HausaTv:
2025-07-12@09:07:57 GMT

MDD: Mafi Yawancin Wadanda Yaki Ya Ci A Gaza Mata Ne Da Kananan Yara

Published: 12th, April 2025 GMT

Hukumar da take kula da hakkin bil’adama ta MDD ta bayyana cewa; Mafi yawancin wadanda yaki ya rutsa da su a Gaza mata ne da kananan yara.

Mai Magana da yawun hukumar ta kare hakkin bil’adama ta MDD Rafina Shamdsani ce ta bayyana hakan a wurin taron hukumar da aka yi a birnin Geneva tana mai kara da cewa; Atsakanin watan Maris zuwa Aprilu na wannan shekara ta 20205 da ake ciki kadan, Isra’ila ta kai hare-hare har sau 224 akan gidajen mutane da kuma hemomin da ‘yan hijira suke ciki.

Har ila yau, hukumar ta kara da cewa; suna ci gaba gudanar da bincike akan wasu hare-hare 36 da sojojin Isra’ilan su ka kai da aka tabbatar da ya ci rayukan mutane da dama da su ka hada mata da kananan yara.

A nata gefen, kungiyar agaji ta “Red- Cross” ta yi gargadin cewa, kayan aikin da ake da su a cikin asibitocin da ake da su a cikin yankin sun kusa karewa.

Haka nan kuma kungiyar ta ce; ” A cikin yankuna da dama na Gaza, ba a iya samun ruwan sha, babu abinci, kuma babu wutar lantarki.

Ita kuwa ma’aikatar kiwon lafiya ta Gaza, ta yi kiran gaggawa domin a shigar da kayan aiki a cikin asibitoci da cibiyoyin kiwon lafiya. Haka nan kuma ta kara da cewa, da akwai masu fama da ciwon suga 80,000 sai masu hawan jini 110,000 ba su samun kula yadda ya dace.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

Dantsoho ya kara da cewa, nuna kwarewar ma’aikata na kara taimaka wa, wajen cimma burin da aka sanya a gaba, musamman a bangaren nuna yin gasa, a tafiyar da Tashohin Jiragen Ruwa.

“Ta irin wannan hanyar ce, za mu iya cimma bukatar da muke da ita da kuma cika muradin masu ruwa da tsaki, da ke a fannin, musamman domin mu kara karfafa karsashin ma’aikatan mu,” Inji Dantsoho.

Dantsoho ya kuma jinjinawa Minsitan ma’aikatar bunsa hada –hadar kasuwanci na kan Teku Adegboyega Oyetola, kan sahalewar Hukumar ta NPA, na yin karin girman ga ma’aikatan da suka amfana, wanda Hukumar ta jima, tana da bukatar yin hakan.

“Dole ne kuma in yabawa Ministanmu Adegboyega Oyetola, kan amincewar da ya yi, na kawo karshen batun yiwa ma’aikatan karin matsayin, ta hanyar gudanar masu da jarrabawar yin gwaji,” A cewar Shugaban.

A na sa jawabin madadin gamayyar kungiyoyin na Tashoshin Jiragen Ruwan kasar SSASCGOC, Kwamarade Bodunde, ya nuna jin dadinsa kan wannan karin matsayin da aka yiwa ma’aikatan.

“Muna kuma godiya, kan inganta walwalar ma’aikatan Hukumar ta NPA da kara inganta ayyukan ‘ya’yan kungiyar, musamman duba da irin yanayin matsin tattalin arzikin da ake fama da ita a kasar, Inji Bodunde.”

Shi kuwa, Janar Manaja a sashen tsare-tsare da samar da bayanai na Hukumar ta NPA Ikechukwu Onyemekara, ya bayyana cewa, zamanantar da kayan aikin Tashoshin Jiragen Ruwan kasar, hakan zai kara taimaka wa wajen kara inganta ayyukan ma’aikatan.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • HKI Ta Roki Amurka Ta Taimake Ta A Fada Da Kasar Yemen
  • Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 
  • NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma
  • Mayakan Huthi Sun Kara Kai Wasu Hare-Hare da Makamai Masu Linzami Kan BenGurio
  • Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana
  • Somaliya: Kungiyar Al-Shabab Ta Kai Wa Barikin Soja Hari A Birnin Magadishu
  • Isra’ila ta kashe Falasdinawa 24 a Zirin Gaza
  • Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Kara Kamfanoni 8 Na Yankin Taiwan Cikin Jerin Wadanda Aka Takaita Sayar Musu Kayayyaki
  • Yara miliyan 5.4 na fama da karancin abinci a jihohin arewa 9 – Red Cross
  • Kungiyar Hamas Ta Yi Fatali Da Mahangar Yahudawan Sahayoniyya Ta Neman Falasdinawa Su Rusuna Musu