A Kasar Gabon Brice Oligui Nguema Ya Lashe Zaben Shugaban Kasa
Published: 14th, April 2025 GMT
Shugaban gwamnatin rikon kwarya na kasar Gabon wanda ya tsaya takarar shugabancin kasar, ya lashe zabe da kawo 90.35% kamar yadda sanarwar ma’aikatar cikin gida ta sanar.
Brice Nguema ne dai ya jagoranci juyin mulkin da ya kifar da gwamnatin Ali Bango a watan Ogusta na shekarar 2023, ya kuma shiga cikin ‘yan takarar shugabancin kasar a wannan zaben.
Dan takara na biyu da yake binsa a baya, shi ne Alain Claude Bilie Bie Nze da ya sami kaso 3.02% na jumillar kuri’un da aka kada.
An sami halartar kaso 70.4% na jumillar wadanda su ka cancanci kada kuri’a da ya zama mai muhimmanci da zai kawo karshen mulkin rikon kwarya na soja.
Zaben na wannan lokacin shi ne irinsa na farko tun 2023.
Yawan masu kada kuri’ar dai sun kai 920,000, sai kuma masu sa idanu daga kasashen waje da sun kai 28,000.
Adadin mutanen kasar Gabon ya kai miliyan 2.3 da mafi yawancinsu suke rayuwar talauci duk da cewa Allah ya huwace wa kasar arzikin man fetur.
Masu Sanya idanu akan zaben sun ce, a kalla san sami kula da dukkanin ka’idojin zabe a cikin kaso 94.8 na mazabun kasar, kuma an baje komai a faifai ba tare da kumbaya-kumbiya ba da kaso 98.6%. Gabanin yin juyin mulkin da ya kawo karshen mulkin iyalan Bango na shekaru 50, Oligui Nguema ya kasance shugaban rundunar da take tsaron fadar shugaban kasa na kusan shekaru biyu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kaso 90 na ’yan bindigar da suka addabi Katsina ’yan asalin jihar ne – Radda
Gwamnan jihar Katsina, Dikko Radda, ya ce kimanin kaso 90 cikin 100 na ’yan bindigar da suka hana jiharsa sakat ba baki ba ne, ’yan cikinta ne.
Ya bayyana haka ne lokacin da ya bayyana a cikin shirin Sunrise Daily na gidan talabijin na Channels a ranar Talata.
Ya ce tuni gwamnatinsa ta kafa rundunar tsaro mallakin jihar mai suna Katsina Community Watch Corps, inda aka debi matasa daga yankunan da ke fama da matsalolin tsaron domin a dakile ta tun daga tushe.
DAGA LARABA: Shin Ko Zafin Nema Na Kawo Samu? Malaman firamare sun janye yajin aiki a AbujaKatsina dai na daya daga cikin jihohin Arewa maso Yamma da ke fama da matsalar ’yan bindiga, inda mutane dauke da makamai kan kai farmaki kan kauyuka su kashe mutanen gari sannan su dauki wasu domin karbar kudin fansa. Sai dai a ’yan kwanakin nan jihar ta dan samu saukin hare-haren.
A cewar Gwamnan, akasarin maharan ba baki ba ne, a yankunan danginsu suke, inda ya ce amfani da mutanen yankin na taka muhimmiyar rawa wajen shawo kan matasalar tun daga tushe.
Ya ce a sakamakon haka, an sami nasarar kama mutane da dama da ke samar wa da ’yan bindigar kayayyaki da kuma bayanan sirri.
Radda ya ce, “Ba wai cewa muke an ga bayan matsalar tsaro gaba dayanta ba, saboda har yanzu a kan samu hare-hare jifa-jifa, amma dai yanzu an samu sauki.
“A baya akwai wadanda suke tunanin gaba daya jihar ma ta koma hannun ’yan ta’addan saboda kashe-kashen da ake yi a ko ina. Amma wannan tunanin ya saba da abin da yake a zahiri.
“Dalilinmu na kirkirar sabuwar rundunar tsaro ta jiha shi ne mu taimaka wa sauran jami’an tsaro a ayyukansu. Mun dauki mutane daga dukkan yankunan da ke da matsalolin tsaro saboda su suka fi sanin yankunansu da ma mutanen cikinsa fiye da kowa.
“Mazauna wadannan yankunan sun san iyayen ’yan bindigar nan da kakanninsu, saboda ba baki ba ne. wannan ne sirrin samun nasararmu, har muke iya zuwa mu farmake su a har a maboyarsu. Dole sai da dan gari a kan ci gari,” in ji Gwamnan na Katsina.