’Yan bindiga sun kashe mutane 40 a sabon hari a Filato
Published: 14th, April 2025 GMT
’Yan bindiga sun kashe mutane arba’in a wani hari suka kai a ƙauyen Zike, a yankin Kwall da ke Ƙaramar Hukumar Bassa a Jihar Filato.
Wani shugaban al’ummar Kwall, Wakili Tongwe, ya ce maharan sun shiga ƙauyen ne da sanyin safiyar ranar Litinin suna harbi kan mai uwa da wabi, lamarin da ya sa mazauna gujegujen neman tsira.
Ya shaida wa wa kafar talabijin ta Channels cewa wata tawagar ’yan banga, da shi kansa da wasu jami’an tsaro, suna sintiri a wani ƙauye ne lokacin da maharan suka kai harin.
Ko da yake jami’an tsaron sun yi artabu da maharan kuma sun yi nasarar fatattakar su, amma an riga an riga an kashe mutane talatin da shida nan take, wasu huɗu kuma suka mutu daga baya.
Boko Haram ta kashe mutum 300 ta kwace ƙananan hukumomi 3 a Borno — Ndume NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar BornoWasu mazauna garin kuma sun samu raunukan harbin bindiga kuma suna samun kulawa a asibiti.
Hukumomin tsaro a jihar ba su yi wani sharhi ba game da harin, wanda ya zo ƙasa da makonni biyu bayan an kashe mutane hamsin da biyu a wasu ƙauyukan Karamar Hukumar Bokkos ta Jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga hari mahara
এছাড়াও পড়ুন:
Masu Tsatsauran Ra’yi Suna Kokarin Kaiwa Masu Hijira Da Musulmi A Ingila
Masu tsatsauran ra’ayi a Burtaniya sun gudanar da jerin gwano masu yawa a kasar don nuna kiyayya ga wadanda suka kaura zuwa kasar musamman musulmi.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran a nan Tehran ta bayyana cewa wannan ya nuna yadda mutane a kasar Burtaniya suka fada cikin rarraba mai zurfi a tsakaninsu dangane da yawan musulmi a kasar da kuma wadanda suka kaura daga kasashen duniya zuwa kasar.
Labarin ya kara da cewa wannan fahinta ta kin baki da kuma musulmi ba zai rasa nasaba da abubuwan da shugaban kasar Amurka Donal Trump yake yi a kasar Amurka na korar baki da kuma nuna kiyayya ga musulmi ba. Wanda hakan yake narazana ga zaman lafiya tsakanin mabiya addinai daban –daban a kasar ba. Sannan wani abin lura shi ne ana iya ganin tutan HKI a hannun wadanda suke fitowa zanga-zangar kin jinin baki da kuma musulmi a kasar ta Burtania a cikin yan kwanakin nan. Wanda yake nuni da yadda Amurka da HKI suke da hannu a ayyukansu. Labarin ya bayyana cewa wani dan siyasa Tommy Robinson ne yake jagorantar wadan nan zanga-zangar ta nuna kiyayya ga baki da kuma musulmi a birnin Londan. Sannan hare-hare a kan musulmi ya karu da kashi 90% a kasar a kuma dukkan masallatai a birnin London. Yawan zage-zage da kuma hare-hare a kan masallatai da kuma kan musulmi ya karu sosai a kasar musamman bayan yakin Gaza.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Bukaci Mutanen Yemen Su Daina Kashe Juna December 14, 2025 Iran Tayi Tir Da Hare-Haren Sydney Na Kasar Austaralia December 14, 2025 Sudan: Makaman ‘Drones’ Sun Kashe Ma’aikatan MDD 6 A Kadugli Na Kurdufan Ta Kudu December 14, 2025 Eritrea Ta Fice Daga Kungiyar Raya Kasahsen Gabacin Afrika (IGAD) December 14, 2025 َA Yau Ne Za’a Gudanar Da Taron Koli Na Kungiyar ECOWAS A Birnin Abuja December 14, 2025 Iran Ta karbi Bakunci Taron Kasashen Dake Makwabtaka Da Afghanistan Da Rasha December 14, 2025 Isra’ilaTa Kashe Wani Bafalasdine Matashi A Wani Hari Da Takai A Arewacin Kogin Jodan. December 14, 2025 Shuwagabannin Majalisar Kasar Iran Da Na Ethiopia Sun Gudanar Da Taron Manema Labarai December 14, 2025 Ghana Ta Kori Wasu Yahudawa Guda 3 Don Mayar Da Martani December 14, 2025 Araghchi ya bukaci Amurka ta girmama al’ummar Iran da gwamnatinta December 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci