HausaTv:
2025-12-03@16:22:53 GMT

Aljeriya ta yi barazanar korar jami’an diflomasiyyar Faransa 12

Published: 14th, April 2025 GMT

Rikicin diflomasiyya tsakanin Paris da Algiers na dada kamari, inda Aljeriya ta bukaci wasu jami’an diflomasiyyar Faransa 12 da su fice daga kasar cikin sa’o’i 48.

Ministan harkokin wajen Faransa Jean-Noël Barrot ya sanar cewa, Aljeriya ta bukaci jami’an diflomasiyyar Faransa da su fice daga kasar bayan kama wasu ‘yan kasar Aljeriya uku a Faransa.

“Ina kira ga hukumomin Aljeriya da su yi watsi da wannan matakin, inda ya kara da cewa: “Idan har aka ci gaba da yanke shawarar korar wakilanmu, ba mu da wani zabi illa mu mayar da martani cikin gaggawa.”

Shekaru da dama, alakar diflomatoyyar da ke tsakanin Aljeriya da Faransa ta yi tsami.

A farkon watan Afrilu, ministan harkokin wajen Faransa ya je kasar Aljeriya, domin kokarin warware matsalolin da suka jefa kasashen biyu cikin tabarbarewar diflomasiyya.

Bayan ganawa da shugaban kasar Aljeriya, Abdelmadjid Tebboune, Jean-Noël Barrot ya bayyana muradin kasashen biyu na “sake gina dangantakar abokantaka.”

A daidai lokacin da ake fuskantar tsamin dangantaka tsakanin Algiers da Paris, ofishin mai gabatar da kara na Faransa ya tuhumi, wasu ‘yan kasar Aljeriya uku, a ranar 11 ga Afrilu, ciki har da wani jami’in ofishin jakadanci, da zarginsu da hannu a sace wani dan adawar gwamnatin Algeria, Amir Boukhors, da aka sani da “AmirDZ na Paris” a cikin 2024.

Aljeriya ta yi kakkausar suka a ranar Asabar, 12 ga Afrilu, don nuna adawa da kamawa da tsare daya daga cikin jami’an ofishin jakadancinta a kasar Faransa tare da neman a gaggauta sakin shi.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Aljeriya Aljeriya ta

এছাড়াও পড়ুন:

Wani ya yi shigar mahaifiyarsa da ta mutu ya je karvar kuxin fanshonta

Wani ya yi shigar mahaifiyarsa da ta mutu ya je karvar kuxin fanshonta

Ana binciken wani tsohon ma’aikacin jinya a qasar Italiya bisa zargin ya yi shigar mahaifiyarsa da ta mutu kuma ya je ma’aikatar fansho a matsayin mahaifiyarsa don neman fanshonta. Haka kuma an gano ya voye gawarta a cikin gidansa har tsawon shekaru uku bayan mutuwarta.

Mutumin xan Italiya ya saka tufafin mahaifiyarsa da ta mutu sannan ya yi kwalliya da gazar da jan-baki kamar yada take yi, ya je bankin da take ajiya yana neman a biya shi kuxi fanshonta, bayan ya voye gawarta a gida.

Mutumin mai shekaru 56, ma’aikacin jinya da ya rasa aikinsa a garin Mantua, ya sami damar karvar dubban kuxi na Yuro kafin asirinsa ya tonu, kamar yadda Jaridar Corriere della Sera ta Italiya ta ruwaito.

An kuma yi zargin cewa, ya naxe gawar mahaifiyarsa, Graziella Dall’Oglio, sannan ya voye ta a cikin firji a gidansu har tsawon shekara uku ba tare da ya sanar da ma’aikatar fansho ba, inda ya riqa zuwa yana cire kuxin fanshon da ake tura mata yana bidirin gabansa.

Mis Dall’Oglio ta rasu kimanin shekara uku da suka gabata, tana da shekara 82. Amma xanta bai bayar da rahoton mutuwarta a hukumance ba, maimakon haka ya naxe gawarta a cikin zane, ya saka ta a cikin wata jakar ajiye kaya sannan ya voye ta a gidan.

Rahotanni sun ce, ya yi shigar mahaifiyarsa, sanye da jan-baki da hoda da gazar da kuma sarqa, sannan ya tafi sabunta katin shaidarta da ya qare a ofishin gwamnati da ke wajen Borgo Virgilio.

Bayanai sun nuna cewa, ya yi wa kansa aski sannan ya sanya gashin mata a kansa kamar irin na mahaifiyarsa da ta rasu, kuma ya sanya kayan ado kamar yadda ta saba.

Jaridar ta bayyana cewa, wannan wani sabon salon damfara ce kamar irin na fim xin ‘Mrs Doubtfire’, wanda aka yi a shekarar 1993 da Robin WilliaMis da ya fito a ciki. Mutumin ya bayyana a ofishin gwamnati da ke wajen Mantua a farkon wannan watan, inda aka yi zargin ya bayyana kansa a matsayin Mis Dall’Oglio.

Wani ma’aikacin ma’aikatar fansho ne ya harvo jirginsa, inda ya lura da cewa, akwai alamar tambaya game da ‘matar’ da take neman a canza mata katin. Musamman da yake ya san wacce take da ainihin katin ba ta da kaurin wuya, sannan kuma muryarta ba ta maza ba ce. Wannan ce ta sanya ma’aikacin bai wata-wata ba cikin sauri ya kai rahoto ga ‘yan sanda nan da nan kuma ya sanar da magajin garin Mantua.

’Yan sanda sun ce, da isarsu sai suka kwatanta hotunan Mis Dall’Oglio na gaske da na xanta da ya yi shigar burtu kuma sun fahimci cewa, akwai lauje a cikin naxi.

Bincike ya nuna xan ya karvi kuxin fanshonta na shekaru uku da suka kai kusan Fam 47,000 kuma da mallakar gidaje uku, a cewar rahotanni.

Bayan an kama shi, ‘yan sanda sun je gidansa, inda suka gano gawar Mis Dall’Oglio da aka voye a xakin wanki.

“Ya shigo ofishin ma’aikatar fansho yana sanye da dogon siket, ya yi ado da jan baki da jan-farce da sarqa da ‘yan kunne irin na tsofaffi,” Francesco Aporti, magajin garin Borgo Virgilio ya shaida wa Jaridar Corriere della Sera.

“Amma sai dai yana da kaurin wuya, sannan kuma fatar hannunsa ba ta yi kama da na tsohuwa ‘yar shekara 85 ba.

“Muryarsa kuma ta maza ce duk da yake ya yi shigar mata. Amma da a ce ba a lura da waxannan abubuwa ba da ya ci lalai.”

Da yake magana game da mahaifiyar wanda ake zargin, magajin garin ya ce, “Wataqila ta mutu ne saboda dalilai na rashin lafiya, amma za a tabbatar da hakan ne kawai ta hanyar binciken gawar.” Wannan labari ne mai ban mamaki kuma abin baqin ciki ne qwarai.”

‘Yan sandan Italiya sun ce, gawar mahaifiyar an naxe ta da zanin gado sannan aka saka ta a wata jakar kaya, aka sanya ta cikin firji.

Daga baya ’yan sanda sun xauki gawar zuwa wajen ajiye gawarwaki a asibitin da ke yankin don yin gwajin qwaqwaf da nufin gano musabbabin rasuwarta. Yanzu haka ana binciken mutumin a kan laifukan zamba da voye gawar da ya yi ba bisa qa’ida ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rikicin Kungiyoyin Asiri Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Wani Matashi A Jihar Kwara
  • Wani ya yi shigar mahaifiyarsa da ta mutu ya je karvar kuxin fanshonta
  • Sharhi:’HKI tana fama da karancin sojojin a dukkan rassan sojojin kasar’.
  • An yi garkuwa da manoma 11 a Kudancin Kaduna
  • Wani Dan Adawa Da Gwamnatin Paul Biya Ya Mutu A Gidan Yari A Kasar Kamaru
  • An kama ’yan bindiga 4 a Kano
  • Tawagar ECOWAS Ta Bar Guinea – Bissau bayan da shugaban kasar yayi barazanar korarsu Da Karfi
  • MAAUN: Ƙungiyar iyaye ta musanta zargin ƙara ƙudin yaye ɗalibai a jami’ar
  • ’Yan bindiga sun sace fasto da matarsa  masu ibada a Kogi 
  • N750,000 kuɗin bikin yaye ɗaliban Jami’ar MAAUN ya tayar da ƙura a Kano