’Yan bindiga sun kashe mutane 40 a sabon hari a Filato
Published: 14th, April 2025 GMT
’Yan bindiga sun kashe mutane arba’in a wani hari suka kai a ƙauyen Zike, a yankin Kwall da ke Ƙaramar Hukumar Bassa a Jihar Filato.
Wani shugaban al’ummar Kwall, Wakili Tongwe, ya ce maharan sun shiga ƙauyen ne da sanyin safiyar ranar Litinin suna harbi kan mai uwa da wabi, lamarin da ya sa mazauna gujegujen neman tsira.
Ya shaida wa wa kafar talabijin ta Channels cewa wata tawagar ’yan banga, da shi kansa da wasu jami’an tsaro, suna sintiri a wani ƙauye ne lokacin da maharan suka kai harin.
Ko da yake jami’an tsaron sun yi artabu da maharan kuma sun yi nasarar fatattakar su, amma an riga an riga an kashe mutane talatin da shida nan take, wasu huɗu kuma suka mutu daga baya.
Boko Haram ta kashe mutum 300 ta kwace ƙananan hukumomi 3 a Borno — Ndume NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar BornoWasu mazauna garin kuma sun samu raunukan harbin bindiga kuma suna samun kulawa a asibiti.
Hukumomin tsaro a jihar ba su yi wani sharhi ba game da harin, wanda ya zo ƙasa da makonni biyu bayan an kashe mutane hamsin da biyu a wasu ƙauyukan Karamar Hukumar Bokkos ta Jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga hari mahara
এছাড়াও পড়ুন:
Cin hanci da rashawa sun yi ƙatutu a Najeriya — ICPC
Hukumar ICPC ta ce da ana aiwatar da dokokin yaƙi da cin hanci da rashawa yadda ya kamata, da kusan kashi 80 na ’yan Najeriya na ɗaure a gidan yari.
Kwamishinan ICPC na Jihar Kaduna, Sakaba Ishaku ne, ya bayyana haka a wani taron horaswa kan yadda ake kula da amana a ƙananan hukumomi.
Kisan Zariya: Na bar Buhari da Allah — Sheikh El-Zakzaky Najeriya za ta buga wasan sada zumunta da Masar kafin fara gasar AFCON ta 2025Ya ce cin hanci ya yi tasiri sosai a rayuwar ’yan Najeriya, kuma yana haifar da talauci, rikice-rikice, da jinkirta ci gaban ƙasa.
Ya ƙara da cewa yawancin dukiyar da wasu ke taƙama da ita a Najeriya ma da alaƙa da aikata rashin gaskiya, kuma mutane da yawa ba sa son jin batun yaƙi da cin hanci saboda suna jin daɗin aikata shi.
Ishaku, ya soki shugabannin ƙananan hukumomi da ke barin kujerarsu ba tare da sun aiwatar da wani gagarumin aiki ba.
Ya kuma nemi a tsaurara hukunci ga masu satar dukiyar gwamnati, inda ya ce duk wanda ya saci dukiyar jama’a bai kamata a masa hukunci mai sauƙi ba.
Kwamishinan Harkokin Ƙananan Hukumomi na Kaduna, Sadiq Mamman Legas, ya goyi bayan bayanan ICPC.
Ya ce gwamnati ta gyara na’urorin wutar lantarki a wasu yankuna, amma mazauna wajen suka lalata, tare da suka sace wasu.
Ya ce ba za a samu ci gaba ba idan mutane suna lalata dukiyar gwamnati.
Dukkanin jami’an sun yi kira da a ƙara ƙarfafa doka, a kula da ayyukan gwamnati sosai, kuma a wayar da kan jama’a domin rage cin hanci da kare kayayyakin gwamnati.