Aminiya:
2025-11-22@18:03:18 GMT

Matashi ya yi yunƙurin soka wa mahaifinsa makami a Kano

Published: 15th, April 2025 GMT

Kotu ta yanke wa wani matashi hukuncin ɗaurin shekara biyu a gidan yari kan laifin yunƙurin soka wa mahaifinsa makami a unguwar Fagge da ke Jihar Kano.

Kotun da ke zamanta a yankin Mai Alluna ta yanke wa matashin hukuncin ne bayan bayan alƙali ya kama shi da laifin yunƙurin soka wa mahaifinsa almakashi saboda ya hana shi kuɗin kashewa.

’Yan sanda sun gurfanar da matashin ne a kan laifin ɗura ashariya da barazanar kisa da kuma ɗaukar makami ba bisa ka’ida ba.

Bayan karanta masa takardar tuhumar, matashin ya amsa laifin, inda Alƙali Nasir Ahmad ya yanke masa hukuncin ɗaurin shekara biyu da tarar Naira dubu 20, da kuma karin ɗaurin wata shida tare da bulala 40.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar Hisbah Ta Rufe Wani Wuri da Ake Zargin Ana Aikata Badala A Kano

Daga  Khadijah Aliyu 

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama wasu samari bakwai da ke shiga irin ta mata da aikata badala a wani shahararren gurin nishadi da ke kan titin Zoo Road a karamar hukumar Kano Municipal.

Yayin tabbatar da faruwar lamarin ga Rediyon Nijeriya, Mataimakin Kwamanda Janar na hukumar Hisbah, Sheikh Mujahid Aminudeen Abubakar, ya ce an kama samarin da ke kasa da shekaru 23 bayan samun bayanan sirri daga wani mai kishin ƙasa.

Mai bayar da bayanan ya sanar da cewa mmatasn da aka fi sani da ‘Yan Daudu, suna yawan zuwa wurin, inda ake zargin cewa motocin mutane daban-daban ke zuwa su ɗauke su.

Sheikh Mujahid ya bayyana cewa binciken farko ya nuna cewa matasan sun fito ne daga jihohin Kogi, Bauchi da Kano.

Ya ƙara da cewa yayin gudanar da aikin, jami’an Hisbah sun kuma kama wani saurayi da wata budurwa da aka same su tare a cikin babur mai ƙafafu uku, sannan kuma an gano wata yarinya da aka ce ta bace a Sakkwato, aka kuma maida ta ga iyayenta.

Mataimakin Kwamanda Janar din ya ƙara da cewa hukumar za ta rufe wurin nishadin saboda zargin  ɓoye ƙananan yara da ke aikata munanan ayyuka.

Ya ce za a mika matasan da aka kama tare da masu kula da wurin ga hukumomin da suka dace domin ci gaba da daukar mataki.

Sheikh Mujahid ya tabbatar da jajircewar Hisbah na kawar da dukkan nau’o’in munanan dabi’u a jihar, tare da kira ga jama’a da su rika kai rahoton duk wata matsala ko abin da suke shakku ga hukumar Hisbah ko wasu hukumomi da suka dace.

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Obi ya yi watsi da hukuncin ɗaurin rai da rai da aka yi wa Kanu
  • Dalibai a Jihohin Arewa Maso Yamma Sun Koka Game da Ƙalubalen Tsaro a Yankin
  • Hukumar Hisbah Ta Rufe Wani Wuri da Ake Zargin Ana Aikata Badala A Kano
  • Iyalan Waɗanda Aka Kashe Yayin Zanga-zangar Bangladesh Sun Yi Maraba Da hukuncin Kisan Tsohuwar Firaminstar
  • Sai da Kwankwaso APC za ta iya samun nasara a 2027 — NNPP
  • Kotu Ta Yanke Wa Nnamdi Kanu Hukuncin Zaman Kurkuku Na Har Abada  Akan Laifin Ta’addanci
  • An yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin ɗaurin rai da rai
  • Kotu ta sami Nnamdi Kanu da laifukan ta’addanci
  • Achraf Hakimi Ya Zama Gwarzon Wasan Kwallon Kafar Afirka Na Shekara Ta 2025
  • Yadda maganin sauro ya yi ajalin magidanci da iyalinsa a Kano