HausaTv:
2025-06-15@01:03:06 GMT

Daruruwan ‘Yan Share Wuri Zauna Sun Kutsa Masallacin Kudus

Published: 15th, April 2025 GMT

A jiya Litinin daruruwan yahudawa ‘yan share wuri zauna sun kutsa cikin masallacin kudus, suna masu bayar da take na tsokana ga Musulmi. Har ila yau ‘yan share wuri zauna din sun kuma gudanar da na’u’oin ibadu na addinin yahudanci a cikin farfajiyar masallacin na Kudus.

Ma’aikatar  da take kula da wuraren ‘wakafi’ na musulunci, ta bayyana cewa; Adadin yahudawa ‘yan share wuri zauna din da su ka kutsa cikin masallacin na Kudus sun kai 765,kuma ‘yan sanda sun rika yi musu rakiya.

A lokaci daya kuma jami’an tsaron na ‘yan sahayoniya sun tsaurara matakan kuntatawa Falasdinawa masu shiga cikin masallacin na Kudus domin yin salla.

Wannan tsokanar ta ‘yan share wuri zauna a masallacin Kudus, tana faruwa ne a lokacin da a can yammacin kogin Jordan, yahudawan suke lalata gonakin Falasdinawa da kankare kasar gonakin ta hanyar amfani da manyan motoci na buldoza.

Har ila yau ‘yan sandan HKI sun kutsa cikin garuruwa da dama na Falasdinawa a yammacin kogin Jordan, inda su ka kama mutane da dama. Haka nan kuma sanadiyyar  harbe-harebn da su  ka yi, sun jikkata Falasdinawa 4 a sansanin Jalzuna dake arewacin birnin Ramallah.

A birnin Tubas kuwa ‘yan sahayoniyar sun kutsa cikin unguwanni mabanbanta tare da tilastawa mazauna wasu unguwanni da su fice daga cikin gidajensu. Kwamitin al’umma na Falasdinu a yankin ya sanar da cewa  a tsawon lokacin yaki adadin Falasdinawan da aka tilastawa ficewa daga cikin gidajensu, sun kai dubu 3 da 227.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: yan share wuri zauna

এছাড়াও পড়ুন:

An kashe mutum 41 cikin mako ɗaya a Filato 

Aƙalla mutum 41 aka kashe, yayin da wasu da dama suka jikkata sakamakon hare-haren da aka kai wa jama’a daban-daban a Jihar Filato cikin mako guda da ya gabata.

Yankunan da aka kai wa hari sun haɗa da Bassa, Riyom, Bokkos da Ƙaramar Hukumar Mangu.

Hajjin 2025: Jihohi 11 sun kashe N6.2bn wajen tallafa wa Alhazai Tattalin arzikin Nijeriya zai haɓaka cikin shekaru uku masu zuwa — Bankin Duniya

Hakazalika, an ruwaito cewa ɗaruruwan mutane sun rasa matsugunansu, an kuma ƙone gidaje da ba a san adadinsu ba.

Ɗaya daga cikin mafi munin hare-haren ya auku ne a ranar 8 ga watan Yuni, a ƙauyen Bauda da ke yankin Langai a Ƙaramar Hukumar Mangu.

’Yan bindiga sun shiga garin da sassafe, inda suka kashe mutum bakwai tare da ƙond gidaje 61, ciki har da cocin COCIN LCC.

A daren ranar, wasu ’yan bindiga sun sake kai hari garin Chinchim da ke yankin Mangu, inda suka kashe mutum takwas.

Shugaban Ƙaramar Hukumar Mangu, Emmanuel Bala, ya tabbatar da aukuwar hare-haren.

“Mutane na cikin gidajensu lokacin da aka kai musu hari. An fi amfani da wuƙa wajen kashe su. Mutane takwas aka kashe a Chinchim. Kafin nan, mutane bakwai aka kashe a Bwai, kuma mun yi musu jana’iza a ranar Talata.”

Washegari, 9 ga watan Yuni, an sake kai hari a Gyenbwas da ke Langai, inda aka kashe mutum uku, an kuma ƙone gidaje sama da 90 ciki har da ginin JNI.

Mazauna yankin sun bayyana cewa maharan sun sace abinci, shanu, katifu da sauran kayayyaki.

Sakataren Ƙungiyar Gan Allah Fulani Development Association of Nigeria (GAFDAN), Abubakar Garba, ya musanta zargin cewa Fulani ne suka kai hare-haren.

“Ba ma goyon bayan tashin hankali. Mambobinmu masu bin doka ne. Muna kira ga hukumomin tsaro da su gudanar da bincike don gano masu laifi,” in ji shi.

Wannan rikici ya daɗe yana faruwa tsakanin manoma da makiyaya a yankin, inda suke yawan kai wa juna hare-hare, lamarin da ke ƙara haifar da rashin yarda a tsakaninsu.

Wasu na ɗora laifi kan wasu ƙabilu, wanda hakan ke ƙara dagula lamarin.

A ranar 7 ga watan Yuni, an kashe mutum huɗu a ƙauyen Uwok-Ishe da ke Kekkek a Bassa.

Har ila yau, an sake kai hari Riyom, inda aka kashe wani yaro guda ɗaya, wani kuma ya jikkata.

Rahotanni sun ce an kashe wasu makiyaya biyu a Ancher, yayin da a Kwall aka kashe mutum uku, bayab kai wani hari cikin dare.

Duk da waɗannan hare-haren da suka faru a cikin ƙanƙanin lokaci, Gwamnatin Jihar Filato ba ta fitar da wata sanarwa ba.

Har ila yau, babu wani martani daga kakakin rundunar ’yan sandan jihar ko rundunar Operation Safe Haven (OPSH), duk da ƙoƙarin da manema labarai suka yi na jin ta bakinsu.

Masana tsaro sun bayar da shawara kan yadda za a magance matsalar.

Tsohon jami’in ’yan sanda, SP Bulus Ajiji, ya ce: “Rashin haɗin kan al’umma da kuma rashin bayar da bayanai ga jami’an tsaro na daga cikin matsalolin. Wasu jama’a na kare miyagu kai-tsaye ko ba tare da sani ba.”

Masanin zaman lafiya kuma malami a jami’a, Joel Baba Alfa, ya bayar da shawarar matakan da za a ɗauka.

“Ya kamata gwamnati ta kai farmaki wajen da maharan ke ɓuya maimakon jiran suka kawo hari. Kuma a ƙirƙiro rundunar zaman lafiya ta al’umma wacce za ta ƙunshi dukkanin ɓangarorin da ke rikici da juna.”

Ya kuma ƙara da cewa: “Dole a riƙa bayyana gaskiya. Idan shanu sun mutu ko gonaki sun lalace, sai a sanar da jama’a. Haka kuma, kafofin watsa labarai su guji ɗaukar ɓangaranci kan addini ko ƙabila domin kaucewa tayar da rikici.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su
  • Sudan Ta Zargi Janar Haftar Na Libiya Da Goyon Bayan ‘Yan Tawayen Kasarta Na Rapid Support Forces
  • Iran : harin da Isra’ila ta kai ‘ ayyana yaki’ ne_ Araghchi
  • Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran
  • Hamas : Ziyarar ministan Isra’ila Ben-Gvir a masallacin al-Aqsa kan iya tayar da yakin addini
  •  Iran Za Ta Kara Yawan Sanadarin Urani’um Da Take Tacewa A Wuri Na Sirri
  • MDD: Adadin ‘Yan Gudun Hijira A Duniya Ya Kai Miliyan 122
  • Basaraken Da Aka Sace A Kogi Ya Kuɓuta Bayan Shafe Kwanaki 27 A Hannun ‘Yan Bindiga 
  • An kashe mutum 41 cikin mako ɗaya a Filato