An gano gawar makiyayi da ƙwato shanu a Filato
Published: 11th, April 2025 GMT
Dakarun rundunar ‘Operation Safe Haven’ da ke aikin tabbatar da zaman lafiya a Jihar Filato, sun nemo gawar wani makiyayi mai shekaru 16 da ya ɓace tare da ƙwato shanu sama da 50 da aka sace.
Daily Trust ta rawaito cewa, sojojin sun gano gawar makiyayin da ya ɓace tare da wasu Fulani makiyaya a ranar Juma’ar nan.
Makiyayin Abdullahi Muhammad mai shekara 16 da ya ɓace, kuma an samu rahoton an yi awon gaba da shanu sama da 70 a yankin Ariri, ƙaramar hukumar Bassa, a lokacin da suke kiwo a yankin.
Sai dai a baya, Danjuma Auta, babban sakataren ƙungiyar raya Irigwe (IDA), ya musanta batun satar shanu a yankin, yana mai zargin cewa an kashe mambobinsu da dama a cikin makonni uku da suka gabata, kuma suna fuskantar ƙalubale na hare-hare.
A cewar Ya’u Idris, shugaban Ƙungiyar MACBAN a garin Bassa, wanda ya tabbatar da samun nasarar gano gawar makiyayin da ya ɓace, sojojin OPSH tare da wasu makiyaya ne suka tsinto gawar a wani kabari mara zurfi, tare da wasu makiyaya a gaɓar kogi da ke kusa da babban yankin Ariri.
Ya ce, an fille kan makiyayin, aka datse hannunsa na hagu.
Da yake ƙarin bayani, shugaban ya ce, “Mun tono gawar kuma muka mayar da shi gida don yin sallar jana’iza, an ceto sama da kashi 80% na shanun, muna godiya ga jami’an tsaro musamman jami’an tsaron OPSH bisa ƙoƙarin da suka yi wajen ƙwato gawar da shanu.”
Mai magana da yawun rundunar ‘Operation Safe Haven’ Manjo Samson Zhakom da DSP Alabo Alfred na rundunar ’yan sandan jihar, har yanzu ba su mayar da martani ga saƙon da wakilinmu ya aika masu kan wannan lamari ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Operation Safe Haven da ya ɓace
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kano ta nemi a binciki Ganduje kan zargin kalaman ta da hankali
Majalisar Zartarwa ta Jihar Kano ta nemi hukumomin tsaro su gaggauta bincikar tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje, kan zarginsa da kalaman tayar da hankali.
Wannan na zuwa ne bayan kammala zaman majalisar zartarwa na 34 da aka yi ranar Alhamis a Fadar Gwamnatin Kano.
Yadda mutane suka yi cikar ƙwari don halartar jana’izar Sheikh Dahiru Bauchi CAF Tayi Watsi Da Alƙalan Wasan Nijeriya a Kofin Afrika Na 2025Zaman ya mayar da hankali kan maganganun da Ganduje da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin suka yi, inda suka ce Kano na ƙara fuskantar barazanar hare-haren ’yan bindiga.
Ganduje ya bayyana aniyar ɗaukar mutum 12,000 aiki wanda hukumar Hisbah ta sallama daga aiki, a wata ƙungiya mai alaka da ake kira da “Khairul Nas”.
Da yake zantawa da manema labarai ranar Juma’a, Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida, Ibrahim Abdullahi Waiya, ya ce waɗannan maganganu na iya kawo koma baya ga harkar tsaro da ƙoƙarin da gwamnatin jihar ke yi.
Majalisar ta kuma nuna damuwarta cewa ƙasa da awanni 48 bayan yin waɗannan maganganu, aka sake kai hari wasu yankuna na jihar.
Gwamnatin jihar ta sake godewa Gwamnatin Tarayya da hukumomin tsaro kan goyon bayan da suke bayarwa wajen yaƙi da matsalolin tsaro.
Haka kuma ta yi gargaɗin cewa ba za ta bari wani ko wata ƙungiya ta kafa haramtacciyar rundunar tsaro ba a Jihar Kano.
A ƙarshe, gwamnatin ta roƙi jami’an gwamnati da’yan siyasa su guji yin maganganun da ka iya tayar da hankali.
Ta kuma tabbatar wa mazauna jihar cewa za ta ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da zaman lafiya da doka a faɗin Kano.