Fashewar bam a mota ta kashe mutum takwas a Borno
Published: 12th, April 2025 GMT
Wani abin takaici ya sake afkuwa a kan hanyar Maiduguri zuwa Damboa a Jihar Borno mai cike da tashin hankali, yayin da wani bam ya tarwatse a safiyar Asabar da rana, inda aƙalla mutane takwas ne suka mutu.
Wasu shaidun gani da ido na nuni da cewa fashewar bam ɗin da ake kyautata zaton mayaƙan Boko ne suka dasa shi ya tarwatsa wata motar bas ƙirar Toyota “Hummer Bus” da ke ɗauke da fasinjoji zuwa Maiduguri babban birnin Jihar Borno.
Wata majiya mai tushe da aka zanta da ita, ta tabbatar da cewa aƙalla mutane bakwai da suka haɗa da direban motar ne ake fargabar sun mutu a wannan mummunan fashewar.
Titin Maiduguri zuwa Damboa ya kasance muhimmiyar hanyar mota da ta haɗa birnin Maiduguri zuwa ƙaramar hukumar Damboa da sauran al’ummomin kudancin Borno wadda a kullum ake fargabar bin ta lura da cewar tana gab da dajin Sambisa.
Don haka wannan lamari na baya-bayan nan ya zama babban abin tunatarwa game da barazanar tsaro da ke fuskantar matafiya da ke bin wannan hanya mai muhimmanci.
Har yanzu dai hukumomin tsaro ba su fitar da wata sanarwa a hukumance kan lamarin ba, har ya zuwa lokacin kammala wannan rahoto.
To sai dai kuma babu shakka wannan harin zai ƙara dagula al’amura game da lafiyar masu tafiye-tafiye da sufuri a yankin da kuma yankin da ake da ’yan tada ƙayar baya a yankin Arewa maso Gabas.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
An kashe jaririn wata 9 da wasu 3 a Filato
Aƙalla mutum huɗu ciki har da jaririn wata tara aka kashe a wani hari da aka kai ƙauyen Nkiendowro da ke Ƙaramar Hukumar Bassa a Jihar Filato.
Mutanen da suka rasu sun haɗa da mata biyu da namiji ɗaya, wanda aka ce suna aikin jigilar kwashe tumatir daga ƙauyen zuwa kasuwar Farin-Gada da ke Jos lokacin da aka kai musu hari.
Rashin wutar lantarki ya durƙusar da kasuwanci a Arewa Maso Gabas An kashe mutum 41 cikin mako ɗaya a FilatoWasu mutum biyu kuma sun jikkata a harin, wanda yanzu haka suna karɓar magani a wani asibiti da ba a bayyana sunansa ba.
Shugaban tsaron al’ummar Miango, Josiah Zongo, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa an ajiye gawarwakin, yayin da waɗanda suka jikkata ke karɓar kulawa.
Rundunar ’yan sandan Jihar Filato ba ta fitar da wata sanarwa ba kan harin.
A wani lamari makamancin haka, an kai hari ƙauyen Murish da ke Ƙaramar Hukumar Mangu a daren ranar Laraba, amma matasa da mazauna ƙauyen sun yi nasarar kare kansu daga maharan.
Wani matashi daga ƙauyen ya bayyana cewa maharan sun shigo suna harbi, amma mutanen ƙauyen sun kare kansu.
Shohotden Mathias Ibrahim, Daraktan Al’adu na ƙungiyar Mwaghavul Development Association kuma shugaban sansanin ‘yan gudun hijira a Mangu, ya roƙi al’umma da su kwantar da hankali su ci gaba da harkokinsu cikin lumana.
Ƙananan hukumomin Mangu da Bassa sun fuskanci hare-hare da dama a ‘yan kwanakin nan, lamarin da ke ƙara tayar da hankalin al’umma game da tsaro a Jihar Filato.