Aminiya:
2025-11-24@04:59:36 GMT

An gano gawar makiyayi da ƙwato shanu a Filato

Published: 11th, April 2025 GMT

Dakarun rundunar ‘Operation Safe Haven’ da ke aikin tabbatar da zaman lafiya a Jihar Filato, sun nemo gawar wani makiyayi mai shekaru 16 da ya ɓace tare da ƙwato shanu sama da 50 da aka sace.

 Daily Trust ta rawaito cewa, sojojin sun gano gawar makiyayin da ya ɓace tare da wasu Fulani makiyaya a ranar Juma’ar nan.

Boko Haram: Zulum ya yi ganawar sirri da Shugabannin sojoji An saki fasto an kuma tsare wanda ya kai kuɗin fansa

Makiyayin Abdullahi Muhammad mai shekara 16 da ya ɓace, kuma an samu rahoton an yi awon gaba da shanu sama da 70 a yankin Ariri, ƙaramar hukumar Bassa, a lokacin da suke kiwo a yankin.

Sai dai a baya, Danjuma Auta, babban sakataren ƙungiyar raya Irigwe (IDA), ya musanta batun satar shanu a yankin, yana mai zargin cewa an kashe mambobinsu da dama a cikin makonni uku da suka gabata, kuma suna fuskantar ƙalubale na hare-hare.

A cewar Ya’u Idris, shugaban Ƙungiyar MACBAN a garin Bassa, wanda ya tabbatar da samun nasarar gano gawar makiyayin da ya ɓace, sojojin OPSH tare da wasu makiyaya ne suka tsinto gawar a wani kabari mara zurfi, tare da wasu makiyaya a gaɓar kogi da ke kusa da babban yankin Ariri.

Ya ce, an fille kan makiyayin, aka datse hannunsa na hagu.

Da yake ƙarin bayani, shugaban ya ce, “Mun tono gawar kuma muka mayar da shi gida don yin sallar jana’iza, an ceto sama da kashi 80% na shanun, muna godiya ga jami’an tsaro musamman jami’an tsaron OPSH bisa ƙoƙarin da suka yi wajen ƙwato gawar da shanu.”

Mai magana da yawun rundunar ‘Operation Safe Haven’ Manjo Samson Zhakom da DSP Alabo Alfred na rundunar ’yan sandan jihar, har yanzu ba su mayar da martani ga saƙon da wakilinmu ya aika masu kan wannan lamari ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Operation Safe Haven da ya ɓace

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan Sanda a Zamfara Sun Ceto Mutane 25 Bayan Dakile Harin ’Yan Bindiga a Damba

Daga Aminu Dalhatu

Rundunar ’Yan Sanda a Jihar Zamfara ta ce ta samu nasarar ceto mutune 25 da aka yi  yunkurin sacewa, bayan  wani hari da ’yan bindiga suka kai wa kauyen Kuraje da ke yankin Damba a Karamar Hukumar Gusau.

Wata sanarwa da Jami’in Hulda da Jama’a na Rundunar, DSP Yazid Abubakar, ya fitar ta bayyana cewa lamarin ya faru ne a daren Juma’a 21 ga watan Nuwamban 2025, da misalin karfe 10 saura kwara, lokacin da gungun ‘yan bindiga dauke da makamai suka mamaye yankin, suna harbe-harbe tare da tasa keyar  mata 10 da yara 15 domin tafiyada su.

Sanarwar ta ce bayan samun kiran gaggawa, tawagar sintiri ta ’yan sanda daga sashen Damba da Sashen Ayyuka na Gusau tare da hadin guiwar jami’an tsaro na sa kai wato Community Protection Guards (CPG) sun hanzarta isa yankin.

Jami’an sun bi diddigin ’yan bindigar da suka tsere sannan suka shiga wani salon aiki na dabaru wanda ya kai ga kubutar da dukkan mutanen da aka sace.

DSP Abubakar ya ce an garzaya da wadanda aka ceto zuwa Sabongari Damba domin tabbatar da tsaronsu, duba lafiyar su da tantance su kafin a mika su ga iyalansu.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Zamfara, CP Ibrahim Balarabe Maikaba, ya jinjinawa jarumta da kwarewar jami’an da suka gudanar da aikin.

Ya kuma tabbatar da kudirin rundunar na ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin jama’ar jihar.

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga sun kashe ’yan sanda 5 a Bauchi
  • An gano wurin da ’yan bindiga ke tsare da ɗalibai 25 da aka sace a Kebbi
  • An rufe makarantun Filato saboda matsalar tsaro
  • H-JRBDA ta yi alƙawarin magance ambaliyar ruwa a Jigawa
  • ’Yan Sanda a Zamfara Sun Ceto Mutane 25 Bayan Dakile Harin ’Yan Bindiga a Damba
  • Mutane 315 ne suka ɓace bayan hari a makaranta Neja
  • Gobara ta lalata gidaje 40 a sansanin ’yan gudun a Borno
  • Duniyarmu A Yau: Sabon Kuduri Mai Yin Allawadai Da Iran A Hukumat IAEA
  • Dalibai a Jihohin Arewa Maso Yamma Sun Koka Game da Ƙalubalen Tsaro a Yankin
  • CORET, ECOWAS Sun Hada Matasa Da Wasu Abokan Hulda Don Inganta Kiwo Da Madara