An gano gawar makiyayi da ƙwato shanu a Filato
Published: 11th, April 2025 GMT
Dakarun rundunar ‘Operation Safe Haven’ da ke aikin tabbatar da zaman lafiya a Jihar Filato, sun nemo gawar wani makiyayi mai shekaru 16 da ya ɓace tare da ƙwato shanu sama da 50 da aka sace.
Daily Trust ta rawaito cewa, sojojin sun gano gawar makiyayin da ya ɓace tare da wasu Fulani makiyaya a ranar Juma’ar nan.
Makiyayin Abdullahi Muhammad mai shekara 16 da ya ɓace, kuma an samu rahoton an yi awon gaba da shanu sama da 70 a yankin Ariri, ƙaramar hukumar Bassa, a lokacin da suke kiwo a yankin.
Sai dai a baya, Danjuma Auta, babban sakataren ƙungiyar raya Irigwe (IDA), ya musanta batun satar shanu a yankin, yana mai zargin cewa an kashe mambobinsu da dama a cikin makonni uku da suka gabata, kuma suna fuskantar ƙalubale na hare-hare.
A cewar Ya’u Idris, shugaban Ƙungiyar MACBAN a garin Bassa, wanda ya tabbatar da samun nasarar gano gawar makiyayin da ya ɓace, sojojin OPSH tare da wasu makiyaya ne suka tsinto gawar a wani kabari mara zurfi, tare da wasu makiyaya a gaɓar kogi da ke kusa da babban yankin Ariri.
Ya ce, an fille kan makiyayin, aka datse hannunsa na hagu.
Da yake ƙarin bayani, shugaban ya ce, “Mun tono gawar kuma muka mayar da shi gida don yin sallar jana’iza, an ceto sama da kashi 80% na shanun, muna godiya ga jami’an tsaro musamman jami’an tsaron OPSH bisa ƙoƙarin da suka yi wajen ƙwato gawar da shanu.”
Mai magana da yawun rundunar ‘Operation Safe Haven’ Manjo Samson Zhakom da DSP Alabo Alfred na rundunar ’yan sandan jihar, har yanzu ba su mayar da martani ga saƙon da wakilinmu ya aika masu kan wannan lamari ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Operation Safe Haven da ya ɓace
এছাড়াও পড়ুন:
Tuƙin ganganci: KASTELEA Ƙaddamar Da gangamin wayar da kai a Zariya
Hukumar Kula da Tsaftace Muhalli da Ababen Hawa ta Jihar Kaduna (KASTELEA) ta ƙaddamar da yaƙin wayar da kan jama’a na watannin ƙarshen shekara na shekarar 2025 a Tashar Motoci ta Malam Nasiru El-Rufa’i da ke ’Yan Ƙarfe, Sabon Gari, Zariya.
Taron yaƙin wayar da kan jama’a na ‘Watannin Ember’ na shekarar 2025 mai taken: “Tafiyar aminci ana cimma ta ta hanyar tuƙi cikin tsaro,” ya samu halartar hukumomin tsaro daban-daban da ke da ƙudirin rage haɗurra a kan manyan hanyoyin jihar
A wajen taron, Sarkin Zazzau, Malam Ahmad Nuhu Bamalli, ya jaddada muhimmancin rawar da kowa a cikin al’umma zai taka wajen tabbatar da tsaron hanya da kuma tuƙi cikin natsuwa.
Wakilin Sarkin a taron, Injiniya Ibrahim Balarabe Musa, ya bayyana cewa harkar kula da zirga-zirgar ababen hawa aiki ne da ya haɗa hukumomi da dama.
Mutane 315 ne suka ɓace bayan hari a makaranta Neja Sace ɗalibai: An rufe makarantu a Katsina da Taraba“Batun zirga-zirga ba na hukuma ɗaya ba ne. Rundunar ’yan sanda, ma’aikatan kashe gobara, Sibil Difens Hukumar Kiyaye Haɗurra ta Ƙasa (FRSC) duk suna da rawar da za su taka wajen cimma manufa ɗaya — tsaro,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa wayar da kan jama’a kan tsaro a hanya aiki ne na kullum, tare da yaba wa jajircewar ma’aikatan tsaro.
‘Watannin Ember’ da cunkoson hanyaA nata jawabin, Shugabar KASTELEA, Karla AbdulMalik, ta bayyana cewa Watannin Ember — daga Satumba zuwa Disamba — sukan fi fuskantar cunkoso sakamakon tafiye-tafiyen al’umma domin bukukuwan ƙarshen shekara.
Ta ce yawan zirga-zirgar ababen hawa a wannan lokaci kan haifar da cunkoso, tuƙin ganganci fa kuma karuwar hadurra, lamarin da ke janyo asarar rayuka da dukiya.
“Mun zo ne domin wayar da kan jama’a su bi ƙa’idojin hanya, tare da ƙarfafa wa fasinjoji gwiwa su tsawatar idan suka ga direba na tuƙi cikin hatsari. Kauce wa haɗurra nauyi ne da ya rataya a kan kowa,” in ji ta.
Ta buƙaci direbobi da ke cikin jihar ko masu wucewa su kiyaye dokokin hanya, su kuma rinƙa tuƙi cikin natsuwa don tsira da rayuwar al’umma.
Kiran FRSC da ƙungiyoyin sufuriA nasa ɓangaren, Kwamandan Shiyyar Zariya na Hukumar FRSC, Nasiru Abdullahi Falgore, wanda SRC Kabiru Kabiru Mado ya wakilta, ya bayyana wannan lokaci a matsayin na tsananin taka-tsantsan.
Ya nuna damuwa kan yawaitar mutuwar mutane da asarar dukiya, tare da kira ga direbobi su bi doka su kuma ɗauki matakan rage haɗurra.
Daga ɓangaren kungiyoyin sufuri, Mataimakin Shugaban NARTO na Jihar Kaduna, Sa’idu Mustapha Basawa, ya bayyana kyakkyawar hulɗar da ke tsakaninsu da hukumomin tsaro.
Ya kuma buƙaci gwamnati ta ƙara sanya alamun hanya a wurare masu muhimmanci, tare da jaddada buƙatar direbobi su riƙa bin ƙa’idojin hanya.