HausaTv:
2025-12-04@04:51:23 GMT

Aljeriya ta yi barazanar korar jami’an diflomasiyyar Faransa 12

Published: 14th, April 2025 GMT

Rikicin diflomasiyya tsakanin Paris da Algiers na dada kamari, inda Aljeriya ta bukaci wasu jami’an diflomasiyyar Faransa 12 da su fice daga kasar cikin sa’o’i 48.

Ministan harkokin wajen Faransa Jean-Noël Barrot ya sanar cewa, Aljeriya ta bukaci jami’an diflomasiyyar Faransa da su fice daga kasar bayan kama wasu ‘yan kasar Aljeriya uku a Faransa.

“Ina kira ga hukumomin Aljeriya da su yi watsi da wannan matakin, inda ya kara da cewa: “Idan har aka ci gaba da yanke shawarar korar wakilanmu, ba mu da wani zabi illa mu mayar da martani cikin gaggawa.”

Shekaru da dama, alakar diflomatoyyar da ke tsakanin Aljeriya da Faransa ta yi tsami.

A farkon watan Afrilu, ministan harkokin wajen Faransa ya je kasar Aljeriya, domin kokarin warware matsalolin da suka jefa kasashen biyu cikin tabarbarewar diflomasiyya.

Bayan ganawa da shugaban kasar Aljeriya, Abdelmadjid Tebboune, Jean-Noël Barrot ya bayyana muradin kasashen biyu na “sake gina dangantakar abokantaka.”

A daidai lokacin da ake fuskantar tsamin dangantaka tsakanin Algiers da Paris, ofishin mai gabatar da kara na Faransa ya tuhumi, wasu ‘yan kasar Aljeriya uku, a ranar 11 ga Afrilu, ciki har da wani jami’in ofishin jakadanci, da zarginsu da hannu a sace wani dan adawar gwamnatin Algeria, Amir Boukhors, da aka sani da “AmirDZ na Paris” a cikin 2024.

Aljeriya ta yi kakkausar suka a ranar Asabar, 12 ga Afrilu, don nuna adawa da kamawa da tsare daya daga cikin jami’an ofishin jakadancinta a kasar Faransa tare da neman a gaggauta sakin shi.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Aljeriya Aljeriya ta

এছাড়াও পড়ুন:

Nijar ta maka kamfanin hakar uranium na Faransa Orano kotu

Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta bayyana aniyar maka hamshakin kamfanin nan na hakar uranium na faransa (Orano) a gaban kotu bayan gano sinadarai masu guba a yankin Madaoulela, dake arewacin kasar.

Dama dai Nijar da Orano sun sun shafe watanni suna takaddama kan sinadarin uranium da ake fitwarwa a kamfanin Somaïr, wanda aka mayar da shi mallakin kasar ta Nijar a watan Yuni.

Ministan Shari’a na Nijar, Alio Daouda, ne ya sanar da hakan a lokacin wani taron manema labarai da aka gudanar a ranar Talata nan.

Ministan ya ce an gano “ganguna 400 da ke dauke da samfuran sinadarai masu guba” a wani tsohon wurin hakar ma’adinan uranium a wani waje da Orano ya fice a yankin Arlit, wanda ke arewacin Nijar.

“Wannan kamfani ya cutar kuma yana ci gaba da cutar da lafiyar al’ummar Nijar ta hanyar amfani da sinadarai masu guba, da sanya rayuwar wasu cikin hadari, da kuma lalata muhalli.

Kamfanin ya ma ki bin umarnin kotu da kotunanmu suka bayar wanda ya tilasta masa na kwashe milyoyin tan na sharar tiriri mai guba na rediyoaktif da aka bari a sararin samaniya, in ji ministan na Nijar.

Ministan Shari’a na Nijar ya bayyana cewa Nijar ta dauki dukkan matakan da suka wajaba don gurfanar da Orano da kuma samun diyya kan duk barnar da aka yi wa Nijar.”

Orano, kamfani ne mallakar gwamnatin Faransa, wanda ya maye gurbin Areva, wacce ke rike da ikon mallakar hakar uranium na Nijar sama da rabin karni, saidai bayan juyin mulkin sojiji a ranar 26 ga Yuli, 2023, sabbin hukumomin Nijar sun yanke dukkan yarjejeniyoyi tsakanin Nijar da Faransa, ciki har da na hakkin hakar uranium na Orano.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Amurka ta soke bada mafaka ga ‘yan kasashen Afirka 10 December 3, 2025 Masar Ta Sanar Da Tattaunawa Da Amurka Don Shirya Sake Gina Gaza December 3, 2025 Isra’ila Ta Hana Motocin Agaji 6000 Shiga Gaza Duk Da Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta December 3, 2025 Kasar Qatar Ta Gargadi Isra’ila Game Da ci Gaba Da Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza December 3, 2025 Sharhi: HKI tana fama da karancin sojoji a dukkan rassan sojojin kasar December 2, 2025 Shugaba Pizishkiyan:  Goyon Bayan Al’ummar Iran Ga Tsarin Musulunci Ne Ya Hana Abokan Gaba Cimma Manufa December 2, 2025 Shugaban Kasar Najeriya Ya Nada Janar Chiristopher Musa ( Ritaya) A Matsayin Ministan Tsaro December 2, 2025 Nigeria Ta Bai Wa Dan Takarar Shugabancin Kasar Guine Bissau Mafakar Siyasa December 2, 2025  Palasdinu: Sojojin “Isra’ila” 3 Su Ka Jikkata Sanadiyyar  Taka Su Da Mota December 2, 2025 Hamas Ta Caccaki Isra’ila Game Da Hana Shigar Da Kayayyakin Agaji  A Yankin Gaza December 2, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rikicin Kungiyoyin Asiri Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Wani Matashi A Jihar Kwara
  • Nijar ta maka kamfanin hakar uranium na Faransa Orano kotu
  • Sharhi:’HKI tana fama da karancin sojojin a dukkan rassan sojojin kasar’.
  • An yi garkuwa da manoma 11 a Kudancin Kaduna
  • Wani Dan Adawa Da Gwamnatin Paul Biya Ya Mutu A Gidan Yari A Kasar Kamaru
  • An kama ’yan bindiga 4 a Kano
  • Tawagar ECOWAS Ta Bar Guinea – Bissau bayan da shugaban kasar yayi barazanar korarsu Da Karfi
  • MAAUN: Ƙungiyar iyaye ta musanta zargin ƙara ƙudin yaye ɗalibai a jami’ar
  • ’Yan bindiga sun sace fasto da matarsa  masu ibada a Kogi 
  • N750,000 kuɗin bikin yaye ɗaliban Jami’ar MAAUN ya tayar da ƙura a Kano