Matashi ya yi yunƙurin soka wa mahaifinsa makami a Kano
Published: 15th, April 2025 GMT
Kotu ta yanke wa wani matashi hukuncin ɗaurin shekara biyu a gidan yari kan laifin yunƙurin soka wa mahaifinsa makami a unguwar Fagge da ke Jihar Kano.
Kotun da ke zamanta a yankin Mai Alluna ta yanke wa matashin hukuncin ne bayan bayan alƙali ya kama shi da laifin yunƙurin soka wa mahaifinsa almakashi saboda ya hana shi kuɗin kashewa.
’Yan sanda sun gurfanar da matashin ne a kan laifin ɗura ashariya da barazanar kisa da kuma ɗaukar makami ba bisa ka’ida ba.
Bayan karanta masa takardar tuhumar, matashin ya amsa laifin, inda Alƙali Nasir Ahmad ya yanke masa hukuncin ɗaurin shekara biyu da tarar Naira dubu 20, da kuma karin ɗaurin wata shida tare da bulala 40.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Mutum biyu sun mutu a harbin bindiga a Jami’ar Brown ta Amurka
Jami’ar Brown a Amurka ta ba da rahoton mutuwar mutum biyu, tare da jikkatar guda tara dake cikin tsanani a harbin da aka yi a makarantar.
An ruwaito cewa mutane da yawa sun jikkata a harbin da aka yi kusa da harabar Ivy League da ke Rhode Island.
Hukumomi yankin sun bukaci jama’a da su ci gaba da kasancewa a kulle yayin da maharin ya tsere.
“Zan iya tabbatar da cewa akwai mutane biyu da suka mutu da yammacin yau, kuma akwai wasu mutane takwas da ke cikin mawuyacin hali, kodayake basu cikin damuwa sosai,” in ji Magajin Garin Brett Smiley, a wani taron manema labarai.
“Muna amfani da duk wata hanya da za mu iya don gano maharin in ji Mataimakin Shugaban ‘Yan Sanda Timothy O’Hara.
Wannan harbin shi ne na baya-bayan nan a cikin jerin hare-haren makarantu a Amurka, inda yunkurin takaita damar malllakar makamai cikin sauki ke fuskantar kalubalen siyasa.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Shugabannin kasashen (ECOWAS) na taro a Abuja December 14, 2025 Kasashen AES zasu kafa bankin dogaro da kai December 14, 2025 Sheikh Na’im Kassim: Idan Duniya Baki Daya Za Ta Taru, Ba Wanda Zai Iya Kwace Makaman Hizbullah December 13, 2025 DRC: Kungiyar M23 Ta Kwace Iko Da Wani Gari Mai Muhimmanci December 13, 2025 Syria: Sojojin “Isra’ila” Sun Kutsa Cikin Yankin Qunaidhara December 13, 2025 Kalibaf: Iran Da Habasha Suna Bunkasa Alakokin Siyasa Da Tattalin Arziki December 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 171 December 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 170 December 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 169 December 13, 2025 Isra’ila Ta Kai Hari A Kudancin Labanon A Ci Gaba Da Keta Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta December 13, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci