HausaTv:
2025-12-02@20:42:39 GMT

Rundunar “Gulani” Ta Shiga Sahun Masu Kin Amincewa Da Yaki

Published: 15th, April 2025 GMT

A kalla tsoffin sojojin rundunar “Gulani” ta HKI 150 ne su ka rattaba hannu akan takardar yin kira da a dawo da fursunoni gida daga Gaza.

Ita dai rundunar “Gulani” ce mafi karf a tsakanin rudunonin sojan HKI,kuma tun da aka kafa ta, ta shiga dukkanin yake-yaken da HKI ta yi.

Wadanda su ka rattaba hannu akan wasikar sun bayyana goyon bayansu ga wasikar da sojan sama su ka rubuta a ranar 9 ga watan Aprilu da ake ciki,ko da kuwa sakamakon hakan shi ne kawo karshen yaki.

A cikin sa’o’i 48 da su ka gabata,dubban sojojin HKI sun rattaba hannu akan wasika wacce take yin kira da a kawo karshen yakin Gaza da kuma dawo da fursunonin da suke can.

A ranar juma’ar da ta gabata kafafen watsa labaru HKI sun ambaci cewa, da akwai sojojin bayan fage 1000 da su ka rattaba hannu akan wasika, da kuma tsofaffin sojojin soja a tsakaninsu da akwai wadanda suna kan ganiyar aikinsu.

Bayan wannan ne kuma sojojin dake kula da motocin yaki da tankoki su 15,25 su ka bi bayansu, sai kuma wasu tsoffin sojojin sama Jannati ,haka nan kuma sojan ruwa da likitocin soja 100. A cikin kwanaki  kadan da su ka gabata ma dai wasu jami’an daga cikin tsoffin ma’aikatan kungiyar leken asirin soja sun shiga cikin masu rubuta wasikar.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: rattaba hannu akan

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan ta’adda sun kashe ɗan sanda a gidan DPO a Jigawa

An kashe wani ɗan sanda a wani mummunan hari da ’yan bindiga suka kai gidan Babban Jami’in Ɗan Sanda (DPO) mai kula Babba Ofishin ’Yan Sanda da ke Aujara a Ƙaramar Hukumar Jahun ta a Jihar Jigawa.  

Da misalin ƙarfe 4:00 na asuba, ranar 25 ga Nuwamba, 2025, ne wasu ’yan bindiga suka kai farmaki gidan DPO na Babban Ofishin ’Yan Sandan.

Sanarwar rundunar ’yan sanda ta Jihar Jigawa ta bayyana cewa jami’an tsaro da ke gadin gidan sun yi ƙoƙarin dakile harin, inda aka samu musayar wuta.

A yayin arangamar, biyu daga cikin jami’an sun samu munanan raunuka, aka garzaya da su asibiti domin samun kulawa.

Tinubu ya gana da Janar Christopher Musa bayan Ministan Tsaro ya yi murabus An kama ’yan bindiga 4 a Kano

Washegari, ɗaya daga cikin waɗanda suka ji rauni ya rasu a sakamakon tsananin raunukan da ya samu.

Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Jigawa, Ɗahiru Muhammad, ya yi ta’aziyya ga iyalan mamacin da abokan aikinsa, yana mai tabbatar da cewa rundunar ta fara bincike na musamman domin kamo waɗanda suka aikata wannan ta’addanci.

Bayan harin, rundunar ta ƙara tsaurara matakan tsaro ta hanyar yawaita sintiri da sanya ido a Aujara da maƙwabtan garuruwan domin hana sake faruwar irin wannan barazana.

Kakakin rundunar, SP Shiisu Lawan Adam, ya roƙi al’umma da su kwantar da hankalinsu tare da ci gaba da ba da sahihan bayanai ga jami’an tsaro domin taimaka wa binciken da ake yi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sharhi:’HKI tana fama da karancin sojojin a dukkan rassan sojojin kasar’.
  •  Palasdinu: Sojojin “Isra’ila” 3 Su Ka Jikkata Sanadiyyar  Taka Su Da Mota
  • Aljeriya: Taron Kasashen Afirka Kan Amincewa Da Mulkin Mallaka A Matsayin Laifi
  • ’Yan ta’adda sun kashe ɗan sanda a gidan DPO a Jigawa
  • MAAUN: Ƙungiyar iyaye ta musanta zargin ƙara ƙudin yaye ɗalibai a jami’ar
  • Gwamnatin Kano Ta Kara Jaddada Dokar Haramcin Yin Haya da Babur a Jihar
  • ’Yan bindiga sun sace fasto da matarsa  masu ibada a Kogi 
  • Lebanon: Wasikar Kungiyar Hizbullah Ga Paparoma
  •  Kasar Ireland Ta Sauya Sunan Shugaban  “Isra’ila” Da Na Shahidiyar Falasdinu
  •  Sau 590 “Isra’ila” Ta Keta Tsagaiwa Wutar Yaki