Aminiya:
2025-12-06@02:25:23 GMT

Atiku ya jagoranci manyan ’yan siyasa sun ziyarci Buhari

Published: 11th, April 2025 GMT

Tsohon Mataimakin Shugaban Nijeriya kuma ɗan takarar shugaban ƙasa a 2023, Alhaji Atiku Abubakar ya ziyarci tsohon shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari a Kaduna.

Atiku ya samu rakiyar tsofaffin gwamnoni da suka haɗa da tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai da tsohon Gwamnan Sokoto Aminu Waziri Tambuwal da wasu jiga-jigan ’yan siyasa.

An gano gawar makiyayi da ƙwato shanu a Filato Boko Haram: Zulum ya yi ganawar sirri da Shugabannin sojoji

Kamar yadda aka wallafa bidiyon ziyarar a Shafin Atiku na Facebook, an rubuta cewa sun ziyarci Buharin, kuma sun sha dariya.

“A matsayina na Wazirin Adamawa, na tsaya domin gudanar da shagungulan Sallah a Adamawa, inda na wakilci Sarkin Adamawa, Lamiɗo Fombina a wasu shagulgulan.

“Yau kuma na kai ziyarar gaisuwar Sallah ga Muhammadu Buhari wanda ya shugabanci ƙasar a tsakanin 2015 zuwa 2023. Na ji daɗin ziyarar, saboda kamar yadda ya saba, ya yi ta ba mu dariya sai da haƙarƙarina suka yi zafi.” Cewar Atiku.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Alhaji Atiku Abubakar Aminu Waziri Tambuwal Muhammadu Buhari

এছাড়াও পড়ুন:

Na kashe N100bn a kan harkar tsaro a 2025 — Zulum

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya ce gwamnatinsa ta kashe kusan Naira biliyan 100 a wannan shekara domin inganta tsaro a faɗin jihar.

Ya bayyana haka ne lokacin da ya ziyarci Sarkin Uba, inda ya yi masa jaje kan hare-haren da suka yi sanadin mutuwar mutane da dama.

Jami’an tsaro sun kama masu garkuwa da mutane 7 a Gombe Najeriya ta shigo da tataccen man fetur na tiriliyan 12.8 cikin watanni 15

Zulum ya yaba wa jami’an tsaro da al’umma kan ceto manoman mata 12 da aka yi garkuwa da su.

Gwamnan, ya ce matsalar tsaro na hana samar da manyan ayyukan ci gaba a yankin.

Ya kuma sake alƙawarin gina makarantu, asibiti, hanyoyi, cibiyar kwamfuta, cibiyar JAMB da kuma Kwaleji a Uba.

“Ziyarar na zo ne don duba yanayin tsaro. Zan gana da jami’an tsaro domin tabbatar da Askira/Uba sun samu kariya.

“Ba za a samu zaman lafiya ba idan babu tsaro. Muna da shirin samar da hanyoyi, ilimi da kiwon lafiya,” in ji Zulum.

Sarkin ya gode wa gwamnan; “Ka yi mana abubuwa da dama. Da doka za ta ba da dama, da mun roƙe ka, ka ci gaba da mulki. Allah Ya yi maka albarka.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun kama tsohon shugaban PCACC, Muhuyi Rimin Gado a Kano
  • Dorinar ruwa ta kashe mutum 2, ta jikkata 6 a Gombe
  • Na kashe N100bn a kan harkar tsaro a 2025 — Zulum
  • Najeriya: Tinubu Ya Nada Wasu Karin Jakadu 65, Sanatoci Da Tsoffin Gwamnoni Na Daga Cikinsu
  • Ziyarar Putin a Indiya alama ce da ke nuna cewa New Delhi na yin watsi da gargadin Trump?
  • Tinubu ya naɗa tsohon kantoman Ribas da Dambazau a matsayin Jakadun Najeriya
  • NAJERIYA A YAU: Abun Da Masu Ruwa Da Tsaki Ke Yi Na Dakile Laifuka A Wurin Matasa
  • Shugaba Tinubu Ya Rantsar da Sabon Shugaban Hukumar Kidaya, Kwamishinoni da Manyan Sakatarori
  • Rikicin Kungiyoyin Asiri Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Wani Matashi A Jihar Kwara
  • Har yanzu ban bar yin waqa ba-Yusuf Lazio