HausaTv:
2025-12-06@09:24:58 GMT

Aljeriya ta yi barazanar korar jami’an diflomasiyyar Faransa 12

Published: 14th, April 2025 GMT

Rikicin diflomasiyya tsakanin Paris da Algiers na dada kamari, inda Aljeriya ta bukaci wasu jami’an diflomasiyyar Faransa 12 da su fice daga kasar cikin sa’o’i 48.

Ministan harkokin wajen Faransa Jean-Noël Barrot ya sanar cewa, Aljeriya ta bukaci jami’an diflomasiyyar Faransa da su fice daga kasar bayan kama wasu ‘yan kasar Aljeriya uku a Faransa.

“Ina kira ga hukumomin Aljeriya da su yi watsi da wannan matakin, inda ya kara da cewa: “Idan har aka ci gaba da yanke shawarar korar wakilanmu, ba mu da wani zabi illa mu mayar da martani cikin gaggawa.”

Shekaru da dama, alakar diflomatoyyar da ke tsakanin Aljeriya da Faransa ta yi tsami.

A farkon watan Afrilu, ministan harkokin wajen Faransa ya je kasar Aljeriya, domin kokarin warware matsalolin da suka jefa kasashen biyu cikin tabarbarewar diflomasiyya.

Bayan ganawa da shugaban kasar Aljeriya, Abdelmadjid Tebboune, Jean-Noël Barrot ya bayyana muradin kasashen biyu na “sake gina dangantakar abokantaka.”

A daidai lokacin da ake fuskantar tsamin dangantaka tsakanin Algiers da Paris, ofishin mai gabatar da kara na Faransa ya tuhumi, wasu ‘yan kasar Aljeriya uku, a ranar 11 ga Afrilu, ciki har da wani jami’in ofishin jakadanci, da zarginsu da hannu a sace wani dan adawar gwamnatin Algeria, Amir Boukhors, da aka sani da “AmirDZ na Paris” a cikin 2024.

Aljeriya ta yi kakkausar suka a ranar Asabar, 12 ga Afrilu, don nuna adawa da kamawa da tsare daya daga cikin jami’an ofishin jakadancinta a kasar Faransa tare da neman a gaggauta sakin shi.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Aljeriya Aljeriya ta

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sanda sun kama tsohon shugaban PCACC, Muhuyi Rimin Gado a Kano

’Yan sanda sun kama tsohon Shugaban Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano (PCACC), Muhuyi Magaji Rimin Gado.

Rahotanni sun nuna cewar wasu ’yan sanda ɗauke makamai ne suka kama shi a ofishinsa da ke Kano, bayan tafka jayayya a ranar Juma’a.

Cikakken jadawalin rukunin Gasar Kofin Duniya ta 2026 Na kashe N100bn a kan harkar tsaro a 2025 — Zulum

Waɗanda lamarin ya faru a kan idonsu, sun  ce manyan motocin ’yan sanda cike da jami’an da ke ɗauke da makamai ne suka dira ofishinsa da ke kan titin zuwa Zariya.

Sun gargaɗi mutane da kada kowa ya kusanci ofishin, inda suka yi barazanar buɗe wa duk wanda ya yi yunƙurin tsoma baki a lamarin wuta.

Muhuyi, ya nemi jami’an su nuna masa takardar kama shi ko su bayyana dalilin kama shi.

Sai dai jami’an sun ƙi bayyana komai, face cewar umarni aka ba su daga Hedikwatar ’Yan Sanda ta Ƙasa da ke Abuja.

Lauya Ridwan Zakariyya, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce bayan tafka jayayya, daga bisani an kai Muhuyi hedikwatar ’yan sanda ta Kano da ke Bompai.

Ya ce jami’an sun ce su wani rukuni ne na musamman na Sufeto Janar na ’Yan Sanda da aka aiko daga Abuja.

Zakariyya, ya ƙara da cewa jami’an sun yi yunƙurin ƙwace wayar Muhuyi tare da yin barazanar harbi.

Wannan shi ne karo na biyu da ake kama Muhuyi a shekarar 2025.

A farkon watan Janairu, rundunar IGP Monitoring Unit ta kama shi kan almundahanar wasu kuɗaɗe da ake zargin suna da alaƙa da wani jigo na jam’iyyar APC, amma daga baya aka sake shi.

Ƙoƙarin jin ta bakin kakakin rundunar ’yan sandan Kano, CSP Abdullahi Kiyawa, ya ci tura, domin bai amsa wayarsa ba, zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Na’im Kassim Ya Yi Suka Akan Shigar Kasar Cikin Kwamitin Tattaunawa Da “Isra’ila” Kai Tsaye
  • Gwamnatin Iraki Ta Kore Saninta Da Shigar Da Sunayen Hizbullah Da “Ansarullah” A Cikin Na ‘Yan Ta’adda
  • ’Yan sanda sun kama tsohon shugaban PCACC, Muhuyi Rimin Gado a Kano
  • Jami’an tsaro sun kama masu garkuwa da mutane 7 a Gombe
  • Iran Da Pakisatan Sun Amince ِDa Dawoda Layin Dogo Tsakanin Istambul, Tehran Zuwa Islamabad
  • Najeriya: Tinubu Ya Nada Wasu Karin Jakadu 65, Sanatoci Da Tsoffin Gwamnoni Na Daga Cikinsu
  • Fadlallah Na Hizbullah Ya Yi Kiran Hadin Kai A Tsakanin Musulmi Da Larabawa Domin Fuskantar Kalubale
  • Rikicin Kungiyoyin Asiri Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Wani Matashi A Jihar Kwara
  • Nijar ta maka kamfanin hakar uranium na Faransa Orano kotu
  • Wani ya yi shigar mahaifiyarsa da ta mutu ya je karvar kuxin fanshonta