HausaTv:
2025-12-12@13:10:37 GMT

Iran da Amurka zasu ci gaba da tattaunawa a mako mai zuwa

Published: 12th, April 2025 GMT

An kammala zagayen farko na tattaunawa tsakanin Iran da Amurka a babban birnin Muscat a shiga tsakanin kasar Oman.

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi da Steve Witkoff, manzon musamman na shugaban Amurka kan harkokin yankin gabas ta tsakiya ne suka jagoranci shawarwarin yau Asabar.

A cikin wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen Iran ta fitar ta ce bangarorin sun yi musayar ra’ayi game da shirin nukiliyar Iran na zaman lafiya, da kuma dage takunkumi.

Ya kara da cewa an gudanar da shawarwarin ne cikin yanayi mai ma’ana kuma bisa mutunta juna.

A karshen sama da sa’o’i biyu da rabi na tattaunawar, shugabannin tawagogin Iran da na Amurka sun yi jawabi na ‘yan mintoci kadan a yayin da suke barin wurin taron a gaban ministan harkokin wajen Omani,” in ji ma’aikatar.

Bangarorin kuma zasu sake tattaunawa nan da mako mai zuwa, saidai ba’a bayyana takaimaimai wajen da tattauanwar za ta wakana ba.

A gefen tattaunawar, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Esmaeil Baghaei ya shaidawa kafar yada labarai ta IRIB a birnin Muscat cewa, Iran na da manufa guda daya tabbatar da muradun kasa.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: harkokin wajen

এছাড়াও পড়ুন:

Karamar Hukumar Agwara ta Jinjinawa Gwamnati Bisa Tabbatar da Tsaron Rayuka da Dukiyoyin Jama’a

Daga Aliyu Lawal 

Karamar Hukumar Agwara da ke Jihar Neja ta ce za ta ci gaba da hada kai da Gwamnatin Tarayya ta Jiha Neja wajen tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’arta, musamman masu rauni.

Shugaban Karamar Hukumar, Alhaji Iliyasu Zakari, ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya rattaba hannu da kansa, wadda ya rabawa manema labarai a Minna, babban birnin jihar Neja.

Alhaji Iliyasu Zakari, wanda ya jaddada cewa kare rayuka da dukiyoyin jama’a shi ne ginshikin mulkinsa, ya kuma yaba wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu, Mai Ba Shugaban Kasa Shawara Kan Tsaro (NSA) Nuhu Ribadu, hukumomin tsaro da Gwamna Mohammed Umar Bago bisa rawar da suka taka wajen tabbatar da sakin dalibai ɗari da aka sace a makarantar Cocin Saint Mary’s Catholic da ke Papiri.

Alhaji Iliyasu Zakari ya ce: “Muna matuƙar godiya ga Shugaba Tinubu, Gwamna Umar Bago, Mai Ba Shugaban Kasa Shawara Kan Tsaro, Nuhu Ribadu, da jaruman jami’an tsaro bisa jajircewarsu wajen kare lafiyar ’ya’yanmu.”

Shugaban ya kuma yi kira da a ci gaba da yin addu’a da bayar da goyon baya ga hukumomi domin tabbatar da dawowar sauran ɗalibai da malamai da har yanzu ba a same su ba, yana mai cewa: “Muna da yakinin cewa, da irin wannan haɗin kai da kula da tsaro, sauran yara da malamansu za su dawo cikin iyalansu ba da jimawa ba.”

Sai dai Alhaji Iliyasu Zakari ya yi kira ga iyaye, al’ummar Neja da ’yan Najeriya gaba ɗaya da su kwantar da hankalinsu domin Gwamnatin Tarayya da ta Jihar Neja na aiki tare da hukumomin tsaro wajen tabbatar da sakin sauran ɗalibai da malamai da ke tsare a hannun masu garkuwa da mutane.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Amince Ya Ziyarci Beirut
  • Islami: Yaki Ba Zai Hana Iran Ci Gaba A Shirinta Na Makamashin Nukliya Ba
  • Yadda APC Da ADC Ke Amfana Da Rikicin Jam’iyyar PDP
  • Ayatollah Khamenei : Iran na samun ci gaba duk da kalubale da dama
  • Ma’aikatar Mata da Walwalar Jama’a ta Jihar Jigawa ta Kare Kasafin Kudinta a Gaban Majalisa
  • Ba ni da shirin ficewa daga PDP — Gwamnan Bauchi
  • Karamar Hukumar Agwara ta Jinjinawa Gwamnati Bisa Tabbatar da Tsaron Rayuka da Dukiyoyin Jama’a
  • Sakkwatawa na murnar kisan da sojoji suka yi wa mataimakin Bello Turji
  • An cire Tony Blair daga jerin wadanda zasu jagoranci Gaza
  • Yara masara zuwa makaranta barazana ne ga kasa — Shettima