wuri Zauna Sun Kona Masallaci A Yammacin Kogin Jodan November 13, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su
  • Tsaro: Na kan yi kuka duk lokacin da na ji an kashe wani — Akpabio
  • Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan
  • Babu Janar ɗin da ISWAP ta kama a Borno — Sojoji
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda, sun kama mutum 94
  • Mayaƙan ISWAP sun sace Janar sun kashe sojoji a Borno
  • Yadda ’yan bindiga suka kashe banga 16 suka sace mutane 42 a Neja
  • ’Yan bindiga sun kashe ’yanga 16 sun sace mutane 42 a Neja
  • Wasu kasashen duniya sun nuna damuwa game da tsarin mulkin bayan yakin Gaza
  • Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci