Haka zalika, Kangye ya kuma tabbatar wa da al’umma cewa; jami’an tsaro na ci gaba da mayar da hankali wajen cafke fitaccen shugaban ‘yan ta’addan nan, Bello Turji.

Sannan, ya yi watsi da ikrarin da sojoji suka yi na cewa; sun dakile hare-haren makiyaya da ‘yan ta’adda da kuma barayin shanu da sauran makamantansu.

Da yake yin jawabi game da kyautata wa sojojin da suka jikkata, Kangye ya musanta zargin yin watsi da sojojin da suka samu raunuka.

Ya ce, “To, a iya sanina dangane da abin da hukumar sojoji ke yi, sojojinmu na samun isasshiyar kulawa, kuma kai dan jarida ne, da ka lura da lokacin hutun Sallah, za ka ga yadda babban hafsan soji da hafsan hafsoshin sojin sama da wasu manyan hafsoshi daga hedikwatar hukumar suka ziyarci sojojin, domin taya su murnar Sallah.

“Sannan kuma, zan iya fada muku cewa; hedikwatar rundunar sojojin Nijeriya, na kula da marasa lafiya da wadanda suka samu raunuka da wasu da ke bukatar a fitar da su zuwa kasashen waje, ana fitar da su, domin nema musu lafiya; wasu sun tafi Masar, wasu Turkiyya, wasu kuma Kasar Indiya. Kamar yadda muke magana yanzu, wasu har yanzu suna can suna samun kulawar likitoci a can.”

Ya kuma bayyana cewa, a ‘yan watannin da suka gabata, an raba wa sojojin da suka samu jikkata a fagen-daga gidaje.

Kangye ya kuma yi nuni da cewa, an raba wa sojojin da suka jikkatan gidajen kyauta ne, domin kuwa wasu daga cikinsu; ba za su iya dawowa fagen aiki ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Nijar

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan ci-rani 26 sun nitse a teku suna ƙoƙarin tsallakawa Turai

Akalla ’yan ci-rani 26 sun mutu bayan jiragen ruwan da suke ciki guda biyu sun nitse a teku a kusa da tsibirin Lampedusa na ƙasar Italiya.

Hukumar Kula da ’Yan Gudun Hijira ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce ana hasashen ƙarin wasu mutanen kuma sun ɓace yayin da ake ci gaba da aikin ceto su.

Allah zai kunyata masu ɗaukar nauyin ta’addanci a Zamfara — Gwamna Dauda Dalilan ƙaruwar mace-mace a hanyoyin Najeriya

Galibi dai ’yan ci-ranin da suka fito daga ƙasashen Afirka na ƙoƙarin tsallakawa nahiyar Turai ne domin samun ingantacciyar rayuwa.

Ko a ranar Laraba dai ma’aikatan ceto sun ce sun ceto mutum 60 da ransu, wadanda suka hada da maza 56 da kuma mata hudu, sannan aka kai su tsibirin na Lampedusa, kungiyar bayar da agaji ta Red Cross a kasar ta Italiya ta tabbatar.

Kakakin Hukumar Kula da ’Yan Gudun Hijira ta Majalisar Dinkin Duniya (IOM), Flavio Di Giacomo, ya ce akwai mutum 95 a cikin jiragen guda biyu da suka nitse.

Ya wallafa a shafukan sada zumunta cewa, “kasancewar an ceto mutum 60 da rai, ana fargabar akwai mutum 35 da suka mutu ko kuma suka ɓace.“

Hatsarin wanda ya ritsa da ’yan ci-ranin da suka taso daga ƙasar Libya shi ne na baya-bayan nan ga mutanen da ke kokarin tsallaka teku domin shiga nahiyar Turai.

Alkaluma sun nuna daga farkon shekarar nan zuwa yanzu, akalla mutum 675 ne suka rasa ransu ta irin wannan hanyar a kan iyakokin kasashen biyu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kai Ziyarar Gani Da Ido A Karamar Hukumar Gwiwa
  • Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya
  • UBEC Ta Kaddamar Da Makarantun Zamani 21 A Sassan Nijeriya
  • Duniyarmu A Yau: Ranar 40 Ta Imam Hussain (a) A Bana
  • Duniyarmu A Yau: Ranar 40 na Imam Hussain (a) Na Bana
  • Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa
  • An Bukaci Ficewar Marasa Lafiya da Likitoci daga Wani Babban Asbiti A birnin London
  • ’Yan ci-rani 26 sun nitse a teku suna ƙoƙarin tsallakawa Turai
  • ’Yan bindiga sun kashe tsohon malamin makaranta a Edo
  • Yadda Ƙananan Hukumomi Ke Yin Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina