Aminiya:
2025-11-25@12:24:51 GMT

’Yan bindiga sun kashe mutane 40 a sabon hari a Filato

Published: 14th, April 2025 GMT

’Yan bindiga sun kashe mutane arba’in a wani hari suka kai a ƙauyen Zike, a yankin Kwall da ke Ƙaramar Hukumar Bassa a Jihar Filato.

Wani shugaban al’ummar Kwall, Wakili Tongwe, ya ce maharan sun shiga ƙauyen ne da sanyin safiyar ranar Litinin suna harbi kan mai uwa da wabi, lamarin da ya sa mazauna gujegujen neman tsira.

Ya shaida wa wa kafar talabijin ta Channels cewa wata tawagar ’yan banga, da shi kansa da wasu jami’an tsaro, suna sintiri a wani ƙauye ne lokacin da maharan suka kai harin.

Ko da yake jami’an tsaron sun yi artabu da maharan kuma sun yi nasarar fatattakar su, amma an riga an riga an kashe mutane talatin da shida nan take, wasu huɗu kuma suka mutu daga baya.

Boko Haram ta kashe mutum 300 ta kwace ƙananan hukumomi 3 a Borno — Ndume NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar Borno

Wasu mazauna garin kuma sun samu raunukan harbin bindiga kuma suna samun kulawa a asibiti.

Hukumomin tsaro a jihar ba su yi wani sharhi ba game da harin, wanda ya zo ƙasa da makonni biyu bayan an kashe mutane hamsin da biyu a wasu ƙauyukan Karamar Hukumar Bokkos ta Jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga hari mahara

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatan lantarki na shirin shiga yajin aiki a faɗin Najeriya 

Ƙungiyar Ƙwadago ta Ma’aikatan Wutar Lantarki ta Ƙasa (NUEE) ta yi barazanar dakatar da dukkan ayyukan samar da wutar lantarki a faɗin Najeriya, sakamakon harin da ta ce jami’anta sun fuskanta a Jihar Imo.

Ƙungiyar ta bayyana cewa wasu jami’an ’yan sanda ɗauke da makamai ne suka kai wa ma’aikatanta hari a Egbu 132/33kB Transmission Substation da ke Owerri, Jihar Imo, lamarin da ya janyo fargaba da tayar da hankali ga ma’aikatan da ke wurin.

Fiye da yara miliyan 400 na fama da talauci a duniya — UNICEF An gano wurin da ’yan bindiga ke tsare da ɗalibai 25 da aka sace a Kebbi

A wata sanarwa da sakataren ƙungiyar na ƙasa ya fitar, NUEE ta ce wannan hari na nuna take haƙƙin ma’aikaci, kuma ba za a lamunta da shi ba.

NUEE ta bayyana cewa ba za ta yi shiru ba yayin da tsaro da mutuncin mambobinta ke fuskantar barazana ba.

Sanarwar ta ce, “Wannan hari da jami’an tsaro suka kai ya saɓa wa duk ka’idojin aikin yi. Jami’anmu na gudanar da aikinsu ne na yau da kullum, amma aka afka musu da duka da barazana. Mun gaji da irin wannan cin zarafi.”

Ƙungiyar ta gargaɗi gwamnati da shugabannin rundunar ’yan sanda da cewa za ta rufe dukkan tashoshin wutar lantarki a sassan ƙasar, muddin ba a ɗauki matakin hukunta masu laifin da kuma bada tabbacin tsaron ma’aikata ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga sun yi yi garkuwa da mutane 11 a Kwara
  • Boko Haram ta file kan mata 2 a Borno
  • NAJERIYA A YAU: Halin Da Shirin Samar Da Tsaro A Makarantun Najeriya Ke Ciki
  • ’Yan bindiga sun kashe ɗan kasuwa, sun sace matarsa a Bauchi
  • ’Yan sanda sun ƙaryata jita-jitar kai wa coci hari a Gombe
  • ’Yan bindiga sun kashe ’yan sanda 5 a Bauchi
  • Najeriya : An sako mutum 38 da ‘yan bindiga suka sace a jihar Kwara_Tinubu
  • Ma’aikatan lantarki na shirin shiga yajin aiki a faɗin Najeriya 
  • An gano wurin da ’yan bindiga ke tsare da ɗalibai 25 da aka sace a Kebbi
  • ’Yan Sanda a Zamfara Sun Ceto Mutane 25 Bayan Dakile Harin ’Yan Bindiga a Damba