Kwamishinan ‘Yansandan Kano Ya Nemi Taimakon Sarakunan Gargajiya Wajen Kawo Ƙarshen Faɗan Daba A Jihar
Published: 15th, April 2025 GMT
Ya ce sama da mutane 150 ne aka kama da laifin faɗan ɗaba da tashin hankali, tare da ƙwato makamai, miyagun ƙwayoyi da kayan sata.
Ya ƙara da cewa matsalolin faɗan ɗaba da shaye-shaye barazana ce ga zaman lafiyar jama’a da makomar matasa.
Duk da yake kame na da muhimmanci, Bakori ya ce dole ne a bai wa matasa damar samun ilimi, koyon sana’o’i da kuma wasu ayyuka da za su riƙa shagaltar da su zuwa hanya mafi dacewa.
Ya kuma shawarci shugabannin ‘yansanda na ƙananan hukumomi da su riƙa haɗa kai da sarakunan gargajiya da al’ummar yankinsu wajen gano matsalolin tsaro a yankunansu.
“Idan muka haɗa kai da goyon bayan jama’a, babu yadda ‘yan daba za su ci gaba da addabar Kano,” in ji CP Bakori.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Yansanda Faɗan Daba Kwamishina
এছাড়াও পড়ুন:
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Karatun Baya Dangane Da Tarihi Shi Ne Abun Da Ya Kamaci Japan
CGTN ta gabatar da kuri’un jin ra’ayin jama’ar ne ta harsunan Turancin Ingilishi, da Sifaniyanci, da Faransanci, da Larabci, da harshen Rasha. Inda masu bayyana ra’ayoyi 10,451 suka fayyace mahangarsu cikin sa’o’i 24. (Mai fassara: Saminu Alhassan)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA