An gano gawar makiyayi da ƙwato shanu a Filato
Published: 11th, April 2025 GMT
Dakarun rundunar ‘Operation Safe Haven’ da ke aikin tabbatar da zaman lafiya a Jihar Filato, sun nemo gawar wani makiyayi mai shekaru 16 da ya ɓace tare da ƙwato shanu sama da 50 da aka sace.
Daily Trust ta rawaito cewa, sojojin sun gano gawar makiyayin da ya ɓace tare da wasu Fulani makiyaya a ranar Juma’ar nan.
Makiyayin Abdullahi Muhammad mai shekara 16 da ya ɓace, kuma an samu rahoton an yi awon gaba da shanu sama da 70 a yankin Ariri, ƙaramar hukumar Bassa, a lokacin da suke kiwo a yankin.
Sai dai a baya, Danjuma Auta, babban sakataren ƙungiyar raya Irigwe (IDA), ya musanta batun satar shanu a yankin, yana mai zargin cewa an kashe mambobinsu da dama a cikin makonni uku da suka gabata, kuma suna fuskantar ƙalubale na hare-hare.
A cewar Ya’u Idris, shugaban Ƙungiyar MACBAN a garin Bassa, wanda ya tabbatar da samun nasarar gano gawar makiyayin da ya ɓace, sojojin OPSH tare da wasu makiyaya ne suka tsinto gawar a wani kabari mara zurfi, tare da wasu makiyaya a gaɓar kogi da ke kusa da babban yankin Ariri.
Ya ce, an fille kan makiyayin, aka datse hannunsa na hagu.
Da yake ƙarin bayani, shugaban ya ce, “Mun tono gawar kuma muka mayar da shi gida don yin sallar jana’iza, an ceto sama da kashi 80% na shanun, muna godiya ga jami’an tsaro musamman jami’an tsaron OPSH bisa ƙoƙarin da suka yi wajen ƙwato gawar da shanu.”
Mai magana da yawun rundunar ‘Operation Safe Haven’ Manjo Samson Zhakom da DSP Alabo Alfred na rundunar ’yan sandan jihar, har yanzu ba su mayar da martani ga saƙon da wakilinmu ya aika masu kan wannan lamari ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Operation Safe Haven da ya ɓace
এছাড়াও পড়ুন:
An gurfanar da wasu kan zargin kashe matafiya bikin aure a Jos
Rundunar ’yan sandan Jihar Filato a ranar Alhamis ta gurfanar da wasu mutane 22 da ake zargi da kashe matafiya bikin aure da a unguwar Mangun da ke Ƙaramar hukumar Mangu ta Jihar Filato.
An kashe mutum 13 daga cikin matafiyan, yayin da wasu da dama suka jikkata sakamakon harin da wasu da ake zargin ’yan daba ne suka kai lokacin da suke kan hanyarsu ta zuwa unguwar Qua da ke ƙaramar hukumar Qua’an Pan ta Jihar Filato.
’Yan sanda sun ƙaddamar da sabon samame, sun kama mutum 98 a Kano Jami’ar Tarayya ta Gashuwa za ta ba matar Tinubu digirin girmamawaAdadin waɗanda aka kashe mutum 32 da suka haɗa da maza da mata da ƙananan yara suna cikin wata mota ƙirar bas mai kujeru 18 daga unguwar Basawa da ke Ƙaramar hukumar Sabon Gari a Jihar Kaduna, domin halartar bikin aure a lokacin da suka haɗu da maharan.
Da yake gurfanar da waɗanda ake zargin a gaban babbar kotun jihar, lauya mai shigar da ƙara, S.I. Ikutanwa, ya nemi izinin kotun domin waɗanda ake zargin su ɗaukaka ƙara kan tuhume-tuhume huɗu da ake yi musu.
Sai dai lauyan da ke kare waɗanda ake zargin Garba Pwol, ya ƙi amincewa da buƙatar ƙarar, inda ya ce biyu daga cikin mutum 22 ƙananan yara ne, wanda hakan ya sa tuhume-tuhumen ba su da tushe.
A cewar lauyan da ke kare waɗanda ake zargin ’yan shekaru 13 ne da kuma 17, kuma doka ba ta yarda a gabatar ƙananan yara a irin wannan shari’ar ba. Lauyan da ke kare waɗanda ake ƙara ya buƙaci kotun da ta ba shi lokaci domin shigar da ƙara.
Da yake mayar da martani ga lauyan waɗanda ake tuhuma, lauyan mai shigar da ƙara ya ce, tun da biyu daga cikin waɗanda ake zargin ’yan ƙasa da shekaru 18 ne a cire sunayensu, sannan a bar sauran mutum 20 da ake tuhuma su amsa tuhumar.
Da yake tsokaci kan sharia’ar ga ɓangarorin biyu da suka gabatar, alƙalin kotun, Mai shari’a Boniface Ngyon, ya ce zai fi kyau kada a shigar da ƙarar nasu ranar Alhamis, maimakon haka za a yi gyara a ranar Juma’a, ban da ƙananan yara.