Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro
Published: 12th, April 2025 GMT
Haka zalika, Kangye ya kuma tabbatar wa da al’umma cewa; jami’an tsaro na ci gaba da mayar da hankali wajen cafke fitaccen shugaban ‘yan ta’addan nan, Bello Turji.
Sannan, ya yi watsi da ikrarin da sojoji suka yi na cewa; sun dakile hare-haren makiyaya da ‘yan ta’adda da kuma barayin shanu da sauran makamantansu.
Da yake yin jawabi game da kyautata wa sojojin da suka jikkata, Kangye ya musanta zargin yin watsi da sojojin da suka samu raunuka.
Ya ce, “To, a iya sanina dangane da abin da hukumar sojoji ke yi, sojojinmu na samun isasshiyar kulawa, kuma kai dan jarida ne, da ka lura da lokacin hutun Sallah, za ka ga yadda babban hafsan soji da hafsan hafsoshin sojin sama da wasu manyan hafsoshi daga hedikwatar hukumar suka ziyarci sojojin, domin taya su murnar Sallah.
“Sannan kuma, zan iya fada muku cewa; hedikwatar rundunar sojojin Nijeriya, na kula da marasa lafiya da wadanda suka samu raunuka da wasu da ke bukatar a fitar da su zuwa kasashen waje, ana fitar da su, domin nema musu lafiya; wasu sun tafi Masar, wasu Turkiyya, wasu kuma Kasar Indiya. Kamar yadda muke magana yanzu, wasu har yanzu suna can suna samun kulawar likitoci a can.”
Ya kuma bayyana cewa, a ‘yan watannin da suka gabata, an raba wa sojojin da suka samu jikkata a fagen-daga gidaje.
Kangye ya kuma yi nuni da cewa, an raba wa sojojin da suka jikkatan gidajen kyauta ne, domin kuwa wasu daga cikinsu; ba za su iya dawowa fagen aiki ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Nijar
এছাড়াও পড়ুন:
Tsaro: Gwamnatin Kano za ta fara amfani da jirage marasa matuƙa a iyakokinta
Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya ce gwamnatinsa na shirin sayen jirage marasa matuƙa da wasu kayan aiki domin kare yankunan da ke iyakar Kano da Katsina.
Kakakin gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ne, ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba.
Gobara ta ƙone kasuwar katako a Abuja CBN ya kara yawan kudin da mutum zai iya cirewa a mako zuwa N500,000Gwamna Abba, ya bayyana haka ne lokacin da ya ziyarci sansanin rundunar haɗin gwiwa ta JTF, domin ganin yadda suke shirin kare al’umma daga hare-haren ’yan bindiga a yankunan Tsanyawa da Shanono.
Ya roƙi al’ummar yankunan da abin ya shafa da su riƙa bai wa jami’an tsaro bayanai masu amfani game da duk wani motsi na ’yan bindiga.
Gwamnan ya ce ya kai wa Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ziyara, domin neman taimako kan lamarin, inda shugaban ya amince da buƙatar da aka gabatar masa cikin gaggawa.
Ya umarci dakarun JTF da su yi duk mai yiwuwa wajen ceto mutanen da aka sace a Tsanyawa da Shanono.
“Mun san cewa waɗannan hare-hare sun jawo asarar rayuka, wasu kuma an yi garkuwa da su. Insha Allah za a ceto su,” in ji shi.
Gwamna Abba ya ce sun kai wannan ziyara ne domin fahimtar halin tsaron yankin da kuma ƙarfafa guiwar jami’an tsaro.
Ya ƙara da cewa irin wannan matsalar tsaro sabon abu ne a Kano, amma gwamnati na aiki tare da hukumomin tsaro domin magance ta.
A yayin ziyarar, ya jajanta wa iyalan mutanen da aka sace tare da tabbatar musu cewa gwamnati na ƙoƙarin ganin an dawo da su cikin gaggawa.
Rahotanni sun nuna cewa aƙalla mutum 10 aka sace a Tsanyawa da Shanono, ciki har da wata tsohuwa da ’yan bindiga suka hallaka.