’Yan bindiga sun kashe mutane 40 a sabon hari a Filato
Published: 14th, April 2025 GMT
’Yan bindiga sun kashe mutane arba’in a wani hari suka kai a ƙauyen Zike, a yankin Kwall da ke Ƙaramar Hukumar Bassa a Jihar Filato.
Wani shugaban al’ummar Kwall, Wakili Tongwe, ya ce maharan sun shiga ƙauyen ne da sanyin safiyar ranar Litinin suna harbi kan mai uwa da wabi, lamarin da ya sa mazauna gujegujen neman tsira.
Ya shaida wa wa kafar talabijin ta Channels cewa wata tawagar ’yan banga, da shi kansa da wasu jami’an tsaro, suna sintiri a wani ƙauye ne lokacin da maharan suka kai harin.
Ko da yake jami’an tsaron sun yi artabu da maharan kuma sun yi nasarar fatattakar su, amma an riga an riga an kashe mutane talatin da shida nan take, wasu huɗu kuma suka mutu daga baya.
Boko Haram ta kashe mutum 300 ta kwace ƙananan hukumomi 3 a Borno — Ndume NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar BornoWasu mazauna garin kuma sun samu raunukan harbin bindiga kuma suna samun kulawa a asibiti.
Hukumomin tsaro a jihar ba su yi wani sharhi ba game da harin, wanda ya zo ƙasa da makonni biyu bayan an kashe mutane hamsin da biyu a wasu ƙauyukan Karamar Hukumar Bokkos ta Jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga hari mahara
এছাড়াও পড়ুন:
Kalibaf: Iran Da Habasha Suna Bunkasa Alakokin Siyasa Da Tattalin Arziki
Shugaban Majalisar Shawarar musulunci ta Iran Muhammad Bakir Kalibaf wanda ya gana da takwaransa na kasar Habasha Tagseh Chapo ya bayyana cewa: Kasashen biyu da suke da alakar diplomasiyya ta tsawon shekaru 70, sun Shata hanyoyin bunkasa alakokin tattalin arziki, siyasa da al’adu.
Haka nan kuma ya ce; kasantuwar kasashen biyu mambobi a cikin kungiyar Bricks yana kara dankon alakar da take tsakaninsu.
Shugaban Majalisar shawarar musuluncin ta Iran Muhammad Bakir Kalibaf, ya kuma ce; A shekarar da ta gabata na kai ziyarar aiki zuwa Addib Ababa,mun gana da Mr. Tagseh Chapo, inda na gayyace shi ya kawo Ziyara Iran, kuma an yi wannan ziyarar ce dai a lokacin da kasashen biyu suke mambobi na kungiyar Bricks.
Haka nan kuma shugaban Majalisar Shawarar musuluncin ta Iran ya ce; Habasha Babbar kasa ce a cikin nahiyar Afirka, musamman ta fuskar yawan jama’a, kuma ta yi tarayya da kasashen musulmi akan al’adu masu, musamman ma Iran.
Bugu da kari Kalibaf ya ce, alakar kasashen biyu ta fuskokin siyasa da tattalin arziki ta kai tsawon shekaru 70, kuma an Shata manufafofin da ake son cimmawa a wadannan fagagen.
A nashi gefen, shugaban majalisar dokokin kasar Habasha ya ce; Alakar kasashen biyu ta kai shekaru 70, kuma shekaru 60 da su ka gabata, sarkin kasarmu ya kawo Ziyara Iran,a wannan lokacin kuma tawaga mai girma daga Habashan ta sake zuwa Ziyara Iran.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 171 December 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 170 December 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 169 December 13, 2025 Isra’ila Ta Kai Hari A Kudancin Labanon A Ci Gaba Da Keta Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta December 13, 2025 Ziyarar Da Shugaban Rasha Ya Kai Indiya Ta Kara Karfafa Dangantakar Mosko Da Delhi December 13, 2025 Amurka Ta Sanya Sabbin Takunkumi A Bangaren Manfetur Na Venuzuela December 13, 2025 Hamas Ta Ce Ci Gaba Da Kai Hare-Haren Isra’ila Ya Nuna Gazawar Tsarin Duniya Na Dakatar Da Ita. December 13, 2025 Matatar Mai ta Dangote Ta Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 699 December 13, 2025 Iran da Rasha sun jaddada aiwatar da yarjejeniyar hadin gwiwa a tsakaninsu December 13, 2025 Ali Nuhu, ya yaba wa Iran kan haskaka Musulinci ta hanyar fina-finai December 13, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci