HausaTv:
2025-12-02@11:22:54 GMT

HKI Ta Jefa Boma-Bomai A Kan Asbiti Tilo Da Ya Rage Yake Aiki A Arewacin Gaza

Published: 13th, April 2025 GMT

Jiragen yakin HKI HKI sun yi ruwan boma-bomai kan astin Al-Ahli, asbiti tilo da ya rage yake aiki a arewacin zirin Gaza, a safiyar yau Lahadi.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa jiragen yakin HKI sun wargaza bangaren ’emagencu’ bukatar kula na gaggawa a asbitin da kuma kofar shiga asbitin.

Har’ila yau hare-haren sun lalata bangaren Iskar Oxigen na kula da wadanda suke bukatar kula mai tsanani a asbiti. Kuma sanadiyyar haka mutane da dama sun rasa rayukansu awannan bangaren daga ciki har da wani yaro dan shekara 12 wanda ya ji rauni a kai.

Razan Al-Nahhas wani likita mai aiki a bangaren  kula na gaggawa a asbitin ya fadawa kafafen yada labarai kan cewa wannan asbitin ne kawai dama yake aiki a arewacin Gaza, kuma a halin yanzu babu wani asbitin da ya rage a yankin.

Labarin ya kara da cewa bayan  wadannan hare-hare kan asbitin na Al-Ahli, mutane da dama basu san inda zasu je don samun jinya ba.

Likitan ta kara da cewa kafin hare-hare na safiyar yau Lahadi dai marasa lafiya wadanda aka yankewa kafafu da kuma wadanda suka ji rauni a kai da kuma kirjinsu ne suka fi yawa a cikinsa. Sannan a halin yanzu babu inda zasu je sai wasu kananan asbitoci wadanda basu da kayakin aiki na kula da su. Kuma tuni wasu sun mutu bayan harin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya gana da Janar Christopher CG Musa bayan Ministan Tsaro ya yi murabus

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi wata ganawar sirri da tsohon Babban Hafsan Tsaron Najeriya, Janar Christopher Gwabin Musa a Fadar Shugaban Kasa.

Ganawar Tinubu da Janar CG Musa ya auku ne a ranar Litinin da dare, jim kadan kafin sanarwar murabus din Ministan Tsaro, Alhaji Muhammad Badaru Abubakar.

Majiyoyi na cewa gananawar shugaban kasa da Janar CG Musa na da nasaba da shirin shugaban kasar na cike gurbin da Badaru ya bari da kuma garambawul a shugabancin tsaron Najeriya.

Mai magana da yawun shugaban kasa Bayo Onanuga ya sanar cewa Badaru ya yi murabus ne saboda dalilai na rashin lafiya.

An kama ’yan bindiga 4 a Kano MAAUN: Ƙungiyar iyaye ta musanta zargin ƙara ƙudin yaye ɗalibai a jami’ar

Badaru ya ajiye aiki ne a daidai lokacin da Najeriya ke fama da karuwar matsalar tsaro musammana a shiyyar Arewa lamarin da ya sa Shugaba Tinubu ya ayyan dokar ta-baci kan sha’anin tsaro.

A cikin ’yan watannin nan ’yan ta’adda a hare-harensu, suka kashe wani Janar din soja, Kwamandan Birget na 25 da ke Jihar Borno, Birgediya-Janar Uba Musa da dakarunsa a Jihar Borno, inda kuma suka yi garkuwa da wasu mata a gona.

A kwanan nan ’yan ta’adda sun tsananta kai hare-hare a Jihar Kano, baya ga sace daruruwan dalibai a jihohin Kebbi da Neja da kuma yin garkuwa da masu ibada a Jihohin Kwara da Kogi da kuma sace wasu mata a Borno.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Tsaron Najeriya  Ya Mika Takardar Ajiye Aiki Ga Shugaban Kasa Ahmad Tinubu.
  • Tinubu ya gana da Janar Christopher Musa bayan Ministan Tsaro ya yi murabus
  • Tinubu ya gana da Janar Christopher CG Musa bayan Ministan Tsaro ya yi murabus
  • Ministan Tsaro Badaru Abubakar Ya Ajiye Aiki
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 165
  • Paparoma Leo Na 14 Yana Ziyarar Aiki Na Kwanaki 3  A Kasar Lebanon
  • Gaza: Fiye da Falasdinawa 350 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila tun bayan tsagaita wuta
  • Nijar : zamu sayar da uranium dinmu ga wanda muka ga dama_ Janar Tiani
  • Shugaban venuzuwela Ya Gargadi Amurka Game Da Kokarin Da Take yi Na Karbe Ikon Kula Da Rijiyoyin Mai Na Kasar
  • Likitoci sun gindaya sabon sharaɗi bayan janye yajin aiki