Atiku ya jagoranci manyan ’yan siyasa sun ziyarci Buhari
Published: 11th, April 2025 GMT
Tsohon Mataimakin Shugaban Nijeriya kuma ɗan takarar shugaban ƙasa a 2023, Alhaji Atiku Abubakar ya ziyarci tsohon shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari a Kaduna.
Atiku ya samu rakiyar tsofaffin gwamnoni da suka haɗa da tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai da tsohon Gwamnan Sokoto Aminu Waziri Tambuwal da wasu jiga-jigan ’yan siyasa.
Kamar yadda aka wallafa bidiyon ziyarar a Shafin Atiku na Facebook, an rubuta cewa sun ziyarci Buharin, kuma sun sha dariya.
“A matsayina na Wazirin Adamawa, na tsaya domin gudanar da shagungulan Sallah a Adamawa, inda na wakilci Sarkin Adamawa, Lamiɗo Fombina a wasu shagulgulan.
“Yau kuma na kai ziyarar gaisuwar Sallah ga Muhammadu Buhari wanda ya shugabanci ƙasar a tsakanin 2015 zuwa 2023. Na ji daɗin ziyarar, saboda kamar yadda ya saba, ya yi ta ba mu dariya sai da haƙarƙarina suka yi zafi.” Cewar Atiku.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Alhaji Atiku Abubakar Aminu Waziri Tambuwal Muhammadu Buhari
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Tana Daukar Bakwancin Taron BRICS Na Binciken Kimiya Da Kuma Ci Gaban Ilmi
Tehran tana daukar bakwancin taron kwamitin bincike da ci gaban na kungiyar BRICS karo na 7Th wanda ya nuna irin yadda kasar Iran take ci gaba a cikin ilmin bincike da kuma na ci gaba.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto masu taron na fadar cewa kasar Iran ta na samun ci gaban a zo a gani a bangaren ci gaban ilmin zamani a fannoni daban-daban.
Wannan kuma ya bayyana cewa, wannan ya nuna irin ci gaban da kasashen BRICS suke samu wanda zai babu damar sauya duniya, ko samar da sabuwar duniya tare da kasashen global South, ko kasashe masu tasowa.
Labarin ya kara da cewa wannan ya nuna irin yadda kungiyar BRICS take kokarin ganin ta rage ko kuma ta kawo karshen dogaro da kasashen yamma a ilmin bincilke da ilmin ci gaba na zamani.
An kafa kwamitin bincike da kuma ci gaba a manya-manyan ayyuka na kungiyar BRICS ne a shekara ta 2015 kuma kwamitin yana daga cikin manya-manyan shirye-shiryen BRICS a fagen ilmi da kimiyar zamani. Kuma a halin yanzu kwamitin yana kula da ayyukan bincike har 13 wadanda yake ayyuka a kansu. Kasashen China, Rasha, India, Brazil, Afirka ta Kudu, Hadaddiyar daular Larabawa, Iran da Indonasia ne suke halattan taron na Tehran.
Taron ya maida hankali wajen ayyukan bincike kan manya-manyan ayyuka, kirkiran hanyoyin ci gaba da kuma hanyoyin samar da kudde don manya-manyan ayyukan bincike na ilmin kimiya.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Nasarar Da Iran Ta Samu A Yakin Kwanaki 12 Kan HKI Yana Jawo Hankalin Kasashen Duniya December 10, 2025 ‘Yan Ta’adda Sun Kai Hare-Hare Kan Sojojin Pakistan Sun Kuma Kashe 6 Daga Cikinsu December 10, 2025 Majalisar Dattawa Ta Bawa Tunubu Damar Kai Sojoji Zuwa Kasar Benin December 10, 2025 Ministan Makamashi: Iran Tana Da Sanayya Ta Ilimi Na Samar Da Hadari Domin Yin Ruwan Sama December 10, 2025 Kasar China Ta Zartar Da Hukuncin Kisa Akan Wani Babban Jami’in Banki December 10, 2025 Ganawa A Tsakanin Mataimakan Ministocin Waje Na Kasashen Saudiyya, China Da Minista Arakci Na Iran December 10, 2025 Antoni Gutress Ya Yi Allawadai Da Kutsen Da “Isra’ila” Ta Yi A Cibiyar Unrwa December 10, 2025 Iran da Saudiyya sun sake jaddada fadada dangantakarsu December 9, 2025 Faransa ta ce da hannunta aka dakile juyin mulki a Benin December 9, 2025 RSF : Rabin ‘Yan jarida 67 da aka kashe a bana, a Zirin Gaza ne December 9, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci