Aminiya:
2025-11-22@07:23:06 GMT

’Yan bindiga sun kashe mutane 40 a sabon hari a Filato

Published: 14th, April 2025 GMT

’Yan bindiga sun kashe mutane arba’in a wani hari suka kai a ƙauyen Zike, a yankin Kwall da ke Ƙaramar Hukumar Bassa a Jihar Filato.

Wani shugaban al’ummar Kwall, Wakili Tongwe, ya ce maharan sun shiga ƙauyen ne da sanyin safiyar ranar Litinin suna harbi kan mai uwa da wabi, lamarin da ya sa mazauna gujegujen neman tsira.

Ya shaida wa wa kafar talabijin ta Channels cewa wata tawagar ’yan banga, da shi kansa da wasu jami’an tsaro, suna sintiri a wani ƙauye ne lokacin da maharan suka kai harin.

Ko da yake jami’an tsaron sun yi artabu da maharan kuma sun yi nasarar fatattakar su, amma an riga an riga an kashe mutane talatin da shida nan take, wasu huɗu kuma suka mutu daga baya.

Boko Haram ta kashe mutum 300 ta kwace ƙananan hukumomi 3 a Borno — Ndume NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar Borno

Wasu mazauna garin kuma sun samu raunukan harbin bindiga kuma suna samun kulawa a asibiti.

Hukumomin tsaro a jihar ba su yi wani sharhi ba game da harin, wanda ya zo ƙasa da makonni biyu bayan an kashe mutane hamsin da biyu a wasu ƙauyukan Karamar Hukumar Bokkos ta Jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga hari mahara

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya ta ɗora alhakin taɓarɓarewar harkokin tsaronta kan Amurka

Gwamnatin Tarayya ta ɗora alhakin dawowar hare-haren ta’addanci, ciki har da sace dalibai mata a jihar Kebbi da kai hari a coci a jihar Kwara, kan kalaman da Amurka ta yi kwanan nan a kan Najeriya.

Sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume, ya ce sakonnin da Shugaban Amurka Donald Trump ya wallafa, inda ya zargi Najeriya da “kisan kiyasin Kiristoci” tare da barazanar tura sojojin kasarsa, sun kara wa wasu ƙungiyoyin ’yan ta’adda kaimin kai hare-hare.

Babu addinin da ake yi wa kisan ƙare dangi a Binuwai — Gwamna Alia Yadda maganin sauro ya yi ajalin magidanci da iyalinsa a Kano

“Kalaman da Amurka ta yi kwanan nan sun kara wa wasu ƙungiyoyin masu tayar da kayar baya da ke son amfani da labaran ƙasashen waje kai hare-hare kan wuraren da ba su da kariya kaimi,” in ji Akume a ranar Laraba.

Yayin da yake magana kan yadda ta’addanci, hare-haren ’yan bindiga da matsalolin tsaro ke ci gaba da sauyawa a ƙasar, Sakataren Gwamnatin ya ƙara da cewa: “Kafin waɗannan kalaman, an riga an raunana ƙungiyoyin ta’addanci sosai, kuma sun rage kai kananan hare-haren daji. Wannan dawowa ya nuna muhimmancin haɗin gwiwa, ba wai Magana kawai ba, tsakanin Najeriya da Amurka.”

Trump, a jerin sakonnin da ya wallafa a shafin X tsakanin 30 ga watan Oktoba da 1 ga Nuwamba, 2025, ya ayyana Najeriya a matsayin “Ƙasa mai Matsala ta Musamman” saboda zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi.

Shugaban Amurka ya yi gargadin cewa zai iya tura sojojin Amurka zuwa Najeriya idan kisan da ake zargin bai tsaya ba.

Ya ce tuni ya umarci Ma’aikatar Yaƙi ta kasar da ta fara shirin yiwuwar daukar matakin soja idan tashin hankali ya ci gaba.

Trump ya kuma yi barazanar dakatar da dukkan taimakon Amurka ga Najeriya idan gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta kasa magance abin da ya kira zaluntar Kiristoci.

A cikin jawabin da SGF ya yi a ranar Laraba, ya ce an riga an raunana cibiyoyin ta’addanci sosai kuma sun rage zuwa kananan hare-haren daji kafin waɗannan kalaman.

“Wasu ƙungiyoyi yanzu suna ƙoƙarin amfani da waɗannan kalaman don samun suna,” in ji shi.

Idan za a iya tunawa a cikin makon nan ne dai wasu ’yan bindiga suka sace dalibai 25 a makarantar sakandaren kwana ta GCGSS Maga da ke jihar Kebbi.

Kazalika, a cikin makon kuma ta wasu maharani sun farmaki wasu masu ibada a wani coci da ke Eruku a jihar Kwara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun bar makarantar Maga kafin ’yan bindiga su kai hari — Gwamna Kebbi 
  • ’Yan bindigar da suka sace masu ibada a cocin Kwara sun nemi a ba su N3bn kafin sakin su
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Dalibai da Malamai a Jihar Neja
  • ’Yan Bindiga Sun Nemi Miliyan 100 Kudin Fansa Kan Kowane Mutum Ɗaya da Suka Sace a Kwara
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Dalibai Mata 25 a Jihar Kebbi 
  • Gwamnatin Kwara ta rufe makarantu a kananan hukumomi 4 saboda matsalar tsaro
  • Wayar wutar lantarki ta kashe mutum 4 a wajen cashiya a Legas
  • Najeriya ta ɗora alhakin taɓarɓarewar harkokin tsaronta kan Amurka
  • Isra’ila ta kashe akalla Falasdinawa 27 a wani sabon harin bam
  • Tankin ruwa ya kashe mutum 4, wasu sun jikkata a Jigawa