Aljeriya ta yi barazanar korar jami’an diflomasiyyar Faransa 12
Published: 14th, April 2025 GMT
Rikicin diflomasiyya tsakanin Paris da Algiers na dada kamari, inda Aljeriya ta bukaci wasu jami’an diflomasiyyar Faransa 12 da su fice daga kasar cikin sa’o’i 48.
Ministan harkokin wajen Faransa Jean-Noël Barrot ya sanar cewa, Aljeriya ta bukaci jami’an diflomasiyyar Faransa da su fice daga kasar bayan kama wasu ‘yan kasar Aljeriya uku a Faransa.
“Ina kira ga hukumomin Aljeriya da su yi watsi da wannan matakin, inda ya kara da cewa: “Idan har aka ci gaba da yanke shawarar korar wakilanmu, ba mu da wani zabi illa mu mayar da martani cikin gaggawa.”
Shekaru da dama, alakar diflomatoyyar da ke tsakanin Aljeriya da Faransa ta yi tsami.
A farkon watan Afrilu, ministan harkokin wajen Faransa ya je kasar Aljeriya, domin kokarin warware matsalolin da suka jefa kasashen biyu cikin tabarbarewar diflomasiyya.
Bayan ganawa da shugaban kasar Aljeriya, Abdelmadjid Tebboune, Jean-Noël Barrot ya bayyana muradin kasashen biyu na “sake gina dangantakar abokantaka.”
A daidai lokacin da ake fuskantar tsamin dangantaka tsakanin Algiers da Paris, ofishin mai gabatar da kara na Faransa ya tuhumi, wasu ‘yan kasar Aljeriya uku, a ranar 11 ga Afrilu, ciki har da wani jami’in ofishin jakadanci, da zarginsu da hannu a sace wani dan adawar gwamnatin Algeria, Amir Boukhors, da aka sani da “AmirDZ na Paris” a cikin 2024.
Aljeriya ta yi kakkausar suka a ranar Asabar, 12 ga Afrilu, don nuna adawa da kamawa da tsare daya daga cikin jami’an ofishin jakadancinta a kasar Faransa tare da neman a gaggauta sakin shi.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Aljeriya Aljeriya ta
এছাড়াও পড়ুন:
Ganawa A Tsakanin Mataimakan Ministocin Waje Na Kasashen Saudiyya, China Da Minista Arakci Na Iran
Kamfanin dillancin labarun “Mehr” na Iran ya nakalto ganawar da aka yi a tsakanin mataimakan ministocin harkokin waje na kasashen Saudiyya, Walid Khariji, da na China Miao Deo da kuma ministan harkokin wajen Iran Abbas Arakci.
A yayin wannan taron, ministan harkokin wajen Iran ya bayyana gamsuwarsa da yadda kasar China take daukar matakai na gina kyakkyawar alaka a cikin yannacin Asiya, sannan kuma ya bayyana matsayar Iran na bunkasa alakarta da kasashe makwabta.
Ministan harkokin wajen na Iran ya yi Ishara da yadda alaka a tsakanin Tehran da Riaydh take bunkasa a cikin fagage mabanbanta, haka nan kuma yadda suke tuntubar juna akan batutuwan da kasashen biyu suke bai wa muhimmanci.
Haka nan kuma ya yi Ishara da rawar da kasar china ta taka wajen karfafa zaman lafiya a tsakanin kasashen Iran da Saudiyya, da kuma taimakawa a wajen aiki da doka a duniya.
Minista Arakci ya kuma tabo batun alaka a tsakanin Iran da China yana mai kara da cewa, kasashen biyu sun daura aniya fadada wannan alakar.
A nasu gefen, jami’an diplomasiyyar na Saudiyya da China sun yaba wa Iran akan yadda ta karbi bakuncin taron kasashen uku wanda shi ne karo na uku. Haka nan kuma sun nuna azamarsu ta ganin an fadada wannan alakar.
Gabanin wannan ganawar, jami’an diplomasiyyar na China da Saudiyya sun gana da takwaransu na Iran Majid Takht-Ravanchi akan batun karfafa alakar kasashen uku.
Sanarwar ta sake jaddada kudirin Iran da Saudiyya na bin dukkan tanade-tanaden Yarjejeniyar Beijing ta 2023, wanda ya sauwaka wajen dawo da huldar diflomasiyya tsakanin kasashen biyu a shiga tsakani na China.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Antoni Gutress Ya Yi Allawadai Da Kutsen Da “Isra’ila” Ta Yi A Cibiyar Unrwa December 10, 2025 Iran da Saudiyya sun sake jaddada fadada dangantakarsu December 9, 2025 Faransa ta ce da hannunta aka dakile juyin mulki a Benin December 9, 2025 RSF : Rabin ‘Yan jarida 67 da aka kashe a bana, a Zirin Gaza ne December 9, 2025 An cire Tony Blair daga jerin wadanda zasu jagoranci Gaza December 9, 2025 Isra’ila ta sake kai hare-haren a kudancin Lebanon December 9, 2025 Trump Ya Yi Gefe Da Kasashen Turai Dangane Da Tattaunawa Kan Rikicin Ukraine December 9, 2025 Iran Ta Gudanar Da Taro Kan Yadda Manzon Allah (s) Ya Yi Mu’amala Da Wadanda Ba Musulmi Ba December 9, 2025 Najeriya : Matsala ce ta sa jirgin sojinmu yin saukar gaggawa A Burkina Faso December 9, 2025 Saudiya da Qatar Zasu Gina Layin Dogo Mai Sauri Tsakanin Kasashen Biyu December 9, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci