Aljeriya ta yi barazanar korar jami’an diflomasiyyar Faransa 12
Published: 14th, April 2025 GMT
Rikicin diflomasiyya tsakanin Paris da Algiers na dada kamari, inda Aljeriya ta bukaci wasu jami’an diflomasiyyar Faransa 12 da su fice daga kasar cikin sa’o’i 48.
Ministan harkokin wajen Faransa Jean-Noël Barrot ya sanar cewa, Aljeriya ta bukaci jami’an diflomasiyyar Faransa da su fice daga kasar bayan kama wasu ‘yan kasar Aljeriya uku a Faransa.
“Ina kira ga hukumomin Aljeriya da su yi watsi da wannan matakin, inda ya kara da cewa: “Idan har aka ci gaba da yanke shawarar korar wakilanmu, ba mu da wani zabi illa mu mayar da martani cikin gaggawa.”
Shekaru da dama, alakar diflomatoyyar da ke tsakanin Aljeriya da Faransa ta yi tsami.
A farkon watan Afrilu, ministan harkokin wajen Faransa ya je kasar Aljeriya, domin kokarin warware matsalolin da suka jefa kasashen biyu cikin tabarbarewar diflomasiyya.
Bayan ganawa da shugaban kasar Aljeriya, Abdelmadjid Tebboune, Jean-Noël Barrot ya bayyana muradin kasashen biyu na “sake gina dangantakar abokantaka.”
A daidai lokacin da ake fuskantar tsamin dangantaka tsakanin Algiers da Paris, ofishin mai gabatar da kara na Faransa ya tuhumi, wasu ‘yan kasar Aljeriya uku, a ranar 11 ga Afrilu, ciki har da wani jami’in ofishin jakadanci, da zarginsu da hannu a sace wani dan adawar gwamnatin Algeria, Amir Boukhors, da aka sani da “AmirDZ na Paris” a cikin 2024.
Aljeriya ta yi kakkausar suka a ranar Asabar, 12 ga Afrilu, don nuna adawa da kamawa da tsare daya daga cikin jami’an ofishin jakadancinta a kasar Faransa tare da neman a gaggauta sakin shi.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Aljeriya Aljeriya ta
এছাড়াও পড়ুন:
An kashe ’yan bindiga 19 yayin daƙile wani hari a Kano
Dakarun Rundunar Sojin Najeriya sun daƙile wani harin ’yan bindiga a ƙaramar hukumar Shanono da ke Jihar Kano, inda suka yi nasarar hallaka 19 daga cikin ’yan ta’addan.
Bayanai sun ce sojojin ƙarƙashin rundunar haɗin gwiwa ta Operation MESA sun fafata da ‘yan bindigar ne da yammacin ranar Asabar bayan samun bayanan sirri kan motsinsu a yankunan Unguwar Tudu da Unguwar Tsamiya da Goron Dutse.
’Yan Sandan Legas sun ayyana neman Sowore ruwa a jallo Kano Pillars ta koma ƙarshen teburin Gasar Firimiyar NijeriyaA sanarwar da kakakin rundunar, Kyaftin Babatunde Zubairu, ya fitar, sojojin sun gaggauta kai samame yankin bayan samun rahoto, inda suka yi musayar wuta da ’yan bindigar.
“A yayin arangamar, an hallaka ’yan bindiga 19, kuma an ƙwato babura da dama da wayoyin salula guda biyu daga hannunsu,” in ji Kyaftin Zubairu.
Sai dai ya tabbatar da cewa sojoji biyu da ɗan sa-kai guda ɗaya sun rasu yayin fafatawar.
Kyaftin Zubairu ya ƙara da cewa ana ci gaba da gudanar da sintiri a yankin don kare al’ummomin da ke cikin haɗarin hare-haren masu satar shanu da sauran laifuka.
Rundunar ta kuma shawarci jama’a su kasance cikin shiri da lura, tare da kai rahoton duk wani motsi da ake zargin ba na halas ba ga jami’an tsaro mafi kusa.
A cewar kwamandan rundunar, Birgediya Janar Ahmed Tukur, Rundunar Sojin Najeriya na ƙoƙari wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a a Kano, tare da haɗin gwiwar sauran hukumomin tsaro.
An bayyana wannan aikin a matsayin wani ɓangare na ci gaba da kare yankunan karkara domin bai wa mazauna ƙwarin gwiwa a wuraren da ake fama da hare-haren ’yan bindiga.