Aminiya:
2025-12-01@18:26:08 GMT

’Yan bindiga sun kashe mutane 40 a sabon hari a Filato

Published: 14th, April 2025 GMT

’Yan bindiga sun kashe mutane arba’in a wani hari suka kai a ƙauyen Zike, a yankin Kwall da ke Ƙaramar Hukumar Bassa a Jihar Filato.

Wani shugaban al’ummar Kwall, Wakili Tongwe, ya ce maharan sun shiga ƙauyen ne da sanyin safiyar ranar Litinin suna harbi kan mai uwa da wabi, lamarin da ya sa mazauna gujegujen neman tsira.

Ya shaida wa wa kafar talabijin ta Channels cewa wata tawagar ’yan banga, da shi kansa da wasu jami’an tsaro, suna sintiri a wani ƙauye ne lokacin da maharan suka kai harin.

Ko da yake jami’an tsaron sun yi artabu da maharan kuma sun yi nasarar fatattakar su, amma an riga an riga an kashe mutane talatin da shida nan take, wasu huɗu kuma suka mutu daga baya.

Boko Haram ta kashe mutum 300 ta kwace ƙananan hukumomi 3 a Borno — Ndume NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar Borno

Wasu mazauna garin kuma sun samu raunukan harbin bindiga kuma suna samun kulawa a asibiti.

Hukumomin tsaro a jihar ba su yi wani sharhi ba game da harin, wanda ya zo ƙasa da makonni biyu bayan an kashe mutane hamsin da biyu a wasu ƙauyukan Karamar Hukumar Bokkos ta Jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga hari mahara

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun sace amarya da ƙawenta 14 a Sakkwato

’Yan bindiga sun shiga garin Chaco da ke Ƙaramar Hukumar Wurno a Jihar Sakkwato, inda suka sace amarya da ƙawayenta guda 14.

Yayin da mutane ke tsaka shagalin bikin auren, sai ’yan bindigar suka afka musu tare da tarwatsa komai.

Mutum 6 sun jikkata a rikici manoma da makiyaya a Jigawa Sojoji sun ceto mutum 7 da ’yan bindiga suka sace a Kano

Sun shigo garin a ƙafa, inda suka wuce kai-tsaye zuwa gidansu amaryar ba tare da sun taɓa kowa ba.

Wani daga cikin iyayen ƙawayen amaryar ya shaida wa Aminiya cewa ba a tantance adadin waɗanda aka sace ba, amma wasu na cewa 15 ne, wasu kuma na cewa 13, amma amaryar da ’yarsa na cikin waɗanda aka sace.

Ya ce: “’Yata ’yar uwar amaryar ce. Ta zo ne kawai domin taya ’yar uwarta murnar bikinta a Chaco. Ban ɗauka za ta kwana a nan ba, ashe ƙaddara ke jiranta.”

A cewarsa, ’yan bindigar sun shiga garin ne da misalin ƙarfe 12 na daren ranar Asabar.

Sun shiga gidansu amaryar kai-tsaye inda suka yi awon gaba da ita da ƙawayenta.

Yayin da suke barin garin, matasa ’yan sa-kai sun yi ƙoƙarin dakatar da su, inda suka yi artabu, tare da yi wa ɗan ɗan sa-kai a hannu.

Ya ƙara da cewa har yanzu ’yan bindigar ba su tuntuɓi kowa ba domin neman kuɗin fansa.

Ranar Lahadi ita ce ranar da aka tsara domin ɗaura auren amaryar, sannan a kai ta gidan mijinta.

Lamarin tsaro a yankin gabashin Sakkwato na ƙara taɓarɓarewa.

Kakakin rundunar ’yan sandan Sakkwato, Ahmad Rufa’i, bai amsa kiran da aka masa ba, zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ’yan bindiga 4 a Kano
  • MAAUN: Ƙungiyar iyaye ta musanta zargin ƙara ƙudin yaye ɗalibai a jami’ar
  • ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Garin Eruka Na Jihar Kwara
  • Gwamnatin Kano Ta Kara Jaddada Dokar Haramcin Yin Haya da Babur a Jihar
  • ’Yan bindiga sun sace fasto da matarsa  masu ibada a Kogi 
  • ’Yan bindiga sun sace amarya da ƙawenta 14 a Sakkwato
  • ’Yan bindiga sun kashe tsohuwa, sun sace mutum 3 a Kano
  • Likitoci sun gindaya sabon sharaɗi bayan janye yajin aiki
  • Kuɗin Cizo ya tilasta rufe fitacciyar sinima a Faransa
  • Barau ya musanta zargin gwamnatin Kano, ya soki gwamna Abba