Matashi ya yi yunƙurin soka wa mahaifinsa makami a Kano
Published: 15th, April 2025 GMT
Kotu ta yanke wa wani matashi hukuncin ɗaurin shekara biyu a gidan yari kan laifin yunƙurin soka wa mahaifinsa makami a unguwar Fagge da ke Jihar Kano.
Kotun da ke zamanta a yankin Mai Alluna ta yanke wa matashin hukuncin ne bayan bayan alƙali ya kama shi da laifin yunƙurin soka wa mahaifinsa almakashi saboda ya hana shi kuɗin kashewa.
’Yan sanda sun gurfanar da matashin ne a kan laifin ɗura ashariya da barazanar kisa da kuma ɗaukar makami ba bisa ka’ida ba.
Bayan karanta masa takardar tuhumar, matashin ya amsa laifin, inda Alƙali Nasir Ahmad ya yanke masa hukuncin ɗaurin shekara biyu da tarar Naira dubu 20, da kuma karin ɗaurin wata shida tare da bulala 40.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kano ta haramta kafa hukumar Hisbah mai zaman kanta
Gwamnatin Jihar Kano, ta haramta kafa Hukumar Hisbah mai zaman kanta tana, wadda tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje, yake ƙoƙarin kafawa.
Gwamnatin ta ce kafa hukumar ya saɓa da doka, kuma zai iya zama barazana ga zaman lafiya a jihar.
Zan yi amfani da Salah a wasan Liverpool da Brighton — Arn Slot Zaɓen 2027 ya hana ni korar wasu ma’aikata – BagoA cikin wata takarda da Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya sanya hannu a ranar 8 ga watan Disamba, 2025, gwamnatin ta ce ta gano an fara ɗaukar mutane aiki a hukumar ba tare da neman izini ba.
Gwamnatin ta ce hakan ya saɓa wa Dokar Hukumar Hisbah ta Jihar Kano.
Da yake zantawa da ’yan jarida, Kwamishinan YaɗaLabarai da Harkokin Cikin Gida na jihar, Ibrahim Abdullahi Waiya, ya ce Hukumar Hisbah ce kaɗai doka ta amince da ita wajen gudanar da ayyuka a jihar.
Ya ce kafa wata ƙungiya ko hukuma ta daban ba bisa ƙa’ida ba na iya kawo cikas ga zaman lafiya.
Umarnin ya bayyana cewa babu wani mutum ko ƙungiya da ke da ikon ɗaukar mutane aiki, tara su, horas da su ko tura su domin kafa wata hukumar Hisbah mai zaman kanta a jihar.
Gwamna Abba, ya kuma ayyana ayyukan hukumar a matsayin haramtattu, tare da gargaɗin cewa duk wanda ya yi amfani da kayan Hisbah, alamominta ko ikonta ba tare da izini ba zai fuskanci hukunci.
Gwamnan, ya umarci jami’an tsaro, ciki har da ’Yan Sanda, DSS, NSCDC, da sauran hukumomin tsaro, da su binciki waɗanda suka kafa sabuwar hukumar.
Gwamnatin ta kuma gargaɗi jama’a cewa duk wanda ya shiga, ya goyi baya ko ya haɗa kai da sabuwar hukumar, zai fuskanci hukunci.
An shawarci waɗanda aka ɗauka aiki su fice daga hukumar nan take tare da komawa ofishin Hisbah, ko Ƙaramar Hukuma.
Umarnin ya kuma tanadi hukunci ga waɗanda suka saɓa wa dokar, ciki har da gurfanar da su a gaban kotu bisa laifin gudanar da taro ba bisa ƙa’ida ba, kwaikwayon hukumomin gwamnati, da kafa rundunar tsaro ba tare da neman izini ba.
Wannan umarni ya fara aiki nan take, kuma za a yaɗa shi a kafofin watsa labarun Gwamnatin Jihar Kano.