’Yan bindiga sun kashe mutane 40 a sabon hari a Filato
Published: 14th, April 2025 GMT
’Yan bindiga sun kashe mutane arba’in a wani hari suka kai a ƙauyen Zike, a yankin Kwall da ke Ƙaramar Hukumar Bassa a Jihar Filato.
Wani shugaban al’ummar Kwall, Wakili Tongwe, ya ce maharan sun shiga ƙauyen ne da sanyin safiyar ranar Litinin suna harbi kan mai uwa da wabi, lamarin da ya sa mazauna gujegujen neman tsira.
Ya shaida wa wa kafar talabijin ta Channels cewa wata tawagar ’yan banga, da shi kansa da wasu jami’an tsaro, suna sintiri a wani ƙauye ne lokacin da maharan suka kai harin.
Ko da yake jami’an tsaron sun yi artabu da maharan kuma sun yi nasarar fatattakar su, amma an riga an riga an kashe mutane talatin da shida nan take, wasu huɗu kuma suka mutu daga baya.
Boko Haram ta kashe mutum 300 ta kwace ƙananan hukumomi 3 a Borno — Ndume NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar BornoWasu mazauna garin kuma sun samu raunukan harbin bindiga kuma suna samun kulawa a asibiti.
Hukumomin tsaro a jihar ba su yi wani sharhi ba game da harin, wanda ya zo ƙasa da makonni biyu bayan an kashe mutane hamsin da biyu a wasu ƙauyukan Karamar Hukumar Bokkos ta Jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga hari mahara
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji sun kashe ’yan fashin daji masu yawan gaske a Zamfara
Rahotanni na cewa ’yan fashin daji masu yawan gaske ne aka tabbatar da kashewa a wani kwanton ɓauna da sojoji suka yi musu a ranar Laraba a jihohin Zamfara da Kebbi.
Sojojin ƙasa da na sama sun yi amfanin da bayanan sirri wajen buɗe wuta kan ayarin ’yan fashin da ke kan ɗaruruwan babura suna zirga-zirga a yankin Yarbuga da ke Karamar Hukumar Maru a Jihar Zamfara.
Kakakin Rundunar Sojojin Sama ta Najeriya, Ehimen Ejodame, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da maraicen Alhamis, inda ya ce wasu daga cikin ’yan ta’addan sun rika kokarin guduwa a kafa da kuma kan baburan, amma sojojin suka ci gaba da yi musu ruwan wuta ta ko ina.
Muna so a kafa doka ta bincikar yadda ’yan Nijeriya ke tara dukiya — EFCC Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 24 a Arewa maso Gabashin NijeriyaYa ce, “A wani mummunan hari da dakarun rundunar Fansan Yamma na rundunar sojojin sama ta Najeriya suka kai, sun hallaka ’yan ta’adda masu yawan gaske a ranar tara ga watan Yulin 2025, kan wani ayarinsu da ke tafiya a tsakanin jihohin Zamfara da Kebbi.
“An kai harin ne bisa wasu bayanan sirri da aka tattara da suka nuna ’yan ta’addan da ke kan Babura sama da 150, kowannensu na dauke da akalla mutum biyu da ke dauke da makamai a kusa da kauyen Yarbuga na karamar hukumar Maru a jihar Zamfara.
“Bayan samun gagarumar nasarar a harin ta sama, kashegari dakarun sojojin kasa sun sake kai wani harin, inda suka gano gawarwaki ’yan ta’addan masu tarin yawa da kuma konannun baburansu. Hare-haren sun y mummunan ta’adi ga gungun ’yan ta’addan da ke yankin,” in ji Kakakin sojojin saman.
Kazalika, wata majiya da ke yankin da aka kai harin ta shaida wa wakilinmu cewan ’yan ta’addan na kan hanyarsu ce ta zuwa kauyen Maga a karamar hukumar Zurun jihar Kebbi, lokacin da suka kwashi kashin nasu a hannu.
Ana dai zargin sun fito ne daga wani daji da ke karamar hukumar Anka, daya daga cikin kananan hukumomi hudu na Zamfara da yanzu haka sojojin rundunar Fansan Yamma ke ruwan wuta a kan ’yan ta’addan na tsawon kwanaki.
“Da alama ’yan ta’addan na cikinn mawuyacin hali a yankin, saboda sojoji na ragargazarsu, kuma gas hi an yanke sabis din waya saboda sojoji su ji dadin aikinsu, sannan su kuma ’yan ta’addan bas u da hanyoyin yin waya da ’yan uwansu domin samun dauki,” in ji majiya tamu.