Yayin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ke ziyarar aiki a Vietnam, shugaban CMG Shen Haixiong, ya kulla yarjejeniyoyin hadin gwiwa da shugaban gidan radiyon Vietnam Nguyen Thanh Lam, da shugaban gidan rediyon na Voice of Vietnam Do Tien Sy, kana da shugaban kwalejin yada labarai da fadakarwa na Vietnam Pham Minh Son, a gaban shugabannin kasashen biyu wato Xi Jinping da Tô Lâm.

(Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Troost-Ekong ya gargaɗi Super Eagles kan wasan da za ta fafata da Gabon

Kyaftin ɗin tawagar Super Eagles ta Najeriya, William Troost-Ekong, ya gargaɗi ’yan wasan ƙasar da su guji tafka kura-kurai a wasan da za su buga da Gabon a ranar Alhamis.

Ekong ya yi wannan gargaɗi ne kafin fara atisayen ’yan wasan a safiyar Talata, a yayin da suke ci gaba da shirin fafatawar neman gurbin shiga Kofin Duniya na 2026.

Wike: Za mu kare duk wani soja da ke aiki bisa doka — Ministan Tsaro ’Yan sanda sun kama mutum 14 kan zargin ta’amali da miyagun ƙwayoyi a Jigawa

Super Eagles za ta kece raini da Panthers of Gabon a wasan da ake sa ran zai kasance mai matuƙar muhimmanci wanda shi zai tabbatar da matsayin Najeriya na samun tikitin babbar gasar tamaula.

A nasa bangaren, mai horar da tawagar Najeriya, Eric Chelle, ya yaba da kishin da ’yan wasan ke nunawa wajen ganin sun kai ƙasar zuwa gasar Kofin Duniya.

A bayan nan ne aka ruwaito cewa, tawargar ta Super Eagles ta ƙaurace wa atisaye a ranar Talata a birnin Rabat a ƙasar Morocco, kwana biyu kafin wasan neman gurbin shiga gasar Kofin Duniya ta 2026 da za su yi da Gabon.

’Yan wasa da jami’ai sun yi zanga-zangar rashin biyan haƙƙoƙinsu, ciki har da kudin alawus da ladan buga wasanni da suke bi tun daga shekarar 2019.

Ƙungiyar, wadda ke da manyan ’yan wasa kamar Victor Osimhen, Alex Iwobi, da Ademola Lookman, na neman hukumar ƙwallon ƙafa ta ƙasa (NFF) ta warware wannan matsalar biyan kuɗin cikin gaggawa.

Wannan lamarin ya jefa shakku kan shirin Super Eagles, yayin da aka tsara za ta fuskanci Gabon ranar Alhamis a filin wasa na Moulay Hassan Stadium da ke Rabat.

Har yanzu NFF ba ta fitar da cikakken bayani ga jama’a ba, amma majiyoyi sun tabbatar cewa ana gudanar da tattaunawa cikin gaggawa don kawo mafita.

Rahotanni sun ce bashin da suke bi ya haɗa da ƙudin alawus na wasannin neman shiga AFCON 2025 da kuma karawar neman shiga Kofin Duniya 2026.

Najeriya ta gaza samun tikitin shiga Gasar Cin Kofin Duniya ta 2022 da aka yi a Qatar, kuma yanzu tana shan matsin lamba daga masu bibiyar tamaula a ƙasar, domin ta dawo da martabarta a duniya.

Sakamakon wasan da za ta kara da Gabon zai iya tantance makomar Super Eagles a neman shiga gasar kofin duniya da za a yi a Amurka da Canada da kuma Mexico a 2026.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kafa Cibiyar Kiwon Lafiya Ta Hadin Gwiwa Ta Farko Tsakanin Sin Da Afirka A Guinea
  • Nijeriya za ta kece raini da Gabon a wasan neman tikitin Kofin Duniya
  • Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2
  • An gano motar da aka sace a Gidan Gwamnatin Kano
  • Troost-Ekong ya gargaɗi Super Eagles kan wasan da za ta fafata da Gabon
  • Majalisar Jihar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Kan Laifin Rashin Ɗa’a
  • Majalisar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Bisa Zargin Rashin Ɗa’a
  • Gabon: An Daure Mata Da ‘Dan  Tsohon Shugaban Kasa Bongo Shekaru 20 A Gidan Yari
  • Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna
  • Gaza : Isra’ila ta karya yarjejeniyar tsagaita wuta sau 282 tun bayan aiwatar da ita