Aminiya:
2025-11-12@12:06:27 GMT

An gano gawar makiyayi da ƙwato shanu a Filato

Published: 11th, April 2025 GMT

Dakarun rundunar ‘Operation Safe Haven’ da ke aikin tabbatar da zaman lafiya a Jihar Filato, sun nemo gawar wani makiyayi mai shekaru 16 da ya ɓace tare da ƙwato shanu sama da 50 da aka sace.

 Daily Trust ta rawaito cewa, sojojin sun gano gawar makiyayin da ya ɓace tare da wasu Fulani makiyaya a ranar Juma’ar nan.

Boko Haram: Zulum ya yi ganawar sirri da Shugabannin sojoji An saki fasto an kuma tsare wanda ya kai kuɗin fansa

Makiyayin Abdullahi Muhammad mai shekara 16 da ya ɓace, kuma an samu rahoton an yi awon gaba da shanu sama da 70 a yankin Ariri, ƙaramar hukumar Bassa, a lokacin da suke kiwo a yankin.

Sai dai a baya, Danjuma Auta, babban sakataren ƙungiyar raya Irigwe (IDA), ya musanta batun satar shanu a yankin, yana mai zargin cewa an kashe mambobinsu da dama a cikin makonni uku da suka gabata, kuma suna fuskantar ƙalubale na hare-hare.

A cewar Ya’u Idris, shugaban Ƙungiyar MACBAN a garin Bassa, wanda ya tabbatar da samun nasarar gano gawar makiyayin da ya ɓace, sojojin OPSH tare da wasu makiyaya ne suka tsinto gawar a wani kabari mara zurfi, tare da wasu makiyaya a gaɓar kogi da ke kusa da babban yankin Ariri.

Ya ce, an fille kan makiyayin, aka datse hannunsa na hagu.

Da yake ƙarin bayani, shugaban ya ce, “Mun tono gawar kuma muka mayar da shi gida don yin sallar jana’iza, an ceto sama da kashi 80% na shanun, muna godiya ga jami’an tsaro musamman jami’an tsaron OPSH bisa ƙoƙarin da suka yi wajen ƙwato gawar da shanu.”

Mai magana da yawun rundunar ‘Operation Safe Haven’ Manjo Samson Zhakom da DSP Alabo Alfred na rundunar ’yan sandan jihar, har yanzu ba su mayar da martani ga saƙon da wakilinmu ya aika masu kan wannan lamari ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Operation Safe Haven da ya ɓace

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina

Ya ƙara da cewa rundunar ta samu nasarar ceto mutane 47 da aka yi garkuwa da su da kuma mutane 39 da aka ceto daga hannun masu safarar mutane, inda aka miƙa su ga iyalansu.

Kayan da aka ƙwato daga hannun waɗanda ake zargi sun haɗa da bindiga AK-47 guda ɗaya, bindiga ta gida guda ɗaya, alburusai 183, motoci uku, babur mai ƙafa uku da keke napep ɗaya, da kuma dabbobi sama da 200 na sata.

Haka kuma, ‘yansanda sun ƙwato tarin miyagun ƙwayoyi irin su Fentalin, Exol, Tramadol, da wiwi, tare da wayar wutar lantarki.

Abubakar ya sake tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da ƙoƙari wajen tabbatar da tsaro, inda ya ce, “Duk da waɗannan nasarori, har yanzu akwai aiki da yawa a gabanmu. Mun ƙuduri aniyar ƙara ƙoƙari.”

Ya gode wa Sufeton ‘Yansanda na Ƙasa, Kayode Egbetokun, da Gwamnatin Jihar Katsina bisa goyon bayansu, tare da kira ga jama’a da su ci gaba da bai wa jami’an tsaro sahihan bayanai da za su taimaka wajen hana aikata laifuka.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa November 12, 2025 Manyan Labarai Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna November 12, 2025 Manyan Labarai Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba November 12, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3 Tare Da Sace Babur A Nasarawa
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina
  • ’Yan bindiga sun kashe mai juna biyu da wasu mutum 4 a Sakkwato
  • An ceto mutane 86 daga hannun ’yan ta’adda a Borno
  • An ceto mutane 86 daga hannun ’yan ta’adda 29 a Borno
  • Matan sojojin da suka mutu na neman agaji
  • An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano
  • Yadda Sojoji Suka Tarwatsa Haramtattun Matatun Mai 14 A Yankin Neja Delta 
  • ’Yan bindiga sun sace mata 5 a Kano