Aminiya:
2025-11-22@14:50:17 GMT

An gano gawar makiyayi da ƙwato shanu a Filato

Published: 11th, April 2025 GMT

Dakarun rundunar ‘Operation Safe Haven’ da ke aikin tabbatar da zaman lafiya a Jihar Filato, sun nemo gawar wani makiyayi mai shekaru 16 da ya ɓace tare da ƙwato shanu sama da 50 da aka sace.

 Daily Trust ta rawaito cewa, sojojin sun gano gawar makiyayin da ya ɓace tare da wasu Fulani makiyaya a ranar Juma’ar nan.

Boko Haram: Zulum ya yi ganawar sirri da Shugabannin sojoji An saki fasto an kuma tsare wanda ya kai kuɗin fansa

Makiyayin Abdullahi Muhammad mai shekara 16 da ya ɓace, kuma an samu rahoton an yi awon gaba da shanu sama da 70 a yankin Ariri, ƙaramar hukumar Bassa, a lokacin da suke kiwo a yankin.

Sai dai a baya, Danjuma Auta, babban sakataren ƙungiyar raya Irigwe (IDA), ya musanta batun satar shanu a yankin, yana mai zargin cewa an kashe mambobinsu da dama a cikin makonni uku da suka gabata, kuma suna fuskantar ƙalubale na hare-hare.

A cewar Ya’u Idris, shugaban Ƙungiyar MACBAN a garin Bassa, wanda ya tabbatar da samun nasarar gano gawar makiyayin da ya ɓace, sojojin OPSH tare da wasu makiyaya ne suka tsinto gawar a wani kabari mara zurfi, tare da wasu makiyaya a gaɓar kogi da ke kusa da babban yankin Ariri.

Ya ce, an fille kan makiyayin, aka datse hannunsa na hagu.

Da yake ƙarin bayani, shugaban ya ce, “Mun tono gawar kuma muka mayar da shi gida don yin sallar jana’iza, an ceto sama da kashi 80% na shanun, muna godiya ga jami’an tsaro musamman jami’an tsaron OPSH bisa ƙoƙarin da suka yi wajen ƙwato gawar da shanu.”

Mai magana da yawun rundunar ‘Operation Safe Haven’ Manjo Samson Zhakom da DSP Alabo Alfred na rundunar ’yan sandan jihar, har yanzu ba su mayar da martani ga saƙon da wakilinmu ya aika masu kan wannan lamari ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Operation Safe Haven da ya ɓace

এছাড়াও পড়ুন:

CORET, ECOWAS Sun Hada Matasa Da Wasu Abokan Hulda Don Inganta Kiwo Da Madara

 

Kungiyar Haɗin Kan Masu Kiwo na Gargajiya ta Afirka (CORET) tare da haɗin gwiwar ECOWAS sun hada matasan da aka horar da su da manyan abokan holda don bunkasa kiyo da bunkasa yawan madara a jihohin Kaduna da Jigawa.

 

A yayin zaman karawa juna sani a Kaduna, Koodinetan Aikin na CORET Dr. Umar Ardo Abdul, ya ce an shirya wannan zama ne domin haɗa matasan da aka horar da su da masu ruwa da tsaki a harkan kiyo da bunkasa yawan madara na gwamnati da masu zaman kansu, domin a horas da su hanyoyin samun aikin yi da kuma bunkasa yawan madara.

 

Wannan shiri na daga cikin Aikin ECOWAS na karfafa samar da ayyukan yi ga matasa da kuma bunkasa darajar madara, wanda yake ɗaukar tsawon shekaru uku, kuma an kaddamar da shi ne domin koya wa matasa ƙwarewar aiki tare da samar musu damar samun kuɗin shiga a cikin fannin kiwo.

 

Koodinetan Aikin, Dr. Umar Ardo Abdul, ya bayyana cewa an yi wa matasa 1,350 rajista a Kaduna da Jigawa.

 

A cewarsa, matasa 26 daga jihohin Kaduna da Jigawa yanzu an haɗa su da masana waɗanda za su tallafa musu a ayyukan yin allurar rigakafi da taimakon lafiyar dabbobi da aikin yaɗa ilimi, da kuma samar da kayan kiwo.

 

Ya yi bayani cewa zaman ya haɗa kwararrun likitocin dabbobi, ma’aikatan yaɗa ilimin kiwo, masu yin dasa ramin maniyyi da masu sarrafa abincin dabbobi da sauran masu ruwa da tsaki a kiwo domin gina ƙaƙƙarfan cibiyar ayyuka.

 

Dr. Umar Ardo ya ce manufar ita ce a tabbatar matasan sun yi amfani da ƙwarewar da suka samu wajen ba da muhimman ayyukan kiwo, samun kuɗin shiga, da kuma tallafawa makiyaya da manoma a yankunansu.

 

Yace ma’aikatar aikin gona ta Jihar Kaduna da Cibiyar Binciken Samar da Dabbobi ta Ƙasa (NAPRI) a matsayin muhimman abokan aikin gwamnati, yana mai cewa NAPRI cibiyar bincike ce da a ke dogaro da ita wajen binciken kiwo, samar da rigakafin dabbobi da kuma kayayyakin kiwo.

 

Koodinetan ya ce gwamnati na da muhimmiyar rawa ta tsare-tsare a fannin kiwon lafiya na dabbobi, rigakafi da kuma samar da kaji, yayin da kamfanonin masu zaman kansu ke taka rawa wajen samar da magungunan dabbobi da kayan kiwo, waɗanda suka zama ginshiƙai ga masu cin gajiyar shirin.

 

Dr. Umar Ardo ya jaddada cewa CORET, a matsayinta na ƙungiyar haɗin kan masu kiwo ta nahiyar Afirka, ta kuduri aniyar cike gibin da ke tsakanin hukumomin gwamnati, cibiyoyin bincike, kamfanoni masu zaman kansu da matasan da aka horar domin inganta harkar kiwo da bunkasa madara.

 

A nasa jawabin, wakilin Hukumar Ilimin Makiyaya ta Ƙasa, Abubakar Lawal Boro, ya ce tsarin PPP (Haɗin Gwiwar Gwamnati da Masu Zaman Kansu) shi ne ginshiƙin cigaban kiwo mai ɗorewa, domin gwamnati na samar da tsarin aiki da jagoranci, yayin da kamfanoni ke samar da muhimman kayayyaki.

Ya yi kira ga iyalan makiyaya su bai wa ilimi muhimmanci ta hanyar mayar da ‘ya’yansu makaranta, yana nuna damuwa kan yawaitar yaran da ba sa zuwa makaranta da tasirin rashin tsaro ga yunkurin wayar da kai.

 

Ɗaya daga cikin mahalarta, Anas Ibrahim, ya bayyana wannan horo a matsayin mai matuƙar amfani kuma ya zo a kan lokaci.

 

Ya ce zaman ya kasance cikin tsari kuma yana ɗaya daga cikin mafi inganci da suka halarta, inda ya faɗaɗa musu fahimtar lafiyar dabbobi, kula da abincin kiwo, da hulɗa da masu samar da ayyukan kiwo.

 

Wani mahalarta kuma, Rabiu Adamu daga Ladugga, ya yaba wa CORET da abokan aikinta bisa samar da dandalin da ya bai wa masu kiwo damar samun damar magungunan dabbobi masu inganci, abincin kiwo, da iri na kiwo da za su inganta kiwon madara.

COV: Adamu Yusuf

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tuƙin ganganci: KASTELEA  Ƙaddamar Da gangamin wayar da kai a Zariya
  • Mutane 315 ne suka ɓace bayan hari a makaranta Neja
  • Gobara ta lalata gidaje 40 a sansanin ’yan gudun a Borno
  • Duniyarmu A Yau: Sabon Kuduri Mai Yin Allawadai Da Iran A Hukumat IAEA
  • Dalibai a Jihohin Arewa Maso Yamma Sun Koka Game da Ƙalubalen Tsaro a Yankin
  • CORET, ECOWAS Sun Hada Matasa Da Wasu Abokan Hulda Don Inganta Kiwo Da Madara
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Dalibai Mata 25 a Jihar Kebbi 
  • Najeriya ta ɗora alhakin taɓarɓarewar harkokin tsaronta kan Amurka
  • Hukumar Kula Da Jiragen Sama Ta Najeriya Ta ci Tarar Kamfanin Jiragen Sama Na Qatar
  • Tankin ruwa ya kashe mutum 4, wasu sun jikkata a Jigawa