HausaTv:
2025-12-09@07:05:58 GMT

Daruruwan ‘Yan Share Wuri Zauna Sun Kutsa Masallacin Kudus

Published: 15th, April 2025 GMT

A jiya Litinin daruruwan yahudawa ‘yan share wuri zauna sun kutsa cikin masallacin kudus, suna masu bayar da take na tsokana ga Musulmi. Har ila yau ‘yan share wuri zauna din sun kuma gudanar da na’u’oin ibadu na addinin yahudanci a cikin farfajiyar masallacin na Kudus.

Ma’aikatar  da take kula da wuraren ‘wakafi’ na musulunci, ta bayyana cewa; Adadin yahudawa ‘yan share wuri zauna din da su ka kutsa cikin masallacin na Kudus sun kai 765,kuma ‘yan sanda sun rika yi musu rakiya.

A lokaci daya kuma jami’an tsaron na ‘yan sahayoniya sun tsaurara matakan kuntatawa Falasdinawa masu shiga cikin masallacin na Kudus domin yin salla.

Wannan tsokanar ta ‘yan share wuri zauna a masallacin Kudus, tana faruwa ne a lokacin da a can yammacin kogin Jordan, yahudawan suke lalata gonakin Falasdinawa da kankare kasar gonakin ta hanyar amfani da manyan motoci na buldoza.

Har ila yau ‘yan sandan HKI sun kutsa cikin garuruwa da dama na Falasdinawa a yammacin kogin Jordan, inda su ka kama mutane da dama. Haka nan kuma sanadiyyar  harbe-harebn da su  ka yi, sun jikkata Falasdinawa 4 a sansanin Jalzuna dake arewacin birnin Ramallah.

A birnin Tubas kuwa ‘yan sahayoniyar sun kutsa cikin unguwanni mabanbanta tare da tilastawa mazauna wasu unguwanni da su fice daga cikin gidajensu. Kwamitin al’umma na Falasdinu a yankin ya sanar da cewa  a tsawon lokacin yaki adadin Falasdinawan da aka tilastawa ficewa daga cikin gidajensu, sun kai dubu 3 da 227.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: yan share wuri zauna

এছাড়াও পড়ুন:

Kasashen Musulmi 8 Sun Ki Amincewa Da Korar Falasdinawa Daga Gaza

Kasashen Larabawa da musulmi 8 ne suka gamu suka ki amincewa da shirin HKI na korar Falasdinawa da karfi daga Gaza.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran tanakalto ministocin harkokin kasashen waje na kasashen Saudia, Masar, Jordan, da UAE Pakisatan Turkey da kuma Qatar sun bada bayanin hadin giwa daga kasashen Saudiya kan cewa shirin HKI na bude Kofar Rafah ta fcewar Falasdinawa Kawai ba tare da shigowa ba, baa bin amincewa bane.

Bayanin ya kara da cewa, wannan shirin yana da hatsari, kuma shiri ne wanda zai hana kafuwar kasar Falasdinu idan har duk wanda ya fit aba zai sake shigowa ba.  

Jami’an diblomasiyyar sun bayyana cewa, shirin ya sabawadokokin kasa da kasa, kuma  barazana ce ga samuwar kasar Falasdinu nan gaba. Dama HKI ta dade tana neman damar korar Falasdinawa daga Gaza, har abada, don hana su kokarin kafa kasar Falasdinu a kasarsu da aka mamaye.

Kasashen 8 sun bukaci a kawo karshen hare-haren da sojojin HKI suke kaiwa kan yankuna Falasdinawa a Gaza, ta kyale kayakin agaji su shiga sannan su bada dama a sake gina yankin. Sun bukaci a sake maida gwamnatin Hamas a gaza saboda ta ci gaba a harkokin gudanarwa.

Daga karshe sun bayyana cewa a shirye suke yi aiki don aiwatar da kudurin kwamitin tsaro na MDD mai lamba 2803.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Sojojin Afganistan Da Pakistan Sun Yi Musayar Wuta A Tsakaninsu Duk Tare Da Tsagait Wuta December 6, 2025 Rasha Tace Ta Kakkabi Jiragen Drones Na Ukrai 116 A Daren Jiya December 6, 2025 ‘Yar Iran ta isa wasan karshe na gasar cin kofin duniya na wasan harbi a karo na 4 December 6, 2025 Iran da Rasha sun rattaba hannu kan yarjejeniyoyi 20 da kwangiloli 5 a fannin fasaha December 6, 2025 Putin Na Rasha Ya Ce; Kasarsa Da India Za Su Kara Girman Kasuwancinsu December 6, 2025 Sheikh Kassim Ya Yi Suka Akan Shigar Lebanon Cikin Kwamitin Tattaunawa Da “Isra’ila” Kai Tsaye December 6, 2025 Gwamnatin Iraki Ta Kore Saninta Da Shigar Da Sunayen Hizbullah Da “Ansarullah” A Cikin Na ‘Yan Ta’adda December 6, 2025 Limamin Tehran:  Idan Abokan Gaba Su Ka  Sake Yin Kuskure Akan Iran Za Su Sake Cin Kasa December 6, 2025 Iran Da Pakisatan Sun Amince Da Farfado da Layin Dogo Tsakanin Istambul, Tehran Zuwa Islamabad December 5, 2025 Iran Ta Raya Ranar Haramta Takunkuman Bangare Guda A Duniya December 5, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Pakistan ta Bai Wa Taliban Ta Aghanistan  Zabi A Tsakanin Mu’amala Da Ita Ko  Da  ‘Yan Ta’adda
  • An gano gawar malamin Islamiyya da ya ɓace a Neja
  • Dole ne Amurka ta amince da ‘yancin Iran na samar da makamashin nukiliya cikin lumana (Araghchi)
  • Tawagar Majalisar Amurka ta iso Nijeriya Don Bincika Zargin Tauye Haƙƙin Addini
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 168
  • Kissoshin rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 167
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 166
  • ’Yan sanda sun ceto yara 2 da aka yi garkuwa da su a Borno
  • Sabuwar Dokar CBN: Nawa Za a Iya Cirewa a ATM da POS?
  • Kasashen Musulmi 8 Sun Ki Amincewa Da Korar Falasdinawa Daga Gaza