Aminiya:
2025-09-18@17:59:58 GMT

’Yan bindiga sun kashe mutane 40 a sabon hari a Filato

Published: 14th, April 2025 GMT

’Yan bindiga sun kashe mutane arba’in a wani hari suka kai a ƙauyen Zike, a yankin Kwall da ke Ƙaramar Hukumar Bassa a Jihar Filato.

Wani shugaban al’ummar Kwall, Wakili Tongwe, ya ce maharan sun shiga ƙauyen ne da sanyin safiyar ranar Litinin suna harbi kan mai uwa da wabi, lamarin da ya sa mazauna gujegujen neman tsira.

Ya shaida wa wa kafar talabijin ta Channels cewa wata tawagar ’yan banga, da shi kansa da wasu jami’an tsaro, suna sintiri a wani ƙauye ne lokacin da maharan suka kai harin.

Ko da yake jami’an tsaron sun yi artabu da maharan kuma sun yi nasarar fatattakar su, amma an riga an riga an kashe mutane talatin da shida nan take, wasu huɗu kuma suka mutu daga baya.

Boko Haram ta kashe mutum 300 ta kwace ƙananan hukumomi 3 a Borno — Ndume NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar Borno

Wasu mazauna garin kuma sun samu raunukan harbin bindiga kuma suna samun kulawa a asibiti.

Hukumomin tsaro a jihar ba su yi wani sharhi ba game da harin, wanda ya zo ƙasa da makonni biyu bayan an kashe mutane hamsin da biyu a wasu ƙauyukan Karamar Hukumar Bokkos ta Jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga hari mahara

এছাড়াও পড়ুন:

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

A lokacin gudanar da bincike, an samu layin waya guda 21 da takardun rijistar layi guda 29 a wajen Suleiman, wanda ya ce yana harkar rijistar layin ne.

Ya amsa cewa shi ne ya bai wa waɗanda “aka sace” waya da lambar da aka yi amfani da ita wajen neman kuɗin fansa.

Binciken ya nuna cewa waɗannan mutanen suna cikin wani tsari na zamba wanda ake kira da Ponzi.

An kuma gano cewa ɗaya daga cikinsu ya haɗa baki da wanda aka ce an yi garkuwa da shi don su karɓi kuɗi daga sauran abokan harkarsu.

SP Abiodun ya ce bincike ana ci gaba da bincike domin kama sauran waɗanda ke da hannu a lamarin, yayin da aka riga aka gurfanar da waɗanda aka kama a kotu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato
  • Yadda jariri ya rasu a bayan mahaifiyarsa yayin tsere wa harin ’yan bindiga a Neja
  • An kashe ’yan ta’addan IPOB da yawa a Imo — ’Yan Sanda
  • ’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara