Aminiya:
2025-07-03@03:08:50 GMT

Fashewar bam a mota ta kashe mutum takwas a Borno

Published: 12th, April 2025 GMT

Wani abin takaici ya sake afkuwa a kan hanyar Maiduguri zuwa Damboa a Jihar Borno mai cike da tashin hankali, yayin da wani bam ya tarwatse a safiyar Asabar da rana, inda aƙalla mutane takwas ne suka mutu.

Wasu shaidun gani da ido na nuni da cewa fashewar bam ɗin da ake kyautata zaton mayaƙan Boko ne suka dasa shi ya tarwatsa wata motar bas ƙirar Toyota “Hummer Bus” da ke ɗauke da fasinjoji zuwa Maiduguri babban birnin Jihar Borno.

An kashe Uba da ’ya’yansa biyu a ƙauyen Filato An kama mutum 8 kan faɗan daba a Kano

Wata majiya mai tushe da aka zanta da ita, ta tabbatar da cewa aƙalla mutane bakwai da suka haɗa da direban motar ne ake fargabar sun mutu a wannan mummunan fashewar.

Titin Maiduguri zuwa Damboa ya kasance muhimmiyar hanyar mota da ta haɗa birnin Maiduguri zuwa ƙaramar hukumar Damboa da sauran al’ummomin kudancin Borno wadda a kullum ake fargabar bin ta lura da cewar tana gab da dajin Sambisa.

Don haka wannan lamari na baya-bayan nan ya zama babban abin tunatarwa game da barazanar tsaro da ke fuskantar matafiya da ke bin wannan hanya mai muhimmanci.

Har yanzu dai hukumomin tsaro ba su fitar da wata sanarwa a hukumance kan lamarin ba, har ya zuwa lokacin kammala wannan rahoto.

To sai dai kuma babu shakka wannan harin zai ƙara dagula al’amura game da lafiyar masu tafiye-tafiye da sufuri a yankin da kuma yankin da ake da ’yan tada ƙayar baya a yankin Arewa maso Gabas.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata zuwa Talata

Rahotanni na cewa an ɗage jana’izar fitaccen ɗan kasuwar nan, Alhaji Aminu Dantata da ya rasu ranar Asabar a ƙasar Hadaɗɗiyar Daular Larabawa.

Gwamnatin Nijeriya ce ta sanar da hakan ta bakin Ministan Labarai, Mohammed Idris yayin ganawa da da BBC.

APC ta sa ranar taron Majalisar Zartarwa bayan murabus ɗin Ganduje An kashe ubangidan Turji, Kacalla Ɗanbokolo a Zamfara

Ministan ya ce an ɗage jana’izar sakamakon rashin isar gawar marigayin a kan lokaci zuwa birnin Madina.

A cewarsa, “akwai ƙa’idoji da Gwamnatin Saudiyya ta shimfiɗa kan yadda za a shigar da gawa domin yi mata jana’iza a ƙasar.

“Saboda haka yanzu ana nan ana ta cike-ciken takardu tsakanin Gwamnatin Saudiyya da iyalan mamacin,” in ji Ministan.

Mohammed Idris ya ce idan an kammala za a ɗauko gawar daga Hadaɗɗiyar Daular Larabawa zuwa Saudiyya.

Ya ƙara da cewa tuni ofishin jakadancin Nijeriya a Saudiyya da iyalan mamacin suka kammala shirye-shiryen jana’izar.

Alhaji Aminu Ɗantata yana burin binne shi a birnin Madina, inda kuma ’yan uwansa suka nemi amincewar hukumomin Saudiyya game da buƙatar kuma ta sahale musu.

Tun da safiyar yau ne tawagogin Gwamnatin Tarayya da na Gwamnatin Kano suka tafi Saudiyyar domin halartar jana’izar da aka shiryi yi a yau Litinin.

Daga cikin tawagogin akwai Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf da Gwamnan Jigawa, Umar Namadi da kuma Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II.

Haka kuma, akwai tawagar Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin jagorancin Ministan Tsaro, Muhammad Badaru Abubakar da kuma malamai irinsu Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa da Dakta Bashir Aliyu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ambaliya: Zulum ya bada umarnin tallafa wa mutanen Damboa da Askira-Uba
  • Aragchi: Hare-Haren HKI Ya Kara Rashin Zaman Lafoya A Yankin Yammacin Asiya
  • ’Yan sanda sun kama matashin da ya kashe mahaifiyarsa a Jigawa
  • Sojoji sun kashe mayaƙan Boko Haram 10 a Borno
  • Dalibai 29 Suka Rasu A Turmutsitsin Tserewa Ga Fashewar Taransifoma A Jamhuriyar Afirka Ta Tsakiya
  • Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku
  • An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata zuwa Talata
  • Hare-haren Isra’ila sun kashe mana mutum 935 a yaƙin kwana 12 — Iran
  • HKI Ta Kashe Falasdinawa 72 A Cikin Gaza A Yua Litinin
  •  Wani Dan Bindiga Dadi Ya Kashe Ma’aikatan Kashe Gobara 2 A Amurka