Aminiya:
2025-10-17@10:03:26 GMT

Fashewar bam a mota ta kashe mutum takwas a Borno

Published: 12th, April 2025 GMT

Wani abin takaici ya sake afkuwa a kan hanyar Maiduguri zuwa Damboa a Jihar Borno mai cike da tashin hankali, yayin da wani bam ya tarwatse a safiyar Asabar da rana, inda aƙalla mutane takwas ne suka mutu.

Wasu shaidun gani da ido na nuni da cewa fashewar bam ɗin da ake kyautata zaton mayaƙan Boko ne suka dasa shi ya tarwatsa wata motar bas ƙirar Toyota “Hummer Bus” da ke ɗauke da fasinjoji zuwa Maiduguri babban birnin Jihar Borno.

An kashe Uba da ’ya’yansa biyu a ƙauyen Filato An kama mutum 8 kan faɗan daba a Kano

Wata majiya mai tushe da aka zanta da ita, ta tabbatar da cewa aƙalla mutane bakwai da suka haɗa da direban motar ne ake fargabar sun mutu a wannan mummunan fashewar.

Titin Maiduguri zuwa Damboa ya kasance muhimmiyar hanyar mota da ta haɗa birnin Maiduguri zuwa ƙaramar hukumar Damboa da sauran al’ummomin kudancin Borno wadda a kullum ake fargabar bin ta lura da cewar tana gab da dajin Sambisa.

Don haka wannan lamari na baya-bayan nan ya zama babban abin tunatarwa game da barazanar tsaro da ke fuskantar matafiya da ke bin wannan hanya mai muhimmanci.

Har yanzu dai hukumomin tsaro ba su fitar da wata sanarwa a hukumance kan lamarin ba, har ya zuwa lokacin kammala wannan rahoto.

To sai dai kuma babu shakka wannan harin zai ƙara dagula al’amura game da lafiyar masu tafiye-tafiye da sufuri a yankin da kuma yankin da ake da ’yan tada ƙayar baya a yankin Arewa maso Gabas.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 8 a harin kwanton ɓauna a Zamfara

Aƙalla jami’an tsaro takwas, ciki har da ɗan sanda guda ɗaya da masu tsaron al’umma bakwai, sun rasa rayukansu a wani harin kwanton bauna da aka kai musu a hanyar Gusau–Funtua da ke Jihar Zamfara a ranar Alhamis.

Lamarin ya faru ne a lokacin da gamayyar jami’an tsaro, waɗanda suka haɗa da ’yan sanda da mambobin rundunar tsaro ta jihar Zamfara ke amsa kiran gaggawa daga kauyen Tungawa da ke ƙaramar hukumar Tsafe.

An ceto mutane 3 da aka yi garkuwa da kama wasu a Bauchi Majalisar Dattawa ta amince da Amupitan Shugaban INEC

“Maganar da nake yanzu haka, an kwashe gawarwakin jami’an da suka mutu zuwa Gusau domin jana’iza,” in ji wani shaida da aka bayyana sunansa da Tsafe.

Shugaban ƙaramar hukumar Tsafe, Hon. Garba Fanchan, ya tabbatar da faruwar lamarin tare da miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan waɗanda suka rasa rayukansu.

Ya bayyana harin a matsayin “mugunta da rashin imani,” yana mai tabbatar wa jama’a cewa gwamnati na ɗaukar matakan gaggawa don dakile matsalar tsaro da ke ƙaruwa a yankin.

Gwamnan jihar, Dauda Lawal, shi ma ya aike da saƙon ta’aziyya ga iyalan mamatan.

A cikin wata sanarwa ranar Alhamis, gwamnan ya jajanta wa hukumomin tsaro tare da addu’ar Allah ya gafarta wa jami’an da suka rasa rayukansu.

“Waɗannan jaruman sun mutu ne a yayin da suke bakin aiki don kare al’ummarmu. Allah ya gafarta musu, ya sa sun huta,” in ji Gwamna Lawal.

Hanyar Gusau–Funtua na ƙara zama wurin da ake yawan kai hare-hare, inda rahotanni ke nuna cewa kusan kowace rana ’yan bindiga na kai farmaki ga matafiya a hanyar.

Hukumomi sun sha alwashin ƙara daukar matakai domin dawo da zaman lafiya a hanyar da kuma tabbatar da lafiyar matafiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 8 a harin kwanton ɓauna a Zamfara
  • FMC Birnin Kudu Ya Yi Bikin Ranar Maganin Kashe Radadi Ta Duniya
  • Jami’an FRSC Sun Mayar Da N6.2m Da Suka Tsinta Bayan Aukuwar Hatsarin Mota A Katsina
  • An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato
  • Ministan Yada Labarai Ya Bayyana Jihar Borno A Matsayin Mafi Juriya A Najeriya
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 1, sun sace dabbobi a Katsina
  • ‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako
  • An kama mata da miji suna safarar makamai a Kaduna
  • ’Yan bindiga sun kai hari a Kankia
  • An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa