Atiku ya jagoranci manyan ’yan siyasa sun ziyarci Buhari
Published: 11th, April 2025 GMT
Tsohon Mataimakin Shugaban Nijeriya kuma ɗan takarar shugaban ƙasa a 2023, Alhaji Atiku Abubakar ya ziyarci tsohon shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari a Kaduna.
Atiku ya samu rakiyar tsofaffin gwamnoni da suka haɗa da tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai da tsohon Gwamnan Sokoto Aminu Waziri Tambuwal da wasu jiga-jigan ’yan siyasa.
Kamar yadda aka wallafa bidiyon ziyarar a Shafin Atiku na Facebook, an rubuta cewa sun ziyarci Buharin, kuma sun sha dariya.
“A matsayina na Wazirin Adamawa, na tsaya domin gudanar da shagungulan Sallah a Adamawa, inda na wakilci Sarkin Adamawa, Lamiɗo Fombina a wasu shagulgulan.
“Yau kuma na kai ziyarar gaisuwar Sallah ga Muhammadu Buhari wanda ya shugabanci ƙasar a tsakanin 2015 zuwa 2023. Na ji daɗin ziyarar, saboda kamar yadda ya saba, ya yi ta ba mu dariya sai da haƙarƙarina suka yi zafi.” Cewar Atiku.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Alhaji Atiku Abubakar Aminu Waziri Tambuwal Muhammadu Buhari
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Jigawa Ta Bukaci Kananan Hukumomi Su Gabatar da Kasafin Kudinsu a Zangon Farko na Sabuwar Shekara
Daga Usman Muhammad Zaria
Shugaban kwamatin kananan hukumomi na majalisar dokokin jihar Jigawa, Alhaji Aminu Zakari, ya bukaci ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar tabbatar da ganin cewa kananan hukumonin jihar 27 sun wallafa cikakken kundin kasafin kudadensu cikin zangon farko na sabuwar shekara.
Alhaji Aminu Zakari wanda shi ne wakilin mazabar Gwiwa, ya bayyana haka ne lokacin tantance kiyasin kasafin kudin sabuwar shekara na ma’aikatar kananan hukumomi.
Ya kuma yi kira ga ma’aikatar da ta duba batun rashin biyan albashi ga wasu daga cikin nadaddun kansiloli, kasancewar yanzu haka akwai nadaddun kansiloli 21 da ba sa samun albashin su.
Ya kara da cewar, kwamitin ya samu koke kan tsallake albashin wasu ma’aikatan kananan hukumomi sakamakon aikin tantance ma’aikata na IPPS ta yadda wasu ma’aikatan sun yi ritaya ba tare sun karbi albashin da aka tsallake su ba.
A nasa jawabin, kwamishinan ma’aikatar kananan hikumomin Jihar, Alhaji Ibrahim Garba Hannun Giwa, ya bada tabbacin yin duk abinda ya kamata domin magance wadannan batutuwa.
Ya ce ma’aikatar ta yi kiyasin kashe naira miliyan dubu 13 domin gudanar da manyan ayyuka da harkokin yau da kullum a shekarar 2026.
Hannun Giwa, ya kuma bayyana cewar daga cikin manyan ayyuka akwai gyaran ofisoshin shiyya na jami’an duba kananan hukumomi guda 7.
Yana mai cewar za’a kuma kammala aikin ginin sabbin ofisoshi dake kananan hukumomin Babura da Kafin Hausa.
Kazalika, Kwamishinan ya ce za’a sayi motocin aiki da babura ga jami’an duba kananan hukimomi da mataimakansu, tare da kudaden gudanarwa domin ziyarar aiki a lungu da sakon kananan hukumomin jihar 27.