HausaTv:
2025-04-30@18:45:22 GMT

Daruruwan ‘Yan Share Wuri Zauna Sun Kutsa Masallacin Kudus

Published: 15th, April 2025 GMT

A jiya Litinin daruruwan yahudawa ‘yan share wuri zauna sun kutsa cikin masallacin kudus, suna masu bayar da take na tsokana ga Musulmi. Har ila yau ‘yan share wuri zauna din sun kuma gudanar da na’u’oin ibadu na addinin yahudanci a cikin farfajiyar masallacin na Kudus.

Ma’aikatar  da take kula da wuraren ‘wakafi’ na musulunci, ta bayyana cewa; Adadin yahudawa ‘yan share wuri zauna din da su ka kutsa cikin masallacin na Kudus sun kai 765,kuma ‘yan sanda sun rika yi musu rakiya.

A lokaci daya kuma jami’an tsaron na ‘yan sahayoniya sun tsaurara matakan kuntatawa Falasdinawa masu shiga cikin masallacin na Kudus domin yin salla.

Wannan tsokanar ta ‘yan share wuri zauna a masallacin Kudus, tana faruwa ne a lokacin da a can yammacin kogin Jordan, yahudawan suke lalata gonakin Falasdinawa da kankare kasar gonakin ta hanyar amfani da manyan motoci na buldoza.

Har ila yau ‘yan sandan HKI sun kutsa cikin garuruwa da dama na Falasdinawa a yammacin kogin Jordan, inda su ka kama mutane da dama. Haka nan kuma sanadiyyar  harbe-harebn da su  ka yi, sun jikkata Falasdinawa 4 a sansanin Jalzuna dake arewacin birnin Ramallah.

A birnin Tubas kuwa ‘yan sahayoniyar sun kutsa cikin unguwanni mabanbanta tare da tilastawa mazauna wasu unguwanni da su fice daga cikin gidajensu. Kwamitin al’umma na Falasdinu a yankin ya sanar da cewa  a tsawon lokacin yaki adadin Falasdinawan da aka tilastawa ficewa daga cikin gidajensu, sun kai dubu 3 da 227.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: yan share wuri zauna

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Mutum 8 Da Bam A Borno

Wata majiya kuma ta bayyana cewa adadin mutanen da suka mutu na iya fin haka, duba da yawan mata da yara da lamarin ya rutsa da su.

A lokacin haɗa wannan rahoto, hukumomin soji da ‘yansanda ba su fitar da wata sanarwa ba dangane da lamarin ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga , Sun Ceto Fasinjoji 6 A Taraba
  •  Falasdinawa 40 Sun Yi Shahada A Cikin Sa’oi 24 A Gaza
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Na Iran Ya Ce: Maganar ‘Yan Sahayoniyya Rudu Ne Maras Amfani
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Quneitra Na Kasar Siriya Tare Da Kafa Shingen Bincike
  • Boko Haram Sun Hallaka ‘Yan Zaman Makoki 7, Sun Jikkata Wasu A Borno
  • HKI Tana Amfani Yunwa A Matsayin Makamin Yaki  A Kan Falasdinawa A Gaza
  • ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Mutum 8 Da Bam A Borno
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Jaddada Wajabcin Komawa Kan Shirin Tsagaita Bude Wuta A Gaza
  • Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara